Sashe 38
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daga ranar kullum Zayed yazo sai ya neme ni munyi hira, tun Hafsat tana tashi in nazo har ta hakura take zama. Na fahimci cewa suna matukar san junan su kuma ni a idona sunyi bala'in dacewa. Zayed yayi min a matsayin brother in law.
Muna kokarin gama clinical din mu ne rannan da weekend naga Hafsat kamar hankalinta a tashe, nayi niyyar in rabu da ita sai kuma dai na kasa, na tambayeta, har ta shareni sai kuma ta dawo kusa dani ta zauna. Tace "Zayed ne zai zo ya gaishe da daddy yau" nan da nan na washe baki na da murna nace "Allah?, to kuma menene abin bata ran ke da zakiyi murna" tace "I am scared moon, gani nake kamar za'a samu matsala, and I really love Zayed you know" sosai na gane yadda take ji saboda nima na taba kasancewa a irin exact position din ta, nan na shiga lallabata ina cewa "daddy ba zai taba kin someone like Zayed ba". Wajen yamma yazo, Hafsat kasa fita tayi dan gabaki daya jikin ta karkarwa yake yi. Sai ni na fita na shigo dashi main palo sannan naje na gayawa daddy yayi bako a palo, sai da daddyn ya fito sannan na tashi na dawo daki, akan sallaya na tarar da Hafsat tana ta faman jan charbi, har dariya taso ta bani amma na dake, kawai na tuno ranar da Ibrahim yazo gidan mu a Abuja yadda securities suka ringa maltreating dinsa, Zayed kuwa yanzu yana zuwa har wani bashi guri suke yi suna gaishe shi, a raina nace rayuwa kenan, if you have money you have everything. Muna nan zaman jiran sakamako ni har na fara bacci naji Hafsat tana kiran sunana, na tashi na hango ta akusa da window, nima naje na leka, Zayed, daddy da ya Walid muka hango suna tafiya hanyar gate, daga ganin yadda suke cikin nishadi kasan an samu nasara, Zayed bakinsa har kunne. Hafsat ta rungume ni itama tana murna, kawai sak naji kwalla a idona. Inama Ibrahim ne muma hakan ta kasance damu. Su daddy basu jima da dawowa cikin gida ba ya kirani a waya yace muzo ni da Hafsat. Hafsat duk kunya ta ishe ta. Muna zuwa kuwa kowa ya fara tsokanarta wai ta dauko balarabe dan take yin aikin Hajji da umra a free. Sai da akayi shiru sannan daddy yace " Hafsat naga sakon ki, kuma ni dai a ra'ayina ni da mommyn ki munyi na'am da zabin ki. Amma na gaya masa in kun gama wannan session din zamu je Nigeria sai ya saka time ya turo magabatan sa sune 'yalleman su gaida baffa da kawunnan ki, su zasu bada auren ki bani ba, suma kuma ina saran insha Allah ba za'a samu matsala dasu ba. Allah ya sanya alkhairi" gaba daya muka ce "Ameen" ya Walid ya kalleni yace "saura ke" nayi sauri na sunkuyar da kaina. Daddy yace "eh Maimunatu saura ke. Ya kuke ciki ne da wannan farin yaron dan Datti Sufyan?" Nayi sauri na dago kaina nace cikin in ina "ba.. ba komai daddy" yace "bangane babu komai ba, dama ba saurayin ki bane?" Na girgiza kaina, yace " to maimunatu, kinsan dai akwai maganar Munnir har yanzu, kuma ni Allah ya sani bana son hadin ku da munnir, amma babu yadda zanyi indai har baki fito da miji ba kafin nan kafin ku kammala karatunku" Mommy tayi ajiyar zuciya tace "ni na rasa gane kan Moon wallahi, kamar wadda take gudun samarin, who would have thought Hafsat zata riga Moon samun miji
Episode Thirty Four : Back to Square One
