← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 190

Sashe 51

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bayan munje England ma haka ce ta kasance, kullum muna tare da Sultan a makaranta dan komawa yayi kamar shima student din ne. Kullum in muna tare sai nasan yadda nayi nayi masa nasiha ta sigar lumana, ina nuna masa this is right and this is wrong, amma ga mamaki na sai naga in aya na fara janyo masa sai ya karasa min, in hadisi na dauko sai ya gayamin wani irinsa, wato yana sane da duk abinda yake yi kenan. Abinda na kara fahimta a dangane dashi shine yana da zuciya, muguwar zuciya ma, wannan shi ya saka ya ke da fada, dan a makaranta kullum ina cikin rabon fada da Sultan. Allah yaso makarantar tana da girma shi yasa har yanzu siblings dina basu san da zaman sultan ba. Sannan kuma Sultan yana da mugun kishi dan ko kallona wani namiji yayi indai kallon bai gamshe shi ba yanzu zakuji kansa, ni har dariya yake bani dan ni mai mutane ce kowa nawa ne babu mace babu namiji. Haduwar su ta farko da Mahdi nayi introducing dinsu suka gaisa kamar gaske sai bayan mahdi ya tafi sannan Sultan ya bata rai yace "I don't like him" nace "saboda me? He is nice and shine best friend dina a school dinnan" ya tsare ni da ido yace "amma kin san yana sonki" na sunkuyar da kaina nace "yes, but I don't love him, I love you".

Sau da yawa sai in samu kaina da comparing Sultan da Ibrahim. Sam basu da alaka, kamanninsu sun sha ban ban, yayinda Ibrahim yake da sanyi Sultan kuma zafi ne dashi, Ibrahim ustaz ne sultan is the total opposite of ustaz, amma abinda yake bani mamaki shine lokacin da muna tare da ibrahim har rigima mukayi dashi akan taba ni duk da kuwa lokacin ina kwaila amma sultan ko da wasa bai taba kai hannun sa jikina ba. Situation din da muke ciki da Sultan is exactly wanda muka kasance da Ibrahim, yadda yake bina duk inda na tafi, yadda yake sona kamar ya cinye ni, da kuma yadda duk nake boye su daga gurin iyayena. They are totally different but exactly the same.

A hankali ina ganin chanji a halayen Sultan, yana behaving kansa especially if I am around. Kuma har yau ban taba ganin shi a buge ba kuma na kasa tambayar sa saboda bansan yadda zai dauki maganar ba, amma nasan ko da yana shan giya to ba sosai ba saboda shi dan giya ko yayane sai an gane shi. Shakuwa ce sosai take kara shiga tsakanin mu kuma Sultan is an open guy, komai nasa yana gayamin saboda koda yaushe yana gayamin shi baya son secret. Rannan muna zaune a school yace min "tell me Love, akwai wani guy da ya kamata in san da zamansa? Ina nufin akwai wani da kuke tare kafin ni ko akwai wani da yake sonki bayan ni? I want to know" nayi shiru ina auna maganar sa, bana jin zan iya gaya masa labarin Ibrahim, there is no need saboda by now na tabbatar cewa Ibrahim ba zai dawo ba, nace "actually there is one guy, sunanshi munir" nan na gaya masa labarin munir da alkawarin baffa nayi mana aure in na gama makaranta ba tare da miji ba. Sultan ya saka hannu a cikin gashinsa yana hargitsawa, dabi'ar dana lura yana yi duk sanda wani abu ya taba zuciyarsa, shi yasa kullum gashinsa yake a hargitse. Na saka ido na a cikin nasa nace "wannan shi yasa nake son ka nutsu yadda zan kaika gida kafin in gama project dina" ya bata fuska yace "am trying, really trying, but this is me, I can't just change over night" naga maganar tana so ta bata masa rai sai na chanja topic din nace masa "to kai fa? Any girl that I should know of?" Nan take murmushi ya yi replacing damuwar sa yace "No, not Sultan. Ban taba son wata ba sai ke though akwai yarinyar da take sona, Khulsum, kanwar Hajiya ce. Farkon dawowa ta Nigeria na tarar da ita a gida, she is a good cook ni kuma I love food sai take yi min girki kullum then I realized tana da hidden agenda sai nayi ending alakar mu, she might still be in love with me duk da dai mun dade bamu hadu ba" na gyada kaina nace "it's OK" amma cikin raina na dan ji babu dadi especially inda yace ta iya girki, in akwai abinda ban iya ba a rayuwata girki ne, lol.

