← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 190

Sashe 80

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mamaki ne ya hana sultan motsawa har suka saka masa ankwa suka fita dashi, lallai mommy ta nuna masa ta fishi shekaru. Ranar a station ya kwana. Bai damu ba, tunanin sa daya shine ina Moon take. Washe gari da sassafe aka turo daga fada akayi bail dinsa, not because an damu dashi but to protect the family name, yana zuwa gida ya tarar da takardar sammaci a kotu, mommy ta kai shi kara, kuma a takardar ance ya sace Moon, dan haka ana tubumarsa daya fito da ita. Duk abinda yake na glass a part din Sultan ranar sai da ya fasa shi, duk ya jiwa hannunsa ciwo, sai da Amir ya kira galadima sannan ya samu kan sultan. Nan da nan Takawa ya fara neman yadda za'a samu alkalin da aka kaiwa karar a kashe maganar ba tare da yasan 'yar waye ma ake rigima akanta ba. Babu wanda ya kira sultan ya tambayeshi ba'asin mai ya faru ko kuma yayi masa fada. Bayan la'asar Amir ya kira masu gyara suna ta aimin gyaran part din Sultan, Sultan ya sulale ya fice daga gidan, gidan su Moon ya koma, gate din a bude yake kamar gidan a cike yake, yayi packing ya fito direct ya nufi gate din yana shiga David ya tso ya tare shi, David shine chief security din gidan, katon gaske ne dan Moon tun tana rayinya take tsoronsa, amma naushi daya Sultan yayi masa sai ga David akan gwuiwoyinsa yana kokarin dawo da numfashinsa, nan take sauran securities din sukayi kansa.

Hayaniyar da suke yi ce ta jawo hankalin daddy wanda yake tsaye ya tsare mommy da ido bayan ta amsa masa da "she is safe" ya fita da sauri su Walid suna binsa a baya. Scene din da ya gani a compound dinsa ne yasa ya saki baki yana mamaki, already Sultan ya zubar da mutun uku a kasa, yana ganin daddyya fito ya gane shi dan yasha ganin pictures dinsa a wayat Moon, ya karaso gabansa da sauri, yana zuwa ya zube akan gwuiwarsa, yana haki yace "Sunana Abubakar Sadiq Abdallah, I am a drunk, I don't know who my mother is and my father hates me, na taba zama a gidan kangararru, I have a bad temper, I get in trouble most of the times and I have heavy criminal record with the police. Nazo ina neman auren 'yarka, Maimunatu"

Episode fifty five : Her Father's Daughter 2

Kowa a gurin sakin baki yayi yana kallon Sultan, hatta daddy rasa mai zaice masa yayi, ya jima yana kallon sa shi kuma Sultan ya sunkuyar da kansa kasa, a zuciyarsa yana wishing ina ma dai zai iya kuka, maybe in hawaye ya fito masa zai ji sanyi a zuciyarsa, wannan mutumin da yake tsaye a kansa is his only chance to happiness, idan yace yes to shi kam ya samu duk wani buri nasa na rayuwa, in yace no kuma tamkar a saka full stop ne a rayuwar sultan. Daddy ya sauke ajjiyar zuciya yace "wannan shine dalilin ka na shigo min gida ka tayar min da hayaniya? Wannan shine dalilinka na dukan securities dina?" Sultan ya kuma sunkuyar da kansa yana jin bugun zuciyarsa yana karuwa. Daddy yace "tambayarka nake yi fa?" Sultan ya dago kai ya kalli daddy da jajayen idanunsa yace "daddy ba zasu bar ni in ganka ba ne. And I must see you. Tun a England muka shirya da Moon za ta kawo ni gurinka, bamu samu dama ba, anan ma muka sake shirin zuwa ganin ka shima still bamu dace ba. This is the only way for me to see you" da mamaki daddy yace "ita moon dince ta amince maka kazo gurina ka nemi auren ta?" Sultan ya gyada kansa yace "yes daddy, kuma yanzu I don't even know where she is" daddy ya jinjina maganar a ransa, in dai har Moon ce ta turo shi gurinsa then she must have her reasons, maybe reasons dinta yana daga cikin dalilan da yasa mommy ta dauke ta. Ya juya ya kalli Walid a gefensa yace "Walid shigo dashi ciki" ya juya ya koma palo, walid ya bishi da kallon mamaki amma shi yasan bai isa yayi masa musu ba, yiwa iyaye musu baya daga cikin tarbiyyar da aka basu. Ya mika wa sultan hannu da niyar ya taimaka nasa ya tashi tsaye, sultan ya watsa masa harara ya mike a hankali yadda su biyu kadai zasu ji yace "zan dawo kanka ne" bai jira walid yayi masa jagora ba ya bi bayan daddy. Ya tarar palo babu kowa, da alama daddy sama ya hau, akan carpet ya zauna ya harde kafafunsa ya zabga tagumi. He is ready to wait to awa nawa ne, ko kwana nawa ne, indai har at last daddy zai saurare shi. Walid ya shigo ya samu guri can nesa da Sultan ya zauna, babu wanda yace wa kowa komai har daddy ya sauko, ya yi wanka ya chanza kaya sai kamshi yake, Sultan ya kalli kayan jikinsa, sun chukurkude saboda fadan da yayi da securities, babu abinda yake sai warin gumi, ya daga kafada bai damu ba.

