Sashe 95
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wajan azahar su Sultan sukaje 'yalleman. Sun samu tarya sosai dan an sanar da baffa zancen zuwan su, kusan duk uncles din Moon su zo taryan manyan baki. Kofar gidan baffa kam cika yayi da mutanen gari da suka zo kallon sarki, a cewar su. Hakimai uku ne suka tafi tare da galadima, sultan kuma cousins dinsa guda biyu da amir ne suka raka shi. A palon baffa aka sauke su, aka gabatar da sultan, ya gaishe da baffa, baffa yana ta tsokanar sa, daga nan aka sallame su suka tafi gidan nuraddeen suka bar manya zasu yi magana a tsakanin su. A gidan nuradden suka ci abincin da akayi ta kawo musu kamar babu gobe, Sultan ya zauna yayi ta shan fura yana santi wai dama abinda Moon take sha kenan in tazo 'yalleman shine bata taba gayyatar sa ba. Nan da nan suka saba da nuraddeen, yana ta bashi labarin Moon sanda tana yarinya. Suna zaune Moon ta kira shi, nuraddeen ne ya dauka, "ke wato yau kadai din ma ba zaki bar mana shi ba ko? Sai kin dame mu da waya?" Tayi dariya "kai yaya, kira nayi fa in ce ya bani kai mu gaisa" yayi dariya "ni zaki yiwa yawo ko? Har da wani yaya sai kace da yayan kike ce min" suka yi dariya gaba daya sannan ya bawa sultan, tace "so...how are you?" Yayi murmushi yace "ke dai ki fadi gaskiya, kin kira kiji yadda nake ko kuma kin kira kiji me ake ciki?" Tayi dariya tace "yanxu shikenan bani da right din da zan kira ka? I just want to know ya kuka je" yace "lafiya lau muka zo love, and maganr kuma da kike so kiji ni ma ban sani ba, suna can suna maganganun su" tace "ni ba wannan ne yasa na kira ka ba, so nake inji ya akayi aka saka maka hular rawanin nan da wannan gashin na kanka?" yayi shiru bai bata amsa ba, ta fara dariya, tace "don't tell me aski aka yi maka" ya bata rai yace "don't laugh, give it a week, zai dawo ne. Besides, ba du aka aske ba ai" tace "can I see it?" Yace "never, ba zaki taba gani ba har sai ya dawo yadda yake"
A wajen su baffa kuwa sosai suke ta shan hira abinsu, da yake baffa mutun ne mai barkwanci nan da nan bakin suka saki jiki da shi suke ta hira. Sai bayan sunci abinci sunyi sallah sannan galadima ya gabatar da maganar data kawo su, suna nemawa dansu Abbakar Sadiq Abdullahi auren Maimunatu Muhammad Dikko, daga nan ya aika aka shigo da wata jaka cike da kudi, aka ajiyewa uncle Aliyu aka bude, mint ne 'yan 1000, galadima yace "ga kudin aure nan, muna fatan zaku karba" kowa ya saki baki yana kallon kudin, uncle Aliyu ya kallu kudin da yasan zasuyi daga miliyan biyar zuwa sama, ya saka hannu ya dauki rafa guda biyu ya ajiye a gefen sa yace "mun gode sosai amma wannan ya isa, albarkar auren muke nema, wannan ma mun dauka ne saboda al'ada ne" Tafida ya matso zai yi magana, baffa yace "abinda zamu iya karba kenan. Tun sanda labarin yaron yazo mana na tura Aliyu yaje har Abujan yayi mana bincike akan yaron, kuma yace min ya gamsu da abinda ya samu, dan haka tunda shine waliyinta na yarda da maganarsa. Na bawa Abbakar Sadiq auren Maimunatu, Allah yayi musu albarka baki daya Allah kuma ya sanya alkhairi" gaba daya aka ce "Ameen" uncle Rufa'i yace "to sai maganar sa rana kuma, yaushe kuke ganin za'ayi?" Tafida yace "ni ina ganin kar aja kwanaki da yawa, matsalar dai kawai yaron bai kammala ginin sa ba, dan haka ina ganin a bashi wata biyu, insha Allah kafin nan ya kammala, ita ma amaryar kafin nan ta shirye2n hidimarsu ta al'ada" kowa yace "wannan yayi, Allah ya kaimu" daga nan nan akayi addu'ar neman alkhairi aka tashi. Sultan kam da aka gaya masa me aka yanke ji yayi kamar ya dora hannu aka yayi kuka. Tun a hanya yake mita "wai wata biyu, ko garin abuja zan gine gaba daya ai iyakacin kwanakin da za'a bani kenan, aikin ginin nawa da a cikin sati daya zan gama shi, aikina ne fa" Ahmad, cousin dinsa yace "why are you whining ne Sultan? Tunda ance an baka ba shikenan ba? Me kake yiwa sauri ne wai" Sultan kawai tsaki yayi yace a ransa 'ba zaku gane ba'