Bayan kwana biyu nayi deciding zan kai Sultan gidan Hafsat su gaisa. Tun safe na kira ta na gaya mata zanzo kuma zan kawo bako, sannan na gaya mata cewa I also want him to meet Zayed. Da yake ranar Weekend ce sai na gaya wa mommy zanje gidan Hafsat tace a dawo lafiya, dama mun gama plan din inda zamu hadu da sultan dan haka muna fita da driver na gaya masa inda zai kaini, muna zuwa na tarar already Sultan yana jira na dan haka nayi changin mota. Tare muka shiga palon Hafsat da sallama. Suka amsa a tare ita da Zayed. Idan sunyi mamakin ganin Sultan to sun boye dan sam banga alama a fuskar su ba. Muka zauna mu hudu muka yi ta hira, nayi ta sha'awar Hafsat da Zayed, yadda suke abubuwansu, Arabic din Hafsat ya gyaru sosai dan dashi suke magana da Zayed. Zayed yayi ta yiwa Sultan tambayoyi shi kuma yana amsawa truthfully, saboda gaskiya Sultan ba shi da karya ko kadan, bashi da boye2, duk abinda ka tambayeshi zai gaya maka, either ka karba ko ka bari. Tare mu kaci abincin rana bayan munyi sallar Zuhr, daga nan su Sultan suka fita suka barmu. Na kalli Hafsat nace "so... Fadi abinda yake ranki" tace "he loves you, that's for sure. But he is Sultan, kinsan sunan da yayi a Nigeria babu inda babu labarinsa da labarin takadirancin sa. Kema kanki kinsan cewa kin debo da zafi Moon. Kuma na tabbatar cewa har yanzu a gida ba'a san da maganar sa ba ko an sani?" na girgiza kaina, ta cigaba da cewa "you are making the same mistake as you do with Ibrahim. Bana so ki shiga da yawa kamar yadda kika shiga son Ibrahim kuma abin yazo baiyiwu ba kika zo kika shiga wani hali" nace "so nake inga na chanja shi kafin in kaishi gida, He is a good guy, kawai dai ya riga yayi wa kansa ado ne da bakin fenti, I want to have a chance dazan yi presenting dinsa as the good guy he is" Hafsat ta girgiza kanta tace "you may not have that chance, kawai kisa rana ki kai shi, in yes, yes in no, no, shikenan an wuce gurin" ita Hafsat bata fahimci cewa no dinne zuciya ta ba zata iya dauka ba, bayan heart break din dana samu akan Ibrahim bana jin zan iya daukar wani heart break din na rabuwa da sultan. Ina so inyi ta jan lokaci for as long as possible saboda bana son rabu da shi. A hanyar mu ta komawa gida sultan ya lura da changin yanayi na ya tambayeni "me ya faru?" Na girgiza kaina nace "babu komai" ya saka hannunsa a gashin sa yace "she doesn't like me ko?" Nace "no ba haka bane wallahi, ta nuna min ya kamata in kaika gida gurin daddy ni kuma am not ready yanzu" ya hade rai yace "why not? ni am ready, ke kawai nake jira ki kirawo ni" na kalle shi naga da gaske yake babu wasa, he is strong, very strong, stronger than Ibrahim, dan nasan Sultan ba zai taba guduwa ya barni ba, ba zai taba rabuwa dani ba sai dai ni in rabu dashi, wannan kuma shine abinda nake tsoro, tunda Sultan yazo duniya yake shan wahala mutane suke juya masa baya da nuna masa kiyayya, bansan abinda zai faru dashi ba in nima iyayena suka tilastamin na rabu dashi.
Chapter 51 · 0% Book details