← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 190

Sashe 59

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Gaba daya jikina karkarwa yake yi saboda irin kukan da na keyi, ba me sound sosai bane sosai amma irin wanda karfinsa yake jijjiga jikin mutun din nan ne. What just happened to us? Ji nayi na tsani kaina gaba daya saboda ina ganin duk abinda ya faru laifina ne. I shouldn't have let Sultan come to America with me tunda nasan ni kadai ce ba kowa a tare dani. Daya biyoni din ma I should have stand my ground in nuna masa limit dinsa. Amma na barshi kusan komai tare muke yi, shi ba muharramina ba sannan ga strong attraction da yake a tsakanin mu. Na tuna lokacin da ya fara cewa yana sona, cemin yayi he has nothing yana so inyi sharing what I have with him. Nothing din da yace bayana nufin kudi ba, yana nufin many things da yayi lacking including tarbiyya, amma maimakon inyi sharing tarbiyyata with him sai na biye masa muka zama marassa tarbiyyar gaba daya. Na tuno maganar Amira da take cemin ita character is contagious, idan ni ban gyara shiba shi zai iya lalata ni, gashi kuwa ta tabbata, ni nasan abubuwan da na aikata zuwana America ko a mafarki akace min zan aikata something like that zance karya ne. Ni nasan wannan abinda ya faru dani har da alhakin iyaye na a ciki. Sunyi iyakacin kokarinsu gurin bani tarbiyya amma nake cin amanar su ina bin Sultan, na tuno abinda na ke yi a abuja da England, sai inyi wa mommy karyar zanje unguwa mu fito da driver sai inyi ditching drivern in bi sultan, instead of in yace min inzo muje yawo in ce masa a'a in yana son gani na yazo ya same ni a gidan mu. Na tuna irin kallon da colleagues dina suke min tinda muka zo America suka ganni tare da Sultan, a lokacin sam ban damu ba, gani nake what people think about me doesn't matter, tunda kullum abinda sultan yake ce min kenan, na manta cewa ita shedar mutane itace shaidar da take bin mutun har kabarinsa. Nan tunanin mutuwa yazo min. Yanzu da zan mutu na tabbatar wuta zanje, annabi saw cewa yayi damu 'kada ku kusanci zina' amma ni exactly opposite abinda yace min nayi. Nan take wani irin tsoron Allah ya fara shigata, kukana ya tsananta, cikin kukan na fara kiran astagfirullah, astagfirullah har sai da murya ta da dashe ni kaina bana jin me nake cewa. Wani sanyi naji yana ratsani sannan na tuna har yanzu babu kaya a jikina, bedsheet din kan gadon na jawo na kudinduna ina karkarwa, a hankali naji na daina jin sanyin, kukan ma ya tsaya sai ajjiyar zuciya. Na sa hannuna na shafa fuskata ina goge hawayena, anan na taba lips dina da suka kumbura, tun da na mallaki hankali na babu wani namijin daya taba koda rike hannuna ne, but Sultan has kissed me today kuma wannan ba shine abinda nafi regretting ba kamar the fact that I kissed him back. I should have control myself but I didn't, I am too weak, too soft.

