← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 119 OF 190

Sashe 119

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Moon
Na sake rufe ido na ina kokarin saita numfashina tare da kiran "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" repeatedly a zuciya ta. Na bude ido na naga har yanzu Sultan ni yake kallo, jijiyoyin wuyansa da goshin sa sun fito rado rado. Na sake hadiyar yawu da kyar nace "Sultan, this is not what you are thinking" ya kalli handkerchief din hannun sa yace cikin shakakkiyar murya "this is your handwriting. Baki bani amsa taba, who is this man to you? What is he doing here today?" Nayi kokarin rike hannunsa ya matsa baya, cikin rawar murya nace "Sultan not here please. Nayi maka laifi, please ka bari muje wani gurin sai inyi naka bayani". Handkerchief din hannunsa ya dunkule ya jefo min a kirjina, ya juya baya ya koma inda yake dazu. Ban taba ganin bacin rai a fuskar sultan irin wanda nake gani yanzu ba. A hankali na juya gurin Hafsat da take tsaye kusa dani na dora kaina a kafadar ta na fara kuka. Muryar Amir naji yana magana "alright ladies and gentlemen, the party is over, we really appreciate your presence but you all need to leave now" na dago kai ina kallon mutane suna ta fita, friends dina ko sallama basu samu damar yi min ba duk Amir ya tisa keyar su suka fice, Amina da Hafsat ne kadai suka ki tafiya, mazan ma duk Amir ya koresu, amma sai na lura da gang bang ko mutun daya bai fita ba, sai kara samun guri suka yi suka zauna. Sultan na hango shi kadai yana tsaye ya juya bayan sa ya dora kafarsa akan kujera yana shan wani abu a cikin kofi. Gaba na ne ya fadi, oh dear God, no. This is all my fault, tun farko dana bawa Sultan labarin Ibrahim da duk haka bata faru ba. A hankali na fara takawa ina tafiya inda Sultan yake tsaye, na karasa bayansa na dora hannuna a kafadarsa nace "am sorry sultan" ya ture hannuna daga jikinsa ya juyo yana kallona da idanunsa da suka fara sauya color zuwa ja, yace cikin daga murya "why? Na sha tambayar ki in akwai wani wanda ya kamata in san da zaman sa amma kika ce min babu" kafin in bashi amsa naji muryar Ibrahim yace "sai ka tambayi kanka me yasa bata ba ka labarina ba, maybe it is because she is still in love with me" nan take idon Sultan ya karasa yin ja kamar garwashin wuta, ya juyo a fusace yace "please somebody should shut up that man for me" tun kafin ya rufe bakin sa kusan mutum biyar suka yi kan Ibrahim suka fara duka, durkushewa nayi a gurin na dora hannu na aka na fara rusa kuka ganin yadda suke ball da Ibrahim ta ko'ina. Banda Solomon wanda yake zaune a gefe ya dora kafa daya kan daya shan abinda yake cikin kofin hannunsa, wanda ko ba'a gaya min ba nasan irin abinda sultan yake sha ne, a cikin gida na ranar da aka kawo ni. Na rike rigar sultan ina kuka guiwowina a kasa "dan Allah Sultan ka kalle ni kaji abinda nake gaya maka, please ka hana su dukansa dan Allah" kamar wanda na kara tunzura shi ya juyo yace min "why? Me yasa ba kya so su dake shi? Saboda abinda ya fada gaskiya ne, saboda still kina sonsa?" Nayi saurin girgiza kaina nace "I don't love him sultan, I Love You, I chose you, I marry you. Menene kuma ya rage?" Cikin fada yace "you marry me sannan kika gayyato tsohon saurayinki cikin gida na?" Ban san sanda na dake shi a kafada ba nace "how can you say that? Come back to your senses Sultan" bai ce min komai ba sai tsayawa da yayi kamar mutum mutumi yana kallona, ta gefen idona na hango Solomon ya taso ya taho inda muke, yana karaso wa ya mika wa sultan kwalbar da take hannunsa, ba musu ya karba, da sauri na na fincike daga hannunsa na zubar da abinda yake ciki a kasa. Solomon ya saki baki yana kallona kafin ya fara magana "ni dama tunda aka bani labarin cewa our sultan has fallen in love with a good girl, nasan cewa we lost him, Sultan din dana sani ba zai zauna ayi masa irin cin mutuncin da aka yi maka ba, this means nan gaba sharing dinta za ka ke yi da sauran samarinta, only God knows su nawa ne, tunda baka san da wannan ba sauran ma ba zaka sanda su ba sai dai ka gansu a kan gadonta" a zuciye sultan ya juya ya kai masa duka yana cewa "shut up, damn you" ya rike hannun sultan yace "in baka son hakan ta faru then end it here, ka nuna min cewa har yanzu baka yi loosing guts dinka ba over a woman" hannunsa ya saka a aljihu ya zaro wani abu, ganin abun kawai ya saka naji wani zazzabi yana neman ya sauko min, Ya Allah intervene. Tunda nake ban taba ganin bindiga ba sai a film amma yau wai gani