← Book details Zakaran Da Allah Ya Nufa Da Cara Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 128

Sashe 128

Zakaran Da Allah Ya Nufa Da Cara Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*BAYAN SHEKARA UKU...*

Abubuwa da dama sun faru ciki harda shiryuwar Sageer, Ashe tun watansa uku a gidan yari daddy yasa aka sako shi batare da sanin kowa ba yyi hakan ne domin tausayin Abba, yaso ma ace an kyaleshi saidai kodan ya horu ya Bari yyi wata uku a gidan yari aikuwa yaji jiki sosai, Bayan dauko shi da daddy yyi a sace ya tura shi can F.U.D jihar jigawa ya karasa karatun sa a hausa department, Sageer ya nutsu kwarai Dan harya Rasa bakin godiya da zaiyiwa daddy har kunyar sama yakeji idan ya tuna tafkin da yyi tayi sai yaji ransa na zafi Ashe Shidin ba kowa bane gsky Saratu ba kowa ta cuta ba sama dashi, shiyasa yasha Alwashin Yana komawa kano Saiya ziyarci inda take, hakan ce kuwa ta kasance Bayan ya Gama degree dinsa a fannin hausa ya roki Alfarmar daddy Yanason ganin Saratu, daddy ya bashi goyon baya yasa aka kaishi can inda su Saratu suke, yana tmbyr ta kuwa akace saidai yaje inda take Dan bazaiyiyu tazo musu Nan ba, Sageer yyi mmki kwarai saidai bece komai ba ya amince bisa jagorancin wata ma'aikaciyar, wani daki dake can gefe yyi nisa da dakunan 'yan prison din aka nuna Masa yaje, Sageer ya fara takawa tun daga nesa yakejin wari Kadan2 be kawo komai a ransa ba ya nufi dakin gadan2, Aiko Yana Isa dab da wajen ya toshe hanci da sauri, ja baya yyi Yana sa hankaci a hancinsa can ya hango Saratu na ihun azaba, gwalo Ido yyi cikin karaji yace, "saratuuu??" Juyowa tayi a firgice idonta yyi luhu2 Kamar me cutar Corona a tsorace yace, "kece Kika koma Haka?" Saratu Tace, "kaidin waye?" Ta Fadi hakan tana Sosa cinyar ta dake mata kekayi sosai ga wasu kuraje masu ruwa duk sun yanyame cinyar, ji yyi ance, "muguwa Azzaluma Allah ya Isa haduwata dake" Nas ta furta hakan tana cije lips dinta sbd azabar da hannun ta suke duk sun rube Suma Suna zubar da ruwa Yunkurun tashi Saratu tayi Nan ruwan diwa ya fara gangarowa ta kasanta Ashe tun daga HQ dinta manyan kuraje ne dankare bula2 masu fitar da kazamin ruwa me cike da wari da makaki yake fitowa, shiyasa duk su biyun aka killace su daga nesa sbd warin da suke, hakan kuwa ya jawo kusan kullum sai sunyi fada tamkar karnuka Suna tsinnewa juna, Sageer ne ya tari Numfashin Saratu da taso yin mgn yace, "yaron da kikaso abin duniya ta dalilin sa shine Kika manta? Lalle Kinga rayuwa" Saratu ta kura Masa Ido sosai can tace, "Sageer?" Sageer ya sake manne hancin sa Yana gyada Kai, fashewa tayi da kuka sosai tana fadin, "Dan Allah Sageer ka yafemin ni nasan na cuci rayuwar ka akan wani buri nawa marar tushe da Asali Dan Allah kayi hakuri kaji?" Sageer yace, "idan ma banyi hakuri bama ya zanyi? Kalli a halin da kike fa? Na tabbata hakkin Wanda kikaci ne yake bibiyar ki, kinyi shekaru da dama kina shirya mugunta iri2 a ranki karshe ke burinki be cika ba, sannan kin kare a wahale, kin Kuma sabawa Allah kin tashi a tutar Babu, a gsky kin cuceni yaseen" hawaye take sharewa sosai wasu na zubowa hakan