← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 190

Sashe 26

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Anan zan dakata inja hankalin samari da 'yan mata a harkar neman aure, in kaga budurwa kana sonta itama tana sonka, in dai har kana da halin yin aure, ma'ana kana da aiki ko sana'a wadda kasan zai iya rike ku to kar kace sai kayi kudi zakayi aure, hakan bashi da ma'ana. Maybe baka da rabon yin kudin. Maybe arzikin ka is linked with her. Fadin ubangiji ne cewa kowacce rai da arzikinta take zuwa duniya, idan baka da arziki sai kaga a sanadiyyar auren da kayi, ko haihuwar da matarka tayi Allah ya baku arziki. Kuma abinda mutanen mu har yanzu bamu gane ba shine, idan kayi aure baka da arziki, kukazo kukayi arzikin tare da matarka to kun fi mutunta juna, ku sha wahala tare kuji dadi tare. Indai har yrinya tace tana sonka, indai har soyayyar Allah da annabi take maka to bata damu da kudinka ko rashin kudinka ba. Wannan wait for me shiriritar bata da ma'ana, kana can kana neman kudin wani zaizo wanda ya fika komai kuma she may fall in love with him, kaga kayi losing kenan, biyu babu.

Next thing da nake so inyi magana akansa, duk da dai sai a next chapter za'a fi fahimtata sosai shine akan judging mutun ba tare da kasan sa ba. Never judge a book by its cover. Yawancin mutane suna da kirki, no matter the tribe, you just need to know them. Masu kudi da masu sarauta, in kaga wulakanci a tare dasu mostly daga gurin na kasansu ne ba daga su bane. You just need to take a deep breath and talk to them...

Next thing shine secrets in a relationship. In kuna so relationship din ku ya dore, never ever keep a secret from each other, never lie to each other.

Ga 'yammata da samarin da suke tsoron relationship dinsu ba zai dore ba saboda banbancin yare, ko social status, do u try to make it work ko kuma a boye kuke yi? Just take a deep breath ku tunkari iyayenku da maganar, it may turn out easier than you imagine. Ita zuciya an halicceta da son wanda yake kyautata mata, ko wanne kabila ne shi, indai har zai juri kyautatawa iyayenki, yana nuna musu best behavior dinsa, ke kuma kullum kina nuna musu how much you love him, insha Allahu zaku ga chanji a gurinsu. But most importantly pray.

Episode Twenty Four: The Heartbreak 💔

Ibrahim has broke many hearts yesterday, especially Moon's.