Daddy ya zauna akan kujera yana studying Sultan. He is a perfect mixture of his father and mother. Fuskarsa sak ta Khairat sai dai kawai shi namiji ne ita mace, sai kuma duhun fata da ya fita saboda yayi mix da duhun fatar babansa, kirar jikinsa kuma sak na babansa lokacin yana age dinsa. Daddy yana hango su a idonsa suna wayo tare ko'ina a Oxford. What has gone wrong tsakanin su? Yayi gyaran murya yace "bismillah malan Abubakar, fara daga farko, a ina ka hadu da 'yata kuma menene a tsakanin ku?" Sultan ya danyi shiru yana controlling emotions dinsa sannan ya fara bada labari, komai sai da ya fada wa daddy, da boye boyen da suke yi saboda tana tsoron kawo shi gida, rayuwar su a England da America, amma duk bluntness din sultan bai bada labarin toilet experience dinsu ba, ya bada labarin plans din da suka ringa hadawa na zuwa ganin daddy amma ana samun sabani, ya bada labarin matsalar da suka samu akan project dinta da fushin da yayi ya tafi bar ita kuma ta bi Amir ya kaita gurin shi, ganin da munir yayi musu da zuwan Walid. Sai da ya gama kaf sannan yace "dan Allah daddy kar ka raba mu wallahi mutuwa zanyi, I have no body a duniyar nan sai ita" daddy ya kalle shi a nutse yace "you look like your mother" Sultan ya dago kansa da sauri ya kalli daddy yana tunanin anya kunnen sa ba karya yayi masa ba, sam babu wasa a fuskar daddy, ya sake cewa "kamar ku daya, sai dai ta fika fari, ta fika kuma hankali da nutsuwa" da rarrafe sultan ya karaso gaban daddy ya rike kafarsa yace "you know my mother?" Daddy ya gyara zama yana kallonsa yace "ba sosai ba, dan bamu taba magana da ita ba, amma na san ta kuma ina ganin ka nasan dan ta ne kai. Oxford sukayi karatu ita da babanka, lokacin yana kamar ka. Baban ka was exactly like you, he was a rogue also. A gang leader na 'ya'yan masu kudi" daddy yayi murmushi yana tuno rayuwarsu ta makaranta yacigaba da cewa "ni lokacin dan talakawa ne dan haka bana cikin su, ina dai hangen su suna yawo da motoci a cikin makaranta. He was so energetic, so stubborn like you. Duk sanda na ganshi a TV yanzu sai inyi ta mamakin yadda akayi ya koma haka" sultan ya saki baki yana mamaki, bai taba tsammanin cewa da akwai wani abu na halayya daya dangantashi da babansa ba. A hankali yace da daddy, "please tell me about my mother" daddy yace "kamar yadda na gaya maka, ban santa sosai ba, nasan dai sunanta khairat, and i always say, she is the most beautiful woman I have ever seen. She is full blood Arab. Tana da nutsuwa sosai, kuma daga ganin ta daga babban gida ta fito. They were so much in love ita da Sadiq. I remember always thinking they look odd, ita so fair shi kuma so dark, ita gentle shi stubborn, ita Arab shi Hausa. Amma duk 'ya'yan masu kudi. Muna gama PhD suka bar Oxford, ni kuma na zauna na kama lecturing a can. Ban taba dauka sun rabu ba. Shi yasa nayi mamaki da kace min baka san mamanka ba, and you said something about your father hating you. Ban gane me kake nufi ba. Why will your father hate you?" Sultan ya girgiza kansa yace "nima ban sani ba fa" nan ya fara bawa daddy labarin rayuwarsa tun sanda yayi wayo har zuwa haduwarsa da Moon. Duk abin ya daure wa daddy kai. He needs time to think about it. Sultan ji yayi kamar zai hadiye daddy, tunda yake babu wanda ya taba bashi labarin mahaifiyarsa, he only know her name shima kuma a birth certificate dinsa ya gani, yanzu yasan she is Arab, yayi murmushi, he always have a thing for Arabs, duk da ba wai iya larabcin yayi ba amma duk sanda yayi sai aji kamar a bakinsa aka rada shi ashe its in his blood. Ina ma dai one day zai ganta? Sai kuma ya cire maganar daga ransa, tunda har ta iya cire shi daga jikinta ta ajiye shi ta tafi without a second look to shima dan me zai nemeta. Suna tare da daddy har magrib sannan suka je masjid tare suka yi sallah daga nan daddy yace masa "kaje gida sultan, give Walid your number, I will think about maganar ka and I will call you" daga haka ya shige gida, Sultan yaji babu dadi, he don't want to go home, to menene a gidan ma in yaje? Shi da daddy zai barshi ma anan gidan zai zauna, it will make him feel closer to Moon and also to his Mom.
Chapter 80 · 0% Book details