← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 190

Sashe 87

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

Na lumshe idona ina addu'ar Allah yasa shi dinne ya gani ba wai gizo yake yi min ba, dan ganin nasa ya taba min wani guri a zuciya ta wanda bansan yadda zanyi ba idan ba shi bane. Muna zuwa airport muka fito, mommy ce ta fara shigewa jirgi, daddy ya tsaya suna sallama da mutane, sai lokacin na samu damar ganawa da yaya Walid dan a mota tsoron mommy ya hana ni magana, na rungume shi tsam a jikina ina ajjiyar zuciya "I missed you" ya rabani da jikinsa yace "I missed you too sweetie pie" ta gefen idona na hango sultan yana tahowa gurin da muke, kara kankame yaya Walid nayi ina runtse idona, 'Oh Allah, give me the strength kar inje inji kunya a gaban mutane' na kasa kallon inda yake dan nasan zan iya loosing control, muryarsa naji yana cewa "to cika ta haka, ai an gama oyoyon" shi dinne dai, dan muryar sa ce wannan. Ya walid ya dafa kafaduna da hannayensa duk biyun yace "anki din, sai ka bari in an daura muku auren sai kayi min iko akanta amma yanzu tawa ce. Ni ban taba ganin ma suruki marar kunya irin kaba sultan, babban wa ai uba ne, ni ne fa madaurin auren ta, inna ga dama sai ince bazan bayar ba" yaushe Sultan suka fara wasa da Ya Walid? Last time I check ya Walid ya mari sultan. Wata dariya sultan yayi yace "kayi kadan yaro, ni iya kacin sanina na girme ka, dan haka kai ya kamata ka ke yi min biyayya" ya walid ya kama hannuna muka tafi jirgi, har yanzu na kasa kallon sultan, sai da muka fara hawa steps din sannan na juyo ina tunanin kar mu tafi mu barshi, ina juyo wa muka hada ido, nayi sauri na dauke kaina.

Chamber biyu ne da jirgin sai gurin pilots, daddy da mommy suna chamber din farko, mu kuma mu uku muna chamber ta biyu. Tunda na zauna har jirgin ya tashi ban daga kaina ba, duk jina nake a takure saboda idanuwan da sultan ya dora a kaina ko kiftawa baya yi. Ji nayi kallon yayi yawa na dan daga kaina kadan sai naga ashe ido hudu ne a kaina ba biyu ba, yau naga ta kaina zasu chinye ni danya. Ya walid yace "kin ganki kuwa? Wannan ai kece ifritu minal jinni. Wannan irin rama haka? Me Aunty Zaliha take miki?" Ni dai bance komai ba na rufe fuskata da hijab dina. Ina jin Sultan yana ce masa ya tashi ya koma gurin su Daddy, ya Walid yace "saboda me? Duk abinda zaka gaya mata ka gaya mata a gabana. Suma wadancan din couple ne, gwara ma ku ba aure ne da ku ba, babu wani abu da zakuyi wanda ba zan iya gani ba" su kayi ta maganganun su ina jinsu bance musu komai ba, shi Sultan yana ta insisting sai Walid ya tashi ya bamu guri shi kuma yaki. Nadan bude fuskata kadan na kallesu naga basa kallona sai na gyara zamana na bude fuskata sosai. A hankali nace ina kallon sultan "how is your leg?" Duk suka jiyo suna kallona da mamaki Sultan yace "What?" Na sake maimaitawa ina kallon kafarsa. Still bai gane mai nake nufi ba, nace "kafarka da kaji ciwo rannan, how is it?" Dariya yayi sosai, da alama yama manta da cewa yaji ciwon, yace "ta warke ai, tun tuni. Abinda ya kamata ki tambayeni shine how is my heart" ya Walid ya harare shi, ni kuma nayi murmushi ina sunkuyar da kai na kasa. Har muka sauka a Nigeria bamu samu munyi wata magana da Sultan ba, muna sauka muka tarar da motoci suna jiran mu, muka shiga sai gida. Tunda da na fito daga mota nake jin idanuwan sultan a kaina amma baki kallon inda yake da sauri na shige cikin gida. Ina shiga palo na tarar da yaran gida kowa sai murnar dawowa ta suke, nan na sha runguma har sai da jikina ya fara ciwo, da wayo na gudu na hau sama na shiga dakina, a gyare na tarar da dakin sai kamshi yake yi, na fada kan gado tare da lumshe idona, home sweet home, da