Na cigaba da kallonsa har ya bace min da gani. Feshin ruwan saman da akeyi yana dukan fuskata amma sam ban damu dashi ba. Zuciya ta tana kuna amma hawaye yaki zuwa ido na balle inji dadi. Motsin mutun naji a baya na, nasan ko wace dan haka ban juya ba. Sai da ta lulluba min towel sannan nasan duk jiki na ya jike da ruwa. A hankali ta jani muka shiga daki ta rufe kofar balcony din. Na zauna a kan stool ina goge ruwan jikina ita kuma ta zauna a gefen gado tana kallona. Tace "what happened Moon?" Na dago kaina na kalleta da busassun idanu na nace "He is gone" "gone?" "Yes, He was mistreated by our security, He saw Daddy and....... Ya walid yazo ya gaya masa cewa daddy ne ya samo masa aiki, he then lost it" Hafsat ta saki hannuna ta rufe bakinta da hannayenta. "Oh my God, me yace kuma" nan na bata labarin duk abinda ya gudana tsakanin mu. Tayi shiru na wani lokaci sannan tace "Moon am so sorry, I really am, amma dama nasan alakar ki dashi ba mai dorewa bace. You are too different from each other. Banbancin da yake tsakanin ku kamar banbancin da yake tsakanin maiduguri ne da lagos, ba zasu taba haduwa ba" na kalleta da murmushin takaici a fuskata nace "you are wrong my dear sister, we are more alike than we are different. Na farko duk kanin mu mutane ne, sannan kuma Africans, must importantly kuma Muslims. As muslims kuma munsan we are all equal a gurin Allah, babu wanda yafi wani sai wanda yafi tsoron Allah. Banbancin da kuke gani a tsakanin mu banbancin kabila ne. Ni a ganina kabilar mutum ba komai bace illar yarensa da al'adunsa. Yanzu misali ke wacce yare ce?" Ta kalleni da mamaki tace "fulani mana" nace "eh, babanki fulani ne amma mamanki buzuwa ce, meaning you are not full blood fulani. Yare yana nufin language, yanzu misali ni, ina jin fulatanci, buzanci, turanci, larabci da hausa. To wanne yare ce ni kenan? Yanzu fulani nawa kika sani wadanda suke full blood fulani amma basu iya fulatancin ba? Wani ko zo bai sani da fulatanci ba amma yana ikirarin shi bafulatani ne. It doesn't make sense to me. In nayi maganar al'ada kuma is much worse than yare, dukkan kabilun Nigeria mun aje al'adun mu a gefe mun dauko na wadansu daban munayi. Then how are we different from each other? Yanzu ke da kika ce ke bafulatana ce duk cikin suturar ki babu ta fulani, babu abinda kika sani na daga al'adar fulani, we are even lucky mun iya yaren ma. This all doesn't make sense to me. Yanzu na tabbata idan aka kawo miki wani bafulatanin wanda bai iya fulatanci ba, aka kawo miki igbo ko yaroba wanda ya iya turanci sai ki fi communicating da igbon ko yaroban akan fulanin" duk maganar da nake Hafsat tayi shiru tana kallona da alamar tana fahimta ta. Can ta nisa tace "Ok, yanzu what will you do?" Na kalleta for some seconds nace "That, my dear sister is what I don't know"

Sati guda kenan chif da zuwan Ibrahim amma har yanzu ban ji sassauci a zafin da zuciya ta keyi min ba, kuma har yanzu ban yanke shawarar menene abinyi next ba. Ina kwance main palo akan kujera, Hafsat tana zaune a gaba na, mommy tana can gefe tana operating system din ta. Waya ta nayi dialing na saka a kunne na "the number you are trying to call is currently switched off, please try again later, thank you" naji wadannan kalmomin ya kai sau dari a cikin satin nan, amma na kasa hakura in daina trying. Na ajiye yawar na lumshe ido na. Muryar Ya Habeeb naji ya shigo da sallama, ya gaida mommy ya zauna kujerar kusa dani. Na dan kalle shi, yayi min murmushi, ban mayar masa ba, na sake mayar da idona na rufe. Wajan five minutes muna zaune a haka babu wanda yayi magana. Can Ya Habeeb yayi tsaki yace "wai menene yake faruwa a gidan nan ne? Duk komai ya zama so dull kwana biyun nan, ni na gaji gaskiya" mommy tayi ajiyar zuciya tace "I don't know Habibi, ni kaina abin ya ishe ni wallahi, dazu nake cewa ko da yamma fita zamuyi ne mu dan zaga gari? Duk gidan babu dadi" Hafsat tace "au wai ku baku san me yake faruwa ba?" Ya Habeeb yace "menene yake faruwa" tace "we are having a lunar eclipse" mommy tace "what? Me kike nufi?" Hafsat tace "our Moob is no longer bright" duk suka juyo suka kalleni. Ya Habeeb yace "tabbas, duk ta zama wata iri kwana biyun nan" mommy tace "ko abincin kirki bata ci fa, kullum na tambayeta ko bata da lafiya sai tace min ita lafiyar ta kalau" duk ina jin abinda suke cewa amma na kasa tanka musu.

Daddy ne ya shigo ya Walid yana binsa a baya. Muka tashi gaba daya muka gaishe shi. Ya amsa mana da fara'arsa kamar yadda ya saba. Ya zauna sannan yace "dama ina son ganin ku gaba dayan ku, to tunda gaku kun hadu shikenan sai muyi maganar" mommy ta rufe system dinta ta dawo kusa da daddy ta zauna, mu kuma duk muka sauka kasa muka zauna a gabansu.
Chapter 26 · 0% Book details