yasa idonta ya cabe da kwantsa Tace, "duk Abinda kace Sageer gskyne nidai kamin Alfarma kwaya daya Tak ko yayane ka rokar min duk Wanda kasan na cuta ya yafe min" Sageer yace, "Wannan Kuma keda su duk Wanda be yafe Miki ba bazan Masa dole ba ni na yafe Miki a Matsayin ki na uwa, domin hausawa sunyi gsky da sukace uwa uwace....Amma fa waccar matar ki sanar Mata bazan yafe Mata ba" ya nuna Nas, Nas ta zaburo tana fadin, "haba yaro yanzu ni meye laifna a ciki? Uwarka ce fa ta sani yin Abinda nayi" dage kafadun sa yyi yace, "I don't care" yana Gama fadin Haka ya juya ya barsu sunata rusa kukan nadama. acan bangaren mom kuwa Saida taga uwar Bari ta nufi garin Huguma can kauyen dake karkashin hukumar takai LGA kano state, anan ubansu Anty shafa yake mlm rabe, a darare kirjinta na bugawa ta isa garin saidai tashin farko data nuna bukatar ta akayi mata wankin babban bargo, lalle taga wulakanci dacin mutunci karara karshe ma cewa yyi yadda ta watsa Masa 'ya'ya haka zata sa kudi ta kawo Masa su ya aurar dasu a kauyen, mom ba yadda ta iya Haka ta fara aikin gyada tana matsar Mai ka'in da na'in harda su casa da Aikatau din wanki, Saida ta Gama figewa ta rame sosai kafin aka samu dakyar da sidin goshi aka samo dubu dari biyu aka Kai can inda aka daure su Anty shafa aka sako su, Suna dawowa kuwa Basu Jima ba mlm rabe ya aurar dasu a wani kauyen dake kasan na Huguma Kuma me Suna langwami duk mazajen tsoffi ne anty shafa cikin mata uku itace ta hudu ga Yara kusan fiye d Ashirin, Haka zalika Anty Jamila itace ta uku a cikin wani katon gida Kuma duk tare sukeyin abinci cikin katuwar tukunya irinta 'yan boarding kowa girkinta yazo ita kadai zatayi abincin ga casa da surfe kafin wani lkci kuwa duk sun saje da mutanen kauyen hakora sunyi Kore Shar da cako2 Kamar dama can anan suke rayuwa, mom ta lallaba ta sake auren mlm rabe itama dai kusan itace ta hudun Nan aka ci gaba da wahala Ana fama da suyar kosai da awara. Acan kano kuwa, Bayan Sageer ya tafi da Alhinin yadda Saratu ta koma daddy ya Mika shi wajen Abba, Abba har yaki sauraron sa daddy yasa baki wajen bashi hakuri ba komai Abba yasa yyi Masa hakan ba saidan ya fahimci ko Sageer din ya shiryu ne, Toh cikin ikon Allah ya shiryun Nan suka hada hannu wajen yin kasuwanci a cikin wambai, ginin Hospital din Dr. Sadeeq an kammala har an fara aiki dashi da taimakon Dr. Omar dayake Aiko musu da duk wani kayan aiki da ake bukata a ciki, a Wannan tsakankanin lkcn ne Dr. Omar ya kara karatu a fannin Likita harya zana professor Haka ma Ameera tayi degree dinta a bangaren microbiology a kalla dai burinta ya cika, Saida akayi dgsk dasa bakin Omar kafin Abba ya sake aure dan ya girgiza da lamarin mata, aikuwa yyi dacen sabuwar matar tasa sumayya me hankali da halin dattako, ko dad din Ameera ma hakane can Adamawa ya samo 'yar bafullata me Suna surayya ya aura, Haka ma Sageer ya auri wata yarinya me Suna ummi yarinyar akwai kamun Kai da kunya yanata murna ya samu kamilar mace saidai tun a Daren farko dayaci Karo da ita ya jita fanko, anan ya Kara Tabbatar wa da kansa lalle ba'a yiwa Allah wayo shi kansa bazai iya