← Book details Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 190

Sashe 18

Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Wasa wasa har saura one week muyi hutu Ibrahim bai ce min komai ba. Ranar akayi taro akan shirye shiryen saukar alqur'ani da zamu yi, an saka ranar hutu ranar za'ayi bikin sauka. Duk an tura wa iyayen mu IV. Ana cikin taron ina kallon Ibrahim yana ta kallona yana yimin murmushi amma na hade rai naki mayar masa. Hafsat sa ido tana lura dashi tace min "yau da alama tsimin ya tashi" nayi banza na rabu da ita. Ana tashi daga taron ya taho gurin mu yace min " I want to see you, please" nace masa "OK, ai gani ko" ya sunkuyo saitin fuskata yace "alone" daga haka ya juya ya fice daga hall din. A raina nace lallai wannan mutumin, amma bance komai a fili ba saboda su Hafsat 'yan bani na iya 😎..Bayan sa nabi na tarar dashi a staff room a zaune shi kadai saboda duk malaman are busy. Ya nuna min kujera na zauna ina ta shan kanshi ni lallai fishi nake yi. Yace "wai wannan fushin na menene Maimunatu?" Na kara tsuke fuskata ina turo baki, dariya ma abin ya bashi yace "ni dai