Na kalli hannuna naga zoben da Sultan ya bani last week. Sai a lokacin na tuna dashi a toilet, duk da abinda ya faru sai naji ina wondering is he OK? Ba motsi sam a toilet din, what if I hit him too hard? Na mike a hankali na dauki kayana dana ajiye na fara sakawa, sai a lokacin na tuna cewa na saba kumfa a jikina ban dauraye ba, na kalli jikina naga babu kumfa babu alamarta. Na saka kayana ba tare da ko mai na shafa a jikina ba, turare ma sai dai yayi hakuri yau kam. A madubi na kalli fuskata naga tayi fari tas tamkar babu jini. Idona ya kumbura sosai saboda kukan da nayi, na dauko glass a cikin handbag dina na saka, na tuna Sultan ne ya saya mana rannan iri daya ni dashi. A kwatina kawai naja nayi gaba, har nakai bakin kofa sai na tsaya ina kallon kofar toilet, har yanzu babu motsi a ciki, na karasa gurin na zare key din daga jikin kofar na tsugunna a hankali na tura shi ta kasan kofar. Still banji motsi ba. Hankali na naji bai kwanta ba, na leka ta keyhole, a zaune na ganshi ya jingina da bango yana facing kofar, idonsa a lumshe, side din fuskarsa daya da jini alamar karfen yaji masa ciwo, na jima ina kallonsa sannan na lura kirjinsa yana dagawa alamar numfashi, sai a lokacin na lura cewa kayan jikinsa complete suke har da takalmi da agogo, sai dai yanzu gaba daya kayan sun jike da kumfar jikina. Ba abinda ya zo gurina yayi kenan ba, zuwa yayi ya kaini airport, he has been good, more than good, how did this happened. Na sake masa one last look sannan na bude kofar apartment din na fita. Na duba agogo naga 12:30, yaushe time ya wuce har haka? Sai da anje gate din hospital din sannan na samu taxi nace ta kaini airport, ina zuwa na sake sayan wani sabon ticket for the next flight to England. Wanda suka ce min sai 6 na yamma zai tashi, I will wait, dan da in koma apartment dina gwara in kwana anan ina jira. Waiting room dinsu na shiga na zauna, na tuna ko breakfast banyi ba amma na share. Ina zaune har lokacin sallar Zuhr yayi na tashi na shiga toilet nayo alwala na dauko potable sallaya ta mai hade da compass na shimfida can gefe na tayar da sallah, sai da nakai sujjadar karshe inda anan na saba gabatar da adduoi na amma yau na kasa addu'ar komai, am a sinner, ta yaya zan roki Allah bukatuna bayan na saba masa, sai kuka, da kyar na dago daga sujjadar na kammala sallar sannan na dinkule a kan sallayar na cigaba da kuka na. Anan na wuni ko ruwa na kasa sha, ina ganin missed calls din mommy, nasan sunje daukana basu ganni ba, bazan iya magana ba shi yasa ban dauka ba. Karfe 6 jirgin mu ya tashi, na zauna a seat dina temperature ta tana hawa, flight attendant na kira nayi requesting a bani bargo, haka na kudunduna ina ta juya zoben sultan a hannuna. Is he OK? Ko ya fito daga toilet din? Duk da abinda ya faru tsakanin mu amma sam har yanzu banji haushinsa ba, nafi jin haushin kaina. Ina nan a kwance har jirgin mu ya sauka around 11:30 na dare, na kunna waya ta na fita reception na kwanta na kudunduna a cikin hijab dina ina karkarwa. Bana son zuwa gida sam saboda gani nake kamar abinda na aikata yana rubuce a goshina ina zuwa gida zasu gane. Number din Hafsat nayi dialing tana dauka nace "Hafsat ina airport bani da lafiya, dan Allah ku zo ku dauke ni" da sauri ta amsa jin yanayin muryata. Ba'afi 20 minutes ba sai gasu ita da Zayed, Hafsat tana taba jikina tace asibiti, Zayed yace "No, mu kaita gida kawai tasha magani ta kwanta, zuwa gobe in babu sauki sai a kaita asibitin" sai da muka je gidan Hafsat sannan ta kira mommy ta gaya mata gani nan a gidansu babu lafiya, nan da nan mommy ta daga hankalinta tace zuwa zatayi ta ganni da kyar daddy ya hana ta yace ta bari sai da safe, tunda daga Zayed har Hafsat duk likitoci ne yasan zasu kula dani. Magunguna zayed ya bani na sha sannan Hafsat ta dama min oats shima na sha, gana nan suka tafi suka barni suka ce in kwanta inyi bacci. Suna fita na tashi na shiga toilet nayo alwala na gabatar da sallah Magrib da Isha, sannan na zauna na fara jero salloli a duk sujjada ina kuka ina neman gafarar Allah, kawai sai na samu kaina da yiwa sultan adduah. Na tuno da maganar da Steve ya gayamin lokacin da na tambayeshi ko sultan yana shan giya, he said only when he is frustrated, yanzu kuwa nasan sultan is as frustrated as frustration goes. Sai da aka fara kiran sallar asuba Hafsat ta shigo da niyyar tashina sai ta ganni already akan sallaya sai ta koma. Sai da na idar da Sallah asuba sannan na kwanta, ji nayi kamar an dauke min wani nauyi daga kaina. A take bacci yayi awon gaba dani.

Aduk sanda bawa ya aikata laifi, babban abinda ubangiji yake so shine bawa ya tuba, taubatan nasuha, ka tuba da niyyar ba zaka sake aikata laifin irin wannan ba. Shi Allah mai gafara ne kuma mai rahama. In dai har ka tuba ga Allah, kai kanka ba sai an gaya maka cewa tubanka ya karbu ba, ajikin ka zakaji, saboda shi zunubi nauyi ne dashi, zakaji kunchi a zuciyar ka amma da zarar ka tuba zakaji kunchin ya yaye. Allah yasa mu dace.
Chapter 59 · 0% Book details