sauri kuma na mike naje na bude window ina leken waje ko zan ganshi amma naga bayanan, to ko ya tafi gidan su? Toilet na shiga na kunna ruwa a tub na hada kumfa sosai, when was the last time I had a real bath? Na cire kayana na shiga ina sauke ajjiyar zuciya. Na lissafo irin wahalar da nasha, kuma duk akan Sultan amma yanzu wai gani gashi na kasa yi masa kwakwkwarar magana. Sai kuma na fara yiwa kaina tambayoyin me ya faru da bana nan? Ya akayi har su daddy suka karbi sultan har ya saba dasu sosai? Jin ana kiran sallar isha yasa na tuna ko magrib banyi ba, na dauraye jikina na fito, na bude kayana naga sunanan yadda na tafi na barsu sai dai daga alama an dan karkade su an sake gyaramin, na saka wasu riga da skirt ga mamaki na sai naga wuyan rigar yayi min yawa skirt din kuma yana zamewa, chafdi, gaskiya na rame da yawa, dole na saka doguwar riga nayi rolling mayafi na fita. Ina saukowa daga sama na tsaya da mamaki, Sultan again, dare dare a kan kujera a palo suna ta zabga musu da ya Habeeb, a tare suka juyo suka kalle ni, dif sultan ya dauke wuta ya daina magana, ya Habeeb kuma ya taso da sauri gurina yana cewa "welcome home, my parrot" nayi murmushi na karasa gurinsa, sai kuma ya rike hannuna yana kallon fuskata, dariya yayi yace "kinga yadda kika yi baki kuwa?" Na juya idona nace "tubarkallah, wannan yace da rame wannan yace nayi baki in ba so kuke ku chinye ni ba ai ya kamata ku kyaleni haka" daddy ne ya shigo Walid yana biye dashi a baya, duk muka gaishe da daddy ya hau sama, har lokacin sultan bai ce min komai ba sai kallo kamar zai chinye ni, dole na tashi na tafi kitchen na zauna ina kallon ana ta fita da kayan abinci, sai da naji daddy ya kuma saukowa sannan na kuma palon, still Sultan yana nan, muka tafi dining har dashi, sai kawai naga ya tashi yana serving din mu, what is happening ne ni maimunatu? Someone should start explaining. Har ya zuba min abincin kuma sai ya dauke ya sake karo min ba tare da ya kalleni ba yace "ki chinye wannan a karo miki wani" ji nayi duk suna dariya ni bansan dariyar me suke yi ba, daddy yace "yes, kina bukatar alot of food da kuma bacci ko kya yi kyan gani" a raina nace Daddy kaima harda kai ko? Allah ne kadai yasan shi kuma Sultan me zai ce min. Na dan fara cin abincin kamar bana so kuma sai naji taste din abincin ba zan iya resisting ba, nayi missing home da duk wani abu na home din, ya Habeeb yace "to 'yar agadaz, bamu labarin agadaz" na yi murmushi nace "sai dai in baka labarin anty Zaliha da samarin 'ya'yanta, dan su kadai na gani tunda naje agadaz din, ko kofar gate ban taba zuwa ba" nan aka koma hirar Niger da zafin garin, suna cewa zafin ne ya sakani baki. Tunda muke hirar Sultan baice mana komai ba abincinsa kawai yake ci, har ya gama yasha lemo ya mike tsaye, ina kallonsa muka hada ido nayi sauri na dauke kaina. Yace da Daddy "Daddy sai da safe" Daddy yace "Allah ya bamu alkhairi" ya dan jima a tsaye kuma sai ya tafi, naji bude kofar palo amma banji rufewa ba. Yaya habeeb ne ya fara taba ni yana nuna min hanyar waje, nayi kamar ban ganshi ba, ina jin yaya Walid yana yin dariya kasa kasa, sai kuma ya dan daga murya yace "na'am? Tana zuwa" sai ya ce a hankali "kamar naji sultan yana kiranki ko?" Shima yi nayi kamar bansan me yake yi ba amma fa ta ciki na ciki, a hankali Daddy yace "tashi kije" nace "yes Daddy" na mike a hankali kamar bana so nayi hanyar waje, amma fa a xuciya ta ji nake kamar in kwasa a guje. Ina zuwa kofar falon na ganta a bude, na fita na mayar da ita na rufe. Kafin inyi taku daya naji ni a jikin sa, duk da banga fuskarsaba amma nasan shine, na danyi kokarin raba jiki na da nashi amma ya rike ni tsam, nima kuma I need the hug, dan