tuna Yara nawa ya Bata ba, Haka dai ya hakura be canja mata ba sukaci gaba da Rayuwar su cikin farinciki, Dr. Sadeeq da Safna sun haifi Diya mace me sunan Mummy Aisha, Suna kiranta da Noor. Lekowa Meera tayi daga dakinsu ta hango Dr. Omar bakin ruwa ya Dan kishingida jikin kujerar ruwa yasa hula hade da rufe idonsa, murmushi tayi tana karewa tsuburin da suke rayuwa kwanan Nan, ba ko Ina bane sai Maldives Island, Basu fi 2weeks da zuwansu wajen ba tun Bayan dawowar su daga naija bikin sunan Sadeeq da Safna suka bar Annor wajen Mummy a Wannan zuwan nasu ne ma Sageer ya nemi yafiyar su dakyar d sidin goshi ma suka saurare shi kafin daga baya suka yafe masa, direct suka taho Nan Dan kawai su more Rayuwar su, bra da pant na ruwane a jikinta dogon gashin ta a watse har zuwa kunkumin ta, ta Isa gareshi tana zuwa ta cire hular daya tare fuskar sa hade da sunkuyowa tana manna fuskarta da tasa, Dr. Omar na dariya ya kamota gaba dayanta ta dawo saman faffadan kirjinsa da Babu riga sai wando kawai a jikinsa yace, "sugar babe daga cewa Bari kije ki dawo kin Barni inata jira" dariya itama Meera tayi Tace, "oh swthrt I'm sorry" ta Fadi hakan tana Kai bakinta saman nipple dinsa tadan lasa kadan, hannunsa yasa cikin gashin kanta cikin wani irin yanayi yace, "pls continue inason Haka" murmushi Meera tayi ta Kara Kai harshen ta Kai Nan suka fara romancing junan su kafin nan suka fada cikin ruwan dake gabansu domin zuwa yanzu sun zama kwararrun masu iya iyo a ruwa sbd yawancin inda suka zauna ba'a Rasa swimming pool a wajen, hakan yasa Suna Shiga ciki suka Fara wasa Kamar yadda suka Saba. Bayan sun fito ne suka wuce daki rungume da junan su, Saida suka Gama shirun su Dr. Omar na gyarawa Meera dogon gashinta ya tsaya kawai Yana kallon ta, Meera ta dage Masa gira tana fadin "Yadai?" Dr. Omar yyi murmushi me kayatarwa kafin yace, "babe....!" Ya Fadi hakan Yana Jan sunan, Meera Tace, "yes boboluv" Dr. Omar yace, "I LOVE YOU, I so much love you dear,
Words are not enough to tell u how wonderful U are, I thank GOD for letting me in to your life and you in to me" ya Ida mgnr Yana lumshe Ido hade da Dora hannun ta saitin zuciyar sa, har cikin kokon ransa yakejin Meera a ransa, har kullum kaunarta da sonta karuwa yake a zuciyar sa be taba Jin sonta ya ragu ba Koda na miskali zarratan, Cikin matukar Jin dadin kalaman sa meera Tace,
"You are my best friend, my human diary, and my other half, You mean the world to me and I love you more than more" Nan suka rungume junan su cikin tsananin farinciki Dr. Omar ya dauketa cancak sai Kan gado anan aka Kara baje basirar dunbin kaunar da suke ma juna.

TAMMAT BI HAMDULILLAH.

*Anan nake kawo karshen littafin Nan ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA....( _ko Ana Muzuru Ana Shaho Sai yyi_) Ina rokon Allah S.W.A ya yafe min duk wani kurakuran d nayi a ciki, darasin da yake ciki Kuma Allah ya bamu ikon amfana dashi, sannan Ina fatan duk Wanda na batawa Rai ta dalilin littafin Nan ya yafe min nidai na yafewa kowa Allah ya yafe mana gaba1 Ameeen, taku a Koda yaushe NUCEEYLUV...✍�*
Chapter 128 · 0% Book details