Sashe 173
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
gagara saboda jikina gaba daya ya zama numb, ganin na kasa ya saka ya dakatar da yawon da yake yi da hannunsa a jikina ya kama wuyan rigar tasa ya ja da karfi, a take duk bottoms din suka tarwatse akan gadon, ya zare rigar a jefar da ita. A tare muka yi team work muka balle belt dinsa, daga dogon wandon har gajeran a tare suka fita suma aka jefar dasu, duk abinda muke yi bakunan mu suna hade da juna, gani muke da mun rabu daya zai iya disappearing ya bar daya. Ya koma ya kwanta akan bayansa, ya jawo ni na dawo samansa. Muka cigaba daga inda muka tsaya. Ana gama round one, Sultan ya fara shirye shiryen komawa filin daga na rike fuskarsa da hannayena duk biyun ina kallon idonsa nace "sultan sallah fa" yayi ajjiyar zuciya ya dora kansa akan kirjina yana sauke numfashi, sai kuma ya dago kai da sauri yana kallon agogo, nima na bishi muka kalla tare 8:30pm, muka kalli juna, sultan yace "akwai shaidan a gurin nan" da sauri ya mike ya tafi ya hada mana ruwan wanka, cewa nayi ya fara yi, dan wankan tare ma wani abin zai kuma jawowa. Dole muka hada magrib da isha mukayi a tare. Na dauko waya ta na saita alarm for all the five daily prayers, dan in kana gurin nan ba sani zakayi ba. Ranar sultan cewa yayi a waje zamu kwana, ya shimfida mana blanket mai laushi a kan floor din waje, ya saka mana pillow duga daya sannan ya sake daukar mana bargon lulluba. A gurin akayi serving din mu dinner, muna gamawa suka zo suka kwashe kayan. Dadin iskar gurin kadai ya isa ya saka mutum bacci ballantana ga gajiyar da muka kwaso, da assuba sanyi ne ya tashe mu duk kuwa da makalkale juna da mukayi muka kudunduna, dole muka koma daki mukayi sallah sannan muka koma bacci, duk da dai ba baccin muka koma ba dan sultan cewa yayi shi a dictionary dinsa babu baccin safe. Da safe na kira Mommy na gaya mata inda muke nace amma kar ta gayawa kowa, she was concerned, tace "to ke yanzu ga yanayin da kike ciki kuma in wani abin ta faru fa? Ba gwara ke ya kawo ki gida ba shi ya zauna?" A raina nace 'Mommy kenan, me raba mu ni da sultan ai sai dai mutuwa kuma, mutuwar ma in san samu ne ta dauke mu tare' na kwantar mata hankali da nuna mata cewa ai suna da asibiti ne kyau anan din, sannan zanke zuwa lokaci zuwa lokaci ana duba lafiya ta data babyn, kuma nasan me nakeyi dan haka da naji wani chanjin da ban yarda dashi ba zan tafi asibiti. Muna gama waya da Mommy na kira Ummee itama, tana jin muryata ta sauke ajjiyar zuciya, "maimumatu I have been waiting, jiya banyi bacci ba, jow are you" na tabbatar mata cewa lafiya lau muke daga ni har sultan, kuma zamu ke kiranta akai akai muna gaisheta. Na bata sultan suka dan gaisa kadan sannan ya kashe. Rayuwa mai dadi muke shimfidawa a Maldives, kullum zamu dauki hayar speedboat mu fita yawo, island by island, duk inda mukaje zamu dauki pictures da camera din da sultan ya sayo mana, in kuwa muka dawo cabin din mu to abu daya ne zamuyi tayi, sallah ce kawai da cin abinci suke raba mu da junanmu, har mamakin mu nake yi, sam bama gajiya da junan mu, yanzu za'ayi yanxu kuma za'aji kamar anyi sati ba'ayi ba. Cikina kam tunda na shiga third trimester sai kara uban girma yake yi da nauyi. Sam girman sa amma baya hanani sakewa da sultan, shima kuma hakan banga yana wani takura masa ba, da kamar game muka maida abin, in mun gwada wani abin yaki yi sai mu koma wani, it makes it more fun. Sultan seems a bit gentler dai yanzu, amma dai he is usually rough. Bani da wani complication, dan duk wata doka da ka'ida ina bi, exercise kam wannan inda ace yana yawa da har yawa zai yi min. Muna yawan yawa gida, and things seems to be happening a Nigeria, abu na farko anyi bikin munir, suddenly abin ya faru, yaje 'yalleman da daddare ya fita aikin nasa, ya samu 'yar mutane a loko yana mammatsewa sai baban ta ya gansu, a take kuwa yaje ya gayawa baffa wanda ya kira uncle Rufa'i yace a daura musu aure, ga kewaye nan a gidan ta tare anan, sannan shima munir din ya baro Lagos tunda dama ba wata uwar yake yi acan ba sai kashe kudin mahaifinsa, ya dawo nan 'yalleman a nema masa ko teaching ne ya fara yi. Haka kuwa akayi, aka daura wa munir aure aka tattaro shi aka dawo dashi 'yalleman aka nemar masa aikin koyarwa. Ana bani labarin ina dariya, ita kanta Aminar da take bani labarin dariya take yi, tace "yanzu in kika ganshi sai kinji tausayinsa, baffa ya saka shi a gaba, dama baffa ga tsufa da rikici, kuma gashi dama babu kowa