A abuja kuwa kiran gaggawa Daddy ya samu daga fada, nan da nan ya tafi, yana zuwa mai martaba sarki ya nemi a basu guri zasu gana, yace "Muhammad dama abinda kake shiryawa kenan? Dama dalilin da yasa ka dauki yaron nan kenan" Daddy yace "Allah ya taimakeka sam ba haka bane, mayar da Sultan gida na daban da alakarsa da yarinyar wajena" Takawa yace "bakasan halin yaron nan ba labarinsa kakeji, duk inda tunanin ka ya kai to ya wuce gurin. Ina tausayawa yarinyar nan, she have no idea what she is in for. Ka taimaka mata ka janye maganar auren nan. Bana son abinda zai bata zumuncin da yake tsakanin mu. Nasamu labarin itin tarbiyyar da ka bawa 'ya'yanka, sam yarinyarka bata dace da yaron nan ba. He don't deserves her" Daddy yayi shiru yana tunanin amsar da zai bayar, sai yace "Allah ya taimake ka ni bani na hada yaran nan ba, hadin Allah ne, kuma magana ba'a hannu na take ba tunda tun dazu suka ce min har sun isa 'yalleman gurin baffa na, yanzu maganar tana hannun sa. Ni ina ganin mu zuba ido kuma muyi addu'ah mu ga zabin da Allah zai yi mana" Takawa yayi shiru kamar ba zai sake magana ba, sannan yace "mu dai mun gayama gaskiya, wanda bai ji bari ba kam tabbas zaiji hoho. Fatan mu shine duk abinda ya faru kar kazo gurin mu. Zaka iya tafiya" Daddy jiki duk ba kwari ya mike ya fito, har yaje gida yana lissafin lallai da akwai wani abu a tsakanin Sultan da babansa wanda duk bincikensa bai sani ba, koma dai menene, it is something big.
Moon
A dakin Hafsat muka zauna, hira kawai muke yi muna dariya abin mu, muna ta labarin Haihuwar Hafsat da irin shagalin da zamu yi ranar suna. Edd dinta ya riga yayi kawai haihuwa ake jira. Hira nake ina dariya amma can kasan raina ina tunanin abinda yake faruwa a 'yallemam. Muna cikin haka naji shigowar kiran Sultan, na daga ina kallon sunan jikin screen din 'my Sultan' na tuna ranar da yayi saving sunan da kansa a waya ta, ranar dinner din Hafsat, a lokacin ban taba tsammanin zan dauki kiran saba ko da ya kirani sai gashi yanzu ya zama tamkar wani sashe na jikina wanda ba zan iya rabuwa da shi ba. Yanzu gashi wai yana kirana ne ya gayamin an bashi aure na ko ba'a bashi ba, sai naji na kasa daukan wayar har ta katse, ya sake kira shima naki dauka. Amira tace "in ba zaki dauka ba bani shi nan, har wani Sultan akewa kunya? Baki san ance kunyar mara kunya asara bace" na mika mata wayar, tana karba aka sake kira, gani nayi ta taba rai ta dawo min da waya ta, na duba screen naga 'Amir" dariya nayi dan nasan drama dinsu da Amir na dauka, yace "wai kunyar amarcin ce za'a fara yi mana tun yanzu?" Nayi murmushi kawai bance komai ba, yace "gamu nan mun taho, amma na san sai dare zamu karaso Abuja, tell that your ugly friend ta shirya mana abinci dan anan zamu fara sauka" nayi kamar banji ba, na saka shi a hands free nace "me kace?" Yace "wannan kawar taki mummuna, bakar nan masifaffiya, kice mata ta dafa mana abinci kafin muzo" ai kuwa Amira ta warce wayar daga hannuna ta kama yi masa masifa "yanzu har kai zaka kalli wani ka kira shi da ugly? Anya kuwa kana kallon fuskar ka a mudubi kuwa? Duk baki na wallahi ni balarabiya ce akan ka" ni dai dariya nake yi Hafsat tana taya ni. Sai bayan isha suka zo, iyakacin samarin ne suka zo nan manya kowa ya kama gabansa, uncle Aliyu ma yazo ya taho da Amina wacce daga jin zancen biki ta rude ta hado kayan ta. A palon su Sultan suka sauka nan aka shiga hidimar kai musu abinci, sai da suka gama sukayi sallolinsu sannan muka je, ni da Amira da Amina. Muna shiga aka fara drama da Sultan dan fir yace babu wanda zai ga fuskata, ai an bashi ni yanzu dan haka i am no longer in tha market. Su Ahmad suka yi ta naci su kuma lallai sai sun ga fuskata tunda takabas dan su ganni suka zo, da kyar dai Sultan ya yadda na bude fuska ta, shima kuma ya kasa ya tsare yace babu dogon kallo, ni dai dariya kawai nake yi musu. Nan fa Amira da Amir suka dora daga inda suka tsaya, Amina ma da yake mai surutu ce sai ta shige cikin su suke tayi. A hankali sultan ya mike ya je bakin kofa sannan yayi min alama da in zo, tsam na zame na bishi ba tare da duk sun lura mun fita ba. Ina fita sai naga ya kama hanyar garden na bishi a baya.