haka na kwantar da kaina, a tare muka sauke ajjiyar zuciya, ina jin bugawar zuciyar sa kamar a kirjina take bugawa, mun jima a haka sannan ya kawo bakinsa dai dai kunne na yace "I missed you" na kara narkewa a jikinsa dan ni inajin ba zan iya cewa ma i missed you din ba. Sai da hankali na ya fara dawowa jikina na tuna anytime wani, ko kuma ma Daddy da kansa zai iya bude kofar palon ya fito. Na dan zame daga jikinsa amma ina jin kamar na bar wani part of me a tare da shi. Yana kallona yace "come, let me show you something" yayi gaba na bishi a baya da sauri, naga yayi hanyar part din su ya Habeeb, ni dai binsa nake, ya bude kofar yayi min alama da in shiga, ina shiga naga gurin gaba daya ya chanza min, wani kamshi mai dadi yana tashi, kamshin Sultan, irin kamshin da kullum motarsa take yi kuma irin kamshin da naji a apartment dinsa na newyork, ya tsaya a bayana yace "welcome to my humble home" na juyo ina kallonsa da mamaki, ya jawo ni ya zaunar dani akan kujera shi kuma ya zauna a gaba na ya harde kafafuwansa yace 'I have a story to tell you" nan fa ya fara bani labarin abubuwan da sula faru tun tafiya ta, duk irin abubuwan da Daddy yayi masa, dawowarsa gidan mu hatta zancen sabon kamfaninsa daya bude sai da ya gayamin, nayi mamakin yadda al'amarin ya kasance sannan na jinjinawa Daddy na, na kuma gode wa Allah da samun uba na gari da nayi, dan iyaye na gari sune ginshikin rayuwar 'ya'ya, sannan kuma na kara imani da kuma godiya ga Allah, dan nasan duk abinda ya faru ya faru ne saboda karfin addu'ah. Ni kam babu abinda zance sai Alhamdulillah. Nan ni kuma na zauna na fara bashi labarin nima abinda ya faru dani tun sanda ya Walid ya dauko ni daga gurinsa, tafiyar mu niger da duk abinda ya faru acan har taimakon da musbahu yayi min na samu na kira daddy na. Nace "yanzu Mommy ce kadai matsala, ita ma kuma insha Allah zata sauko" na sauko daga kan kujerar nima nayi irin zaman da yayi na cigaba da bashi shawarwari akan sabon companyn sa, na bashi shawarar ya bude branch a New York tunda yana da mutane sosai acan, naga alamar yaji dadin shawarar, nan yace in zabarwa companyn suna wai dama ni yake ta jira in dawo in fadi sunan da nake so, nace zan zaba amma ba yanzu ba sai nayi tunani. Nan kuma na sake bashi shawarar yake zuwa palace yana gaishe da babanshi, ya dan bata fuska yace "why?" Nace "because he is your father" Ya Habeeb ne ya shigo palon, ya tsaya yana kallon mu da mamaki yace "wai ke har yanzu kina nan? Mu duk mun dauka kinyi bacci by now?" Na kalli wall clock din palon 12:49, da sauri na mike ina rufe bakina da hannu, na shiga uku, duk dariya suke min, Allah yasa Mommy bata shiga dakina ba, dan tunda muka dawo gidan ban kuma ganinta ba, kar in kara wani laifin akan wani. Ya Habeeb yace "soyayya dadi, wayo ku baku ma san lokacin ya tafi ba ko?" Da sauri nayi hanyar waje ina jin Sultan ya biyo bayana yana kirana, a bakin kofa na tsaya ya karaso ya miko min wani abu a leda, na kalle shi da alamar tambaya yace "it is a phone, ba zan iya hakura da jin muryar ki ba, dazu na siyo na yi miki charge dinta na saka miki sabon sim" na dan yi shiru amma kuma nima ina son muke wayar ai. Na karba nace "thank you" bai ce komai ba, na juya na cigaba da tafiya ya sake biyoni ya sha gabana yana tafiya da baya da baya yana kallona kamar wacce zan gudu, har muka je kofar palon mu, na kama handle din kofar yace a hankali "love" na juyo na kalleshi, a hankali ya sake cewa "thank you for loving me" bance komai ba sai murmushi da nayi, shima murmushin yayi min, and in that moment ji nayi duk hawalar da nasha is nothing, for him, I can do it all over again, ko da wacce tafi ta baya ce ma.
Chapter 87 · 0% Book details