Daddy ya tashi ya shige daki. Yana shiga Hafsat ta mike ta fada cinyar mommy ita kuma ta rungume ta suna dariya, nima dariyar nake yi amma ta yaqe ce, maganar daddy ce take yi min yawo aka, tabbas nasan munir bashi da niyyar hakura, kuma nasan in har na gama school bani da wani sauran excuse, ballantana yanzu idan iyayen Zayed suka je neman auren Hafsat kowa kuma hankalinsa dawo wa kaina zaiyi. Ina cikin wannan lissafin naji maganar mommy wacce ta sake daga min hankali "ai naji yace ma indai har su baffan sun amince acikin hutun nan naku yake so ayi komai a gama, in yaso kya karasa project dinki a gidan sa, kinga nan da baifi wata biyar ko shida ba za'a gama komai" Hafsat ta boye fuskar ta a cinyar mommy wai ita kunya, su yaya Habeeb suna ta tsokanarta da amarya, ni kuwa, shock din maganar ne ya daskarar dani a inda nake zaune, mommy ta kara da cewa "ni dai kam ni aka tasa a tsaye, lokacin yayi min kadan gaskiya, saboda ni plan dina shine nan da kamar shekara biyu masu zuwa, so nayi yadda kuka taso tare ke da moon in hada ku rana daya in aurar daku shikenan" I have heard enough, na mike zuciya ta tayi min nauyi na kama hanyar fita, ina jiyo su suna ta making plans, mommy ta kira daada tana gaya mata. Ina fita part dinmu na shiga, sai kuma na rasa me zan dauka, sai kawai na dauki hijab dina na saka na kama hanyar gate. Ni kaina bansan inda zani ba, I just want to get away for a while. Baifi saura wata biyu ya rage mana muyi hutu ba, muna yin hutu zamu tafi Nigeria. Allah ne kadai yasan irin abinda zan fuskanta a can. Dan jiki na yana bani baffa zai iya cewa a hada aure na dana Hafsat, da zarar nace bani da saurayi kuwa za'a ce ai ga munnir nan yana ta zaman jira. Allah ya gani bazan iya auran munnir ba. I despise him. To ko Mahdi zan lallaba ne? But I don't love him and I will end up hurting him. Ya Ilahi. Ina fita gate na hango motar Zayed a gurin da yake tsayawa in yazo gurin Hafsat. Na juya na fara tafiya in opposite direction, ina jinsa yana horn kuma nasan dani yake amma naki juyowa. Ban ankara ba sai ganin mota nayi a gaba na, yayi winding glass din motar ya kalle ni da murmushi a fuskar sa "beautiful one ina zaki je ne haka ke kadai kuma a kafa?" Nayi niyyar inyi banza in rabu dashi tunda duk shi ya ja min daya dauko maganar auren Hafsat amma kuma sai na kasa, it is not in my nature wulakanta mutane. Na karasa kusa da motar sa nace "nan baya zan je ba nisa" daga yadda yake kallona nasan bai yarda da maganata ba, ya bude kofar motar yace "shigo in kai ki" na danyi jim sai kuma na shiga. Ina zama yace "What is wrong" kawai sai jin hawaye nayi yana zubo min, nayi sauri na rufe fuskata da hannuna na fara kuka. Ya gyara packing din motar ya zauna, bai ce min komai ba, bai kuma rarrasheni ba, sai da nayi kuka na me isa ta sannan na dube fuskata ina goge idona da hannuna, ya miko min box din tissues, sannan ya sake tambayata "what's wrong?" Nan take na fara bashi labarin tun farkon haduwar mu da Ibrahim, aikin da na saka daddy ya samo masa, graduation din mu, yadda ta kasance ranar da yazo gidan mu da tafiyarsa, dawowarmu England da labarin aurensa,na kara da cewa "har yau babu shi babu labarinsa, he might be dead for all I know. Amma na kasa chire shi daga raina, na rage tunaninsa amma na kasa mantawa dashi, I can't fall in love again" sannan sai na bashi labarin Munnir, na kuma bashi labarin Mahdi. Na kara da cewa "yanzu muna zuwa Nigeria aka fara maganar ku da Hafsat, shikenan hankalin kowa zai dawo kaina, ko dai in fito da miji, which I don't have, ko kuma a aura min Munnir, who I don't love". Nayi shiru idona a lumshe ina sauraren yadda zuciyata take bugawa. Zayed yayi gyaran murya yace "do u want the truth?" Ba tare da na kalle shi ba na gyada kaina. A hankali yace "He is not coming back" na