← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 190

Sashe 75

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A hankali nace "aunty Zaliha?" Tace "eh nice dai, in kin manta ni ma ki tuna ni, kinsan cewa ni ba Fatima bace bana daukan nonsense. Kin bata wayonki wallahi Moon. Kin bani mamaki. Ni ba dan fatima bace ta gaya min ba zan iya rantsewa karya ake miki. Amma babu komai, zaki dawo hankalin ki ne. Ni na bawa Fatiman shawarar ta kawo ki nan gurina har sai komai ya daidaita tukun" kowa yayi shiru ni kam bakin ciki ne ya kamani jin itace ta bada shawarar rabani da Sultan da babana da 'yan'uwana, sai kuma ta cigaba "yarinya kamarki, me kika rasa ke kuwa a rayuwa, mai kika gani a gurin wannan kangararren yaron da bamu tabbatar ma da asalinsa ba? Kina da asalin ki, ilimi, tarbiyya, ga kyau, na tabbatar samari suna nan suna layi wadanda ko yau akace su fito zasu fito din, amma shine kika gwammace ki zibar mana da mutunci a gurin jama'a" fada take tayi da duk karfinta, ni kuma na sunkuyar da kaina kasa amma ta inda fadan nata yake shiga ta nan yake fita. Daada itama ta dauka suka yi tayi. Sai da sukayi mai isarsu sannan sukayi shiru. Wani daga cikin samarin ne ya zubo min abinci ya miko min, na karba tare da yi masa godiya. Aunty Zaliha tayi sauri tace "a'a, no friendliness of any kind. Duk wanda a cikin ku ya sake ya bata wayarsa ko da wasa ne sai na saba masa wallahi. I am dead serious. There is a very bad person a Nigeria da yake son bata rayuwarta, an kawo ta nan ne saboda a raba su. Duk wanda ya taimaka mata to ya sani cutar ta yayi. Did I make myself clear?" Duk suka amsa da yes. Sakani tayi a gaba sai da na chinye abincin da aka zubo min sannan na sha magani na tace inje in kwanta. Gaba daya jikina ciwo yake yi, ina zuwa nayi sallar isha nayi shirin bacci na kwanta. Bacci me nauyi ne ya daukeni, amma daga baya sai mafarkan suka fara dawowa, na farka na kuma kasa komawa. Daada tana gefena tana ta baccin ta, na tashi na shiga toilet nayo alwala nazo na saka goduwar riga ta na dauko al'qurani na na fara karan tawa, ina yi ina zubar da kwalla. Allah ka fini sanin halin da nake ciki, Allah ka fini sanin waye Sultan. Allah ka huci ran mommy da daddy. Allah ka bani dauriya da juriyar daukan duk wani abinda ka kaddara zai sane ni. Allah ka bawa Sultan hakuri na duk abinda ka kaddara masa. Allah ka zaba mana mafi alkhairi a rayuwar mu baki daya.

Kwana daya ya wuce, na biyu ma haka, sati daya ya wuce na biyu ya biyo bayansa, wata daya yazo, haka wata biyu sannan wata na uku yazo shima. Ko bakin gate ban taba zuwa ba ballantana in fita waje. Daga daki sai palo. Kullum da alqurani na a hannuna dan yanzu shine babban abokina, it's the only thing that's keeping me sane. Ko da yaushe daada ko aunty Zaliha suna kallona, ni kam daga gaisuwa babu abinda nake kara cewa kowa. In an bani abinci inci, in an bani magani in sha. Samarin gidan kullum suna son kula ni amma babu hali saboda suna tsoron aunty zaliha sosai. Amma ina ganin tausayina a idon su. Wanda muke magana dashi kawai shine mijin Aunty Zaliha, kullum in ya ganni palo zai ta tsokanata wai bafulatanar daji tazo birni ko yawo bata zuwa saboda kyauyenci. Kullum sai ina jin aunty zaliha ko daada sai sunyi waya da mommy amma bata taba cewa a bani ba, ni kuma ban taba cewa zan karba ba.

