← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 155 OF 190

Sashe 155

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Episode Eighty Four : Little Love

Ya dago ya kalle ni nayi masa murmushi ya sake kallon hoton sannan yace " then she is alive. All this time ina tunanin cewa bata raye shi yasa bata neme ni ba, amma tana raye ashe, kawai ta ajiye ni tayi tafiyarta, without a second thought" nace "please Sultan kar ka ce haka mana. Baka san uzurin ta ba. Ka bari idan ka samu lafiya sai mu tafi har Riyadh din mu same ta acan, ka gabatar mata da kanka, na tabbatar zata yi maka gamsashshen bayani a dangane da wacece ita" tun kafin in karasa maganar yake girgiza kansa, yace "I will not go, babu inda zanje, haka kawai muje ta wulakanta mu? Kamar yadda ta wulakanta ni ta ajiye ni ta tafi? If she wants to see me ai tasan a inda ta barni, in tana son ganina tazo inda nake" nayi sauri nace "sultan uwa ce fa, kar ka fadi mata maganar da Allah zaiyi fishi damu kuma" yace "ko menene nace mata Allah ba zai kama ni ba. I don't know much about love but naji ana cewa mother's love is the purest of love, hakan yana nufin ya kamata ace sonda take min yafi son da nake miki yawa, ni kuma nasan a yanzu yadda nake jinki a raina rabuwa dake will be the end of me. Ita wacce irin zuciya ce da ita?" Sosai naga ransa ya baci na tuna cewa bashi da lafiya, na karbi wayar daga hannunsa nace "sultan baka da lafiya, let's not talk about this now, in ka samu lafiya sai mu san abinda zamuyi akai" ya jawo ni jikinsa muka koma muka kwanta, ya jawo bargo zai rufe mu, temp dinsa naji da zafi na yaye bargon, ya rabu dani bai tanka min ba sai kara matse ni da yayi a jikin sa, yace "tell me something nice" banyi magana ba na dora hannunsa akan mara ta, yayi dariya kadan yace "yeah, that's a nice topic of discussion" ya danyi shiru sannan yace "mace nake so ki haifa, mai kama dake kuma mai halinki, kuma ina son itama take sona kamar yadda kike sona. Maimunatu zan saka mata" nayi sauri na kalle shi nace "maimunatu? Ai sai muyi maka yawa kuma" ya saka dan yatsansa yana zagaye lips dina dashi, abinda yake fara yi lokuta da dama in zai kissing dina, yace "kin taba ganin inda haske yayi wa mutum yawa a rayuwarsa? Gaba daya rayuwata a cikin duhu nake yinta sai da kika zo sannan kika fara haska min hanya, you brought so many blessings to me, uncountable, yanzu ga baby, to menene laifi dan na kira ta da moon itama, kogi ma ai baya kin dadi" naji dadin maganarsa amma nace "idan hasken yayi maka yawa kuma ai sai ya kashe maka ido ka kasa gani sosai" yace "sai in saka sunglasses" a tare muka yi dariya, abinda nayi tsammani shi ya biyo bayan dariyar tamu, hot kiss, wanda naji shi tun daga kafata har kaina, ganin yana neman zarcewa ya saka na ture shi nace "a asibiti fa muke baka da lafiya" ya shagwabe fuska "ni na warke ai" nace "to in ka warke ka bari a sallameka in munje gida koma menene za'ayi sai ayi, amma yanzu in wani ya shigo fa? Besides kai da baka da lafiya so kake ka karar da sauran karfinka ko?" Bai kula ni ba ya koma ya kwanta irin yaji haushin nan. Banyi aune ba kawai bacci ya dauke mu a haka, daga ni har shi.
Chapter 155 · 0% Book details