juyo da sauri na kalleshi ya gyada min kai tare da maimaitawa "he is not coming back" na dauke kaina na daina kallonsa, yacigaba da cewa "he left because he weak and unsure of himself, yes, sanda ya tafi maybe yana da niyyar dawowa sanda yaji he is strong enough, auren sa ya kara rage chances dinsa of coming back to you saboda matarsa zata yi iya kokarinta wajan janye hankalinsa daga kanki, da zarar ta haihu kuma shikenan hankalinsa zai kara karkata kan 'ya'yansa. After almost five years kuwa his chance of coming back to you is zero percent. Dole ki saka a zuciyarki kuma ki yadda da fact that he is not coming back. Abu na farko kenan. Abu na biyu shine, dole kiyi opening heart dinki for another man. Love at first sight is very rear dan haka idan guy yace yana sonki kamata yayi ki bashi chance, get to know him sannan zaki san cewa you can love him or not. You are very young and very beautiful Moon, your life is just starting, kar ki bar wani can da maybe ya manta dake yayi ruining happiness dinki. Open your heart to both Munnir and Mahadi and whoever else comes your way. Kina jina Moon?" Na gyada kaina yayinda wasu siraran hawaye suka biyo kuncina. Ya cigaba "daga duk kan stories dinki da nake ji a gun Hafsat, na fahimci cewa you have a good heart, mutane like you, I mean people with good heart sun fi kowa facing challenges a rayuwa akan harkar aure, kasuwanci da sauran al'amuran rayuwa saboda Allah yana testing din su yaga how good they are saboda He is saving something good for them"
Idan kana ta samun matsala a rayuwa, kuma ka tabbatar baka da hakkin kowa akan ka, ka tabbatar kana bin iyayenka kuma kana da zuciya mai kyau wacce babu hassada babu ganin kyashi babu kwadayi ko zalunci a ciki, to ka tabbatar cewa jarabawa ce daga Allah kuma in har kaci jarabawarka to sakamakon ka zai zamo something very good aduniya da kuma lahira. Allah ya bamu dacewa, Ameen.
Muna kokarin gama clinical din mu ne rannan da weekend naga Hafsat kamar hankalinta a tashe, nayi niyyar in rabu da ita sai kuma dai na kasa, na tambayeta, har ta shareni sai kuma ta dawo kusa dani ta zauna. Tace "Zayed ne zai zo ya gaishe da daddy yau" nan da nan na washe baki na da murna nace "Allah?, to kuma menene abin bata ran ke da zakiyi murna" tace "I am scared moon, gani nake kamar za'a samu matsala, and I really love Zayed you know" sosai na gane yadda take ji saboda nima na taba kasancewa a irin exact position din ta, nan na shiga lallabata ina cewa "daddy ba zai taba kin someone like Zayed ba". Wajen yamma yazo, Hafsat kasa fita tayi dan gabaki daya jikin ta karkarwa yake yi. Sai ni na fita na shigo dashi main palo sannan naje na gayawa daddy yayi bako a palo, sai da daddyn ya fito sannan na tashi na dawo daki, akan sallaya na tarar da Hafsat tana ta faman jan charbi, har dariya taso ta bani amma na dake, kawai na tuno ranar da Ibrahim yazo gidan mu a Abuja yadda securities suka ringa maltreating dinsa, Zayed kuwa yanzu yana zuwa har wani bashi guri suke yi suna gaishe shi, a raina nace rayuwa kenan, if you have money you have everything. Muna nan zaman jiran sakamako ni har na fara bacci naji Hafsat tana kiran sunana, na tashi na hango ta akusa da window, nima naje na leka, Zayed, daddy da ya Walid muka hango suna tafiya hanyar gate, daga ganin yadda suke cikin nishadi kasan an samu nasara, Zayed bakinsa har kunne. Hafsat ta rungume ni itama tana murna, kawai sak naji kwalla a idona. Inama Ibrahim ne muma hakan ta kasance damu. Su daddy basu jima da dawowa