A wajen su baffa kuwa sosai suke ta shan hira abinsu, da yake baffa mutun ne mai barkwanci nan da nan bakin suka saki jiki da shi suke ta hira. Sai bayan sunci abinci sunyi sallah sannan galadima ya gabatar da maganar data kawo su, suna nemawa dansu Abbakar Sadiq Abdullahi auren Maimunatu Muhammad Dikko, daga nan ya aika aka shigo da wata jaka cike da kudi, aka ajiyewa uncle Aliyu aka bude, mint ne 'yan 1000, galadima yace "ga kudin aure nan, muna fatan zaku karba" kowa ya saki baki yana kallon kudin, uncle Aliyu ya kallu kudin da yasan zasuyi daga miliyan biyar zuwa sama, ya saka hannu ya dauki rafa guda biyu ya ajiye a gefen sa yace "mun gode sosai amma wannan ya isa, albarkar auren muke nema, wannan ma mun dauka ne saboda al'ada ne" Tafida ya matso zai yi magana, baffa yace "abinda zamu iya karba kenan. Tun sanda labarin yaron yazo mana na tura Aliyu yaje har Abujan yayi mana bincike akan yaron, kuma yace min ya gamsu da abinda ya samu, dan haka tunda shine waliyinta na yarda da maganarsa. Na bawa Abbakar Sadiq auren Maimunatu, Allah yayi musu albarka baki daya Allah kuma ya sanya alkhairi" gaba daya aka ce "Ameen" uncle Rufa'i yace "to sai maganar sa rana kuma, yaushe kuke ganin za'ayi?" Tafida yace "ni ina ganin kar aja kwanaki da yawa, matsalar dai kawai yaron bai kammala ginin sa ba, dan haka ina ganin a bashi wata biyu, insha Allah kafin nan ya kammala, ita ma amaryar kafin nan ta shirye2n hidimarsu ta al'ada" kowa yace "wannan yayi, Allah ya kaimu" daga nan nan akayi addu'ar neman alkhairi aka tashi. Sultan kam da aka gaya masa me aka yanke ji yayi kamar ya dora hannu aka yayi kuka. Tun a hanya yake mita "wai wata biyu, ko garin abuja zan gine gaba daya ai iyakacin kwanakin da za'a bani kenan, aikin ginin nawa da a cikin sati daya zan gama shi, aikina ne fa" Ahmad, cousin dinsa yace "why are you whining ne Sultan? Tunda ance an baka ba shikenan ba? Me kake yiwa sauri ne wai" Sultan kawai tsaki yayi yace a ransa 'ba zaku gane ba'
A abuja kuwa kiran gaggawa Daddy ya samu daga fada, nan da nan ya tafi, yana zuwa mai martaba sarki ya nemi a basu guri zasu gana, yace "Muhammad dama abinda kake shiryawa kenan? Dama dalilin da yasa ka dauki yaron nan kenan" Daddy yace "Allah ya taimakeka sam ba haka bane, mayar da Sultan gida na daban da alakarsa da yarinyar wajena" Takawa yace "bakasan halin yaron nan ba labarinsa kakeji, duk inda tunanin ka ya kai to ya wuce gurin. Ina tausayawa yarinyar nan, she have no idea what she is in for. Ka taimaka mata ka janye maganar auren nan. Bana son abinda zai bata zumuncin da yake tsakanin mu. Nasamu labarin itin tarbiyyar da ka bawa 'ya'yanka, sam yarinyarka bata dace da yaron nan ba. He don't deserves her" Daddy yayi shiru yana tunanin amsar da zai bayar, sai yace "Allah ya taimake ka ni bani na hada yaran nan ba, hadin Allah ne, kuma magana ba'a hannu na take ba tunda tun dazu suka ce min har sun isa 'yalleman gurin baffa na, yanzu maganar tana hannun sa. Ni ina ganin mu zuba ido kuma muyi addu'ah mu ga zabin da Allah zai yi mana" Takawa yayi shiru kamar ba zai sake magana ba, sannan yace "mu dai mun gayama gaskiya, wanda bai ji bari ba kam tabbas zaiji hoho. Fatan mu shine duk abinda ya faru kar kazo gurin mu. Zaka iya tafiya" Daddy jiki duk ba kwari ya mike ya fito, har yaje gida yana lissafin lallai da akwai wani abu a tsakanin Sultan da babansa wanda duk bincikensa bai sani ba, koma dai menene, it is something big.