a gabansa, dan haka tare suke komai da munir. Abu na biyu da ya faru shine neman auren Amina da akaje yi 'yalleman, farko uncle Rufa'i yaki yarda, amma da yaga Daddy ne akan maganar sai yayi shiru, ansha dai rigima da Baffa dan cewa yayi shi bazai bawa bayarabe jikarsa ba, Daddy ne da uncle Ali suka dage, suka saka baffa a gaba da nasihohi ta lallami suna nuna masa irin tarbiyyar yaron, bashi da wani nakasu da addini zai ce kar a bashi aure, kuma suka nuna masa irin wannan intertribal marriages din shine zai kawo solution a rigin gimun kabilanci. Yanzu dai baffa ya yarda, an saka bikin Amina nan da wata biyu. Na lissafa naga kusan lokacin EDD na kenan. Sai shugabannin gwauraye na Abuja, yaya walid da yaya Habeeb, Daddy yace duk ya gaji da ganinsu suna zamar masa a gida, yace kowa a cikinsu ya fito da matar aure a hada dana Amina. Yaya Habeeb kam kamar danshi, dan sabofa yawan 'yammatansa sai da yayi ta ruwan ido kafin ya fitar da guda daya, wata Fadila 'yar Bauchi. A inda aka samu matsala shine gurin yaya walid, shi ko hanyar zuwa zance bai sani ba, ga 'yammatan kuma binsa suke yi kamar zasu kwanta masa, ga kuma kyan ga kudin, dan nesa ba kusa ba yaya Walid yafi yaya Habeeb kyau da iya daukar wanka, sai dai babu budurwa, da Daddy ya gaji da magana da kansa yayi wa Hajja waya yace ta samowa Walid mata a cikin 'yan'uwa, ai kuwa kamar an bawa kura ajjiyar nama, Hajja taji dadi sosai tana ganin Daddy ya huce mata haushin mu ni da Hafsat, kuma sai ta bawa kowa mamaki itama, mamar data zaba masa itace Zainab, 'yar autar uncle Ali. Yarinya ce karama dan wannan shekarar ta gama sec sch. Kyakykyawar bafulatana sosai ga hankali da tarbiyya irin ta uncle Aliyu, babu wasa. Uncle Aliyu bai ce komai ba sai ya tattara ta ya kaiwa hajja ita yace ita zata yi mata shirin auren, anan gurinta za'azo a dauke ta. Yaya walid kam farko cewa yayi bai yarda ba, wai shi tayi masa kankanta, sai da Daddy ya nuna masa bacin ransa sosai sannan ya hakura. Ni kam ina wata duniyar amma babu wanda ya kaini murna, dan dama can ina son yarinyar nan saboda nutsuwarta, sai dai ba tausaya mata an hada ta da shugaban bachelors na Abuja. Sultan kuwa da yaji labarin cewa yayi dai dai kenan, gwara da aka bashi karamar, dan yadda yake da shiru shirun nan in aka samo mai budadden ido aka bashi rakumi da akala zata mayar dashi. Jin labarin su Amina yasa na kira kawata Amira dan inji ya take ciki ita kuma, ta dauka da murnarta tace "maman baby shiru kin buya, wayarki ma bata shiga" nace "wallahi kuwa Amira, abubuwan ne sai a hankali" tace "dama nayi ta nemanki ne in gaya miki nagode da shawarar da kika bani, Ibrahim ya yafe min kuma sosai naji dadin yafiyarsa" nace "to me kike ciki yanzu?" Tace "ina kano yanzu. Bayan mun rabu da Ibrahim kawai sai naga cewa na bata wa mama rai itama da yawa, ta sha wahala sosai a kaina, dan haka na yanke shawarar zan huce mata haushin abinda nayi mata ta hanyar bar mata zabin mijin da zan aura, taji dadi kuma sosai, shine ta dauko ni muka dawo kano ta kawo ni gurin kanin baba, yanzu har ta saka gidan mu na abuja ma a kasuwa zata sayar ta sayi wani anan kano tayi zamanta, tace itama in ta samu miji aure zatayi" Nace "to zancen naki auren fa?" Tayi dariya tace "kinsan yadda tsarin yake ai, idan mace taki fitar da miji tayi aure sai a nemo dan uwanta shima wanda yaki aure sai a hada su. Yanzu dai wani cousin dina ne shima wai yaki yin aure, yana kasar waje karatu, shi akae cewa za'a hada mu, amma sai yazo munga juna tukunna" nayi mata fatan alkhairi muka yi sallama. Mommy tayi min waya tace "to bikin ma ba zaki zo ba sai surukan naki sun shirya?" Nace "ai bikin da saura Mommy, it won't take that long". Na kira Ummee ina son inyi tsegumi inji ya suke ciki, har muka gama hirar mu bata cemin komai ba, sai zancen kayan babies din da take yin order take min, har zamuyi sallama nace " Ummee is there any chance na zamu dawo gida nan kusa?" Ta yi shiru sannan tace "wato ku kuna son kuji status din mu amma mu ba zaku gaya mana naku ba ko? Tunda ba zaku gaya mana a ina kuke ba shikenan kowa ya rike labarinsa" but from her voice naji kamar things are going the right way. A bangaren sultan kuwa tunda muka zo Maldives ya kira Amir wanda shima duk shirye shiryen bikinsa sun sako shi a gaba, ga babban abokin ya gudu ya barshi, yace yake turo masa aiki yana yi daga nan, dama kuma aiyukan sun taro sosai, dan haka ya turo wa sultan da yawa. Haka sultan yake zama in his spare times yayi