Rannan muna palo da aunty zaliha da Musbahu sai mommy ta kira suna magana ta tashi ta shiga daki dan kar inji me suke cewa, dama haka suke yi kullum. Tana shiga musbahu ya matso kusa dani yace "ya sunan sa?" A hankali nace "Sultan" when was the last time I called his name out loud? Yace "am sorry, I know what love feels like" a lokacin muka ji motsin aunty zaliha zata fito, yayi sauri ya matsa. Tana zuwa ta miko min waya "Fatima zata yi magana dake" na karba kawai ina kallon wayar, hannuna har rawa yake yi na saka a kunnena amma na kasa magana, can naji muryarta tace "Moon?" Wasu hawaye masu zafi suka zu bo min, banyi magana ba ta sake cewa " Moon banyi tunanin zaki dade haka ba, banyi tunanin abinda nayi planning zai dau lokaci ba" ta kuma yin shiru. A hankali nace "mommy ina daddy dasu ya Walid? Mommy in Hafsat ta haihu?" Ta jima bata yi magana ba, sanda tayi muryarta tayi alamar kuka, tace "duk lafiya lau suke, Hafsat bata haihu ba" desperately nace "mommy dan Allah ki bar ni ko waya ne inyi dasu" dif naji ta kashe, na saki wayar na rife fuskata da hannuna ina kuka. Jin muryar mommy ya daga min hankali sosai, gida kawai nake son zuwa. Aunty Zaliha ta dauke wayarta ta sake dialing number din mommy ta koma daki. Ina cikin kuka na naji an ajiye min wani abu a kan cinya ta, na dago kaina da sauri naga Musbahu yana min murmushi, na kalli cinya ta naga waya, a hankali yace "call him, but let it be our secret" gaba nane ya fadi sosai, shi kuma ya mike ya fice daga palon. Da sauri na dau wayar na saka a riga ta ina rarraba ido. I got a phone now, what do I do? Kar a kama ni kuma a kaini wani gurin da yake worse than here. Na tashi na shiga daki naga daada a kwance, nima na kwanta a gefenta na rufe idona kamar mai bacci ina ta lissafi a raina, menene yasa mommy kuka? Me ya faru a gidan? Me yasa tace abinda ta shirya is taking time? Ko dai wani abin ta saka aka yiwa Sultan kuma take regretting yanzu. Na shiga uku. Ina nan kwance har naji daada ta tashi ta shiga toilet, ta fito ta jima tana kallona sannan ta fita palo. Tana fita na mike na shiga toilet nayi locking kofar sannan na dauko wayar, babu security a jikin ta ya chire. Na shiga dialer da sauri na saka number din Sultan, na daga hannu zan dialing na kasa, what if something bad has happened to him? My heart can't take it, ya Ilahi. Sai kawai na goge number. Na saka number din daddy, ta gama ringing har ta katse bai dauka ba. Ya Allah. Na sake re-dialing ina lissafo sunayen Allah a ziciyata. Ringing na uku ya dauka "salamu Alaikum" a hankali nace "daddy" ya danyi shiru sai yace "Moon? Is that you?" Sai hawaye na kasa magana, yace "my God, Moon kiyi min magana mana, a ina kike? Ina Fatima ta kai min ke? Are you Ok?" Kuka ne yaci karfina nace "daddy ina Agadaz" yace "what? Agadaz fa kika ce? Yanzu Fatima cikin extreme saharar agadaz ta kai min yarinyar? To uban wa ta sani a agadaz din?" Nace "aunty Zaliha tsohuwar kawarta ta office dinsu" yace "Zaliha? Dama agadaz suka koma? Are they treating you well? Ko tabo na gani a jikin ki sai na dau mataki akai" nace "daddy am OK. Yaron gidan ne ya taimaka min da aron yawarsa. Please daddy kar asan shi ya bani" yace "don't worry about him, I will come and pick you up tomorrow. OK? Kar ki gayawa kowa kin kira ni, OK?" Na gyada kai kamar yana kallona. Har yanzu hawaye bai tsaya a ido na ba. A hankali nace "Daddy how is Sultan?"

Godiya marar adadi ga duk masoyana masu bibiyar lafiyata, Alhamdulillah lafiyata kalau, biki ne dai muke yi shi yasa akaji shiru. Nagode Allah ya bar zumunci.

Na samu labarin wadansu masoyan moon a whatsaap suna shirya riot dan kwato mata 'yancinta, haha, to sai ku shirya zuwa Agadaz, amma sai dai kuje ku kadai dan ni ban shirya zuwa sahara da zafin nan ba. Lol

I love you all 💖

Episode Fifty Three : Daddy
Chapter 75 · 0% Book details