Moon
A dakin Hafsat muka zauna, hira kawai muke yi muna dariya abin mu, muna ta labarin Haihuwar Hafsat da irin shagalin da zamu yi ranar suna. Edd dinta ya riga yayi kawai haihuwa ake jira. Hira nake ina dariya amma can kasan raina ina tunanin abinda yake faruwa a 'yallemam. Muna cikin haka naji shigowar kiran Sultan, na daga ina kallon sunan jikin screen din 'my Sultan' na tuna ranar da yayi saving sunan da kansa a waya ta, ranar dinner din Hafsat, a lokacin ban taba tsammanin zan dauki kiran saba ko da ya kirani sai gashi yanzu ya zama tamkar wani sashe na jikina wanda ba zan iya rabuwa da shi ba. Yanzu gashi wai yana kirana ne ya gayamin an bashi aure na ko ba'a bashi ba, sai naji na kasa daukan wayar har ta katse, ya sake kira shima naki dauka. Amira tace "in ba zaki dauka ba bani shi nan, har wani Sultan akewa kunya? Baki san ance kunyar mara kunya asara bace" na mika mata wayar, tana karba aka sake kira, gani nayi ta taba rai ta dawo min da waya ta, na duba screen naga 'Amir" dariya nayi dan nasan drama dinsu da Amir na dauka, yace "wai kunyar amarcin ce za'a fara yi mana tun yanzu?" Nayi murmushi kawai bance komai ba, yace "gamu nan mun taho, amma na san sai dare zamu karaso Abuja, tell that your ugly friend ta shirya mana abinci dan anan zamu fara sauka" nayi kamar banji ba, na saka shi a hands free nace "me kace?" Yace "wannan kawar taki mummuna, bakar nan masifaffiya, kice mata ta dafa mana abinci kafin muzo" ai kuwa Amira ta warce wayar daga hannuna ta kama yi masa masifa "yanzu har kai zaka kalli wani ka kira shi da ugly? Anya kuwa kana kallon fuskar ka a mudubi kuwa? Duk baki na wallahi ni balarabiya ce akan ka" ni dai dariya nake yi Hafsat tana taya ni. Sai bayan isha suka zo, iyakacin samarin ne suka zo nan manya kowa ya kama gabansa, uncle Aliyu ma yazo ya taho da Amina wacce daga jin zancen biki ta rude ta hado kayan ta. A palon su Sultan suka sauka nan aka shiga hidimar kai musu abinci, sai da suka gama sukayi sallolinsu sannan muka je, ni da Amira da Amina. Muna shiga aka fara drama da Sultan dan fir yace babu wanda zai ga fuskata, ai an bashi ni yanzu dan haka i am no longer in tha market. Su Ahmad suka yi ta naci su kuma lallai sai sun ga fuskata tunda takabas dan su ganni suka zo, da kyar dai Sultan ya yadda na bude fuska ta, shima kuma ya kasa ya tsare yace babu dogon kallo, ni dai dariya kawai nake yi musu. Nan fa Amira da Amir suka dora daga inda suka tsaya, Amina ma da yake mai surutu ce sai ta shige cikin su suke tayi. A hankali sultan ya mike ya je bakin kofa sannan yayi min alama da in zo, tsam na zame na bishi ba tare da duk sun lura mun fita ba. Ina fita sai naga ya kama hanyar garden na bishi a baya.