ga ita a daren farko na na aure. A hannun sultan ya saka bindigar yace a hankali "shoot him between the eyes, in kayi haka sauran babu wanda zai sake zuwa" gaba daya jiki na karkarwa yake yi dan bana jin bakina zai iya budewa har inyi magana. Amir ne ya karaso gurin da sauri fuskarsa cike da tashin hankali yayi kokarin karbar bindigar daga hannun sultan amma Solomon ya ture shi yace "stay out of this" yaje ya jawo Ibrahim wanda akayi wa laga laga, ya ajiye a gaban Sultan yace "Shoot him" na kama hannun sultan daya ke rike da bindigar nace "Sultan no" a hankali sultan ya dago kansa ya kalli Solomon yace calmly "no, I will not shoot him" ya juyo da jajayen idanunsa kaina ya ce "kince min you chose me over him, let's find out in gaskiya kike fada" ya saka min bindigar a hannuna yace "choose again, me or him" kallonshi kawai nake da mamaki, this is not my Sultan, this is someone else's. "Ki zaba, in har kina sonshi then put a bullet in me, in har kuma ni kike so kamar yadda kika fada then put a bullet in him" sama sama na ke jin sauran maganganun, naji Hafsat tana cewa da Sultan "baka da hankali Sultan? Menene hakan kake yi" na daga mata hannu alamar tayi shiru ba tare dana kalleta ba, no body will get hurt again a saboda ni, naji Solomon yana yiwa Sultan masifa "what if she shoots you?" Sultan yace "then so be it" Amir naji a kusa dani yana magana shima "Moon give me the gun" a hankali na fara jero sunayen Allah a zuciya ta, a take naji duk wani tsoro ya kauce min, na fahimci duk hikima ta ubangiji akan abubuwan da suka faru. This is a battle, Sultan's battle, between his good side and his bad side, I am his good side and Solomon and his other bad friends are his bad side. Yanzu na fahimci komai, na fahimci hikimar ubangiji da ya dawo da Ibrahim cikin rayuwata a wannan lokacin. Kamar yadda Ibrahim ya fada hakane, it is destiny amma ba destiny din zamuyi aure ba. Allah ya dawo da Ibrahim rayuwar mu ne saboda yana son yayi amfani dashi yayi testing Sultan, wannan duk jarabawa ce, ni kuma zanyi iya kacin kokarina inga na taimakawa Sultan gurin cin wannan jarabawar. I now understand everything and I know exactly what to do. Na gyara rikon bindigar a hannuna, it is heavier than it looks. A hankali na dago idona ina kallon rinannun idanun sultan, na motsa bakina na furta I Love You amma ba tare da sauti ba amma na tabbatar ya fahimci abinda nace. Na daga bindigar a hankali ina kallonta, cikin second daya na juya ta zuwa kaina sannan na lumshe idona na dora dan yatsa na akan trigger kamar mai niyyar harbawa. Exactly abinda nayi tsammanin zai faru shi ya faru, kafin in dora dan yatsa na akan trigger Sultan yazo gurin ya doke hannun bindigar ta fadi kasa, dama ba wani rikon kirki nayi mata ba, tana faduwa ya kankame ni tamkar zai tsaga kirjinsa ya sakani a ciki, jikinsa gaba daya karkarwa yake yi. This is my chance, a hankali na fara yi masa magana, yadda babu wanda zai ji daga ni sai shi "Na zabe kane saboda ina sonka, na aure ka saboda ina sonka, ban gaya maka labarin saba saboda bana son in bata maka rai, amma ina son ka sani, babu sauran sonsa daya rage min a zuciyata saboda zuciyata taka ce. Bani nace yazo ba kuma bansan menene yasa yazo ba. Na ce maka ka hana dukansa saboda nasan cewa kai mutumin kirki ne, kuma mutanen kirki basa rama sharri da sharri, mutane ne masu afuwa masu tausayi, mutanen da ubangiji yake alfahari dasu. Nayi kokarin hana ka harbin sa not because I care about him but because I care about you. Kisan kai yana daya daga cikin manyan laifuka da Allah baya so, bana son ka dauki zunubin sa akan ka. Na juyar da bindiga kaina ne saboda in nuna maka how much I Love You. I Love you more than my life it self". Ya jima yana rike dani sannan ya sake ni ya juya da sauri gurin da Ibrahim yake yace masa " GO. But I swear to God, in na kara ganin ka ten miles close to my wife I Will Shoot you". Hafsat ce da Amina suka zo gurina, na rungume daya daga cikin su ba tare da nasan ko wacece ba. Ina jin hayaniyar gang bang "Sultan ya za'ayi ka bar shi ya tafi?" "Har cikin gidan ka fa ya shigo gurin matar ka, har yana ce mata ta gudu daha gurinka" "lallai Sultan ka zama nusari, you are no longer one of us" Sultan yace "gida na ne, kuma matata ce, kuma ni nace masa ya tafi. Duk wanda yake da problem da decision dina will settle it with me" ta gefen ido na naga Amir yana fita da Ibrahim da ga gurin, sannan kuma daya bayan daya suka fara fita, Sultan ne na karshen fita.
Chapter 119 · 0% Book details