cikin gida ba ya kirani a waya yace muzo ni da Hafsat. Hafsat duk kunya ta ishe ta. Muna zuwa kuwa kowa ya fara tsokanarta wai ta dauko balarabe dan take yin aikin Hajji da umra a free. Sai da akayi shiru sannan daddy yace " Hafsat naga sakon ki, kuma ni dai a ra'ayina ni da mommyn ki munyi na'am da zabin ki. Amma na gaya masa in kun gama wannan session din zamu je Nigeria sai ya saka time ya turo magabatan sa sune 'yalleman su gaida baffa da kawunnan ki, su zasu bada auren ki bani ba, suma kuma ina saran insha Allah ba za'a samu matsala dasu ba. Allah ya sanya alkhairi" gaba daya muka ce "Ameen" ya Walid ya kalleni yace "saura ke" nayi sauri na sunkuyar da kaina. Daddy yace "eh Maimunatu saura ke. Ya kuke ciki ne da wannan farin yaron dan Datti Sufyan?" Nayi sauri na dago kaina nace cikin in ina "ba.. ba komai daddy" yace "bangane babu komai ba, dama ba saurayin ki bane?" Na girgiza kaina, yace " to maimunatu, kinsan dai akwai maganar Munnir har yanzu, kuma ni Allah ya sani bana son hadin ku da munnir, amma babu yadda zanyi indai har baki fito da miji ba kafin nan kafin ku kammala karatunku" Mommy tayi ajiyar zuciya tace "ni na rasa gane kan Moon wallahi, kamar wadda take gudun samarin, who would have thought Hafsat zata riga Moon samun miji
Episode Thirty Four : Back to Square One
Daddy ya tashi ya shige daki. Yana shiga Hafsat ta mike ta fada cinyar mommy ita kuma ta rungume ta suna dariya, nima dariyar nake yi amma ta yaqe ce, maganar daddy ce take yi min yawo aka, tabbas nasan munir bashi da niyyar hakura, kuma nasan in har na gama school bani da wani sauran excuse, ballantana yanzu idan iyayen Zayed suka je neman auren Hafsat kowa kuma hankalinsa dawo wa kaina zaiyi. Ina cikin wannan lissafin naji maganar mommy wacce ta sake daga min hankali "ai naji yace ma indai har su baffan sun amince acikin hutun nan naku yake so ayi komai a gama, in yaso kya karasa project dinki a gidan sa, kinga nan da baifi wata biyar ko shida ba za'a gama komai" Hafsat ta boye fuskar ta a cinyar mommy wai ita kunya, su yaya Habeeb suna ta tsokanarta da amarya, ni kuwa, shock din maganar ne ya daskarar dani a inda nake zaune, mommy ta kara da cewa "ni dai kam ni aka tasa a tsaye, lokacin yayi min kadan gaskiya, saboda ni plan dina shine nan da kamar shekara biyu masu zuwa, so nayi yadda kuka taso tare ke da moon in hada ku rana daya in aurar daku shikenan" I have heard enough, na mike zuciya ta tayi min nauyi na kama hanyar fita, ina jiyo su suna ta making plans, mommy ta kira daada tana gaya mata. Ina fita part dinmu na shiga, sai kuma na rasa me zan dauka, sai kawai na dauki hijab dina na saka na kama hanyar gate. Ni kaina bansan inda zani ba, I just want to get away for a while. Baifi saura wata biyu ya rage mana muyi hutu ba, muna yin hutu zamu tafi Nigeria. Allah ne kadai yasan irin abinda zan fuskanta a can. Dan jiki na yana bani baffa zai iya cewa a hada aure na dana Hafsat, da zarar nace bani da saurayi kuwa za'a ce ai ga munnir nan yana ta zaman jira. Allah ya gani bazan iya auran munnir ba. I despise him. To ko Mahdi zan lallaba ne? But I don't love him and I will end up hurting him. Ya Ilahi. Ina fita gate na hango motar Zayed a gurin da yake tsayawa in yazo gurin Hafsat. Na juya na fara tafiya in opposite direction, ina jinsa yana horn kuma nasan dani yake amma naki juyowa. Ban ankara ba sai ganin mota nayi a gaba na, yayi winding glass din motar ya kalle ni da murmushi a fuskar sa "beautiful one ina zaki je ne haka ke kadai kuma a kafa?" Nayi niyyar inyi banza in rabu dashi tunda duk shi ya ja min daya dauko maganar auren Hafsat amma kuma sai na kasa, it is not in my nature wulakanta mutane. Na karasa kusa da motar sa nace "nan baya zan je ba nisa" daga yadda yake kallona nasan bai yarda da maganata ba, ya bude kofar motar yace "shigo in kai ki" na danyi jim sai kuma na shiga. Ina zama yace "What is wrong" kawai sai jin hawaye nayi yana zubo min, nayi sauri na rufe fuskata da hannuna na fara kuka. Ya gyara packing din motar ya zauna, bai ce min komai ba, bai kuma rarrasheni ba, sai da nayi kuka na me isa ta sannan na dube fuskata ina goge idona da hannuna, ya miko min box din tissues, sannan ya sake tambayata "what's wrong?" Nan take na fara bashi labarin tun farkon haduwar mu da Ibrahim, aikin da na saka daddy ya samo masa, graduation din mu, yadda ta kasance ranar da yazo gidan mu da tafiyarsa, dawowarmu England da labarin aurensa,na kara da cewa "har yau babu shi babu labarinsa, he might be dead for all I know. Amma na kasa chire shi daga raina, na rage tunaninsa amma na kasa mantawa dashi, I can't fall in love again" sannan sai na bashi labarin Munnir, na kuma bashi labarin Mahdi. Na kara da cewa "yanzu muna zuwa Nigeria aka fara maganar ku da Hafsat, shikenan hankalin kowa zai dawo kaina, ko dai in fito da miji, which I don't have, ko kuma a aura min Munnir, who I don't love". Nayi shiru idona a lumshe ina sauraren yadda zuciyata take bugawa. Zayed yayi gyaran murya yace "do u want the truth?" Ba tare da na kalle shi ba na gyada kaina. A hankali yace "He is not coming back" na juyo da sauri na kalleshi ya gyada min kai tare da maimaitawa "he is not coming back" na dauke kaina na daina kallonsa, yacigaba da cewa "he left because he weak and unsure of himself, yes, sanda ya tafi maybe yana da niyyar dawowa sanda yaji he is strong enough, auren sa ya kara rage chances dinsa of coming back to you saboda matarsa zata yi iya kokarinta wajan janye hankalinsa daga kanki, da zarar ta haihu kuma shikenan hankalinsa zai kara karkata kan 'ya'yansa. After almost five years kuwa his chance of coming back to you is zero percent. Dole ki saka a zuciyarki kuma ki yadda da fact that he is not coming back. Abu na farko kenan. Abu na biyu shine, dole kiyi opening heart dinki for another man. Love at first sight is very rear dan haka idan guy yace yana sonki kamata yayi ki bashi chance, get to know him sannan zaki san cewa you can love him or not. You are very young and very beautiful Moon, your life is just starting, kar ki bar wani can da maybe ya manta dake yayi ruining happiness dinki. Open your heart to both Munnir and Mahadi and whoever else comes your way. Kina jina Moon?" Na gyada kaina yayinda wasu siraran hawaye suka biyo kuncina. Ya cigaba "daga duk kan stories dinki da nake ji a gun Hafsat, na fahimci cewa you have a good heart, mutane like you, I mean people with good heart sun fi kowa facing challenges a rayuwa akan harkar aure, kasuwanci da sauran al'amuran rayuwa saboda Allah yana testing din su yaga how good they are saboda He is saving something good for them"
Idan kana ta samun matsala a rayuwa, kuma ka tabbatar baka da hakkin kowa akan ka, ka tabbatar kana bin iyayenka kuma kana da zuciya mai kyau wacce babu hassada babu ganin kyashi babu kwadayi ko zalunci a ciki, to ka tabbatar cewa jarabawa ce daga Allah kuma in har kaci jarabawarka to sakamakon ka zai zamo something very good aduniya da kuma lahira. Allah ya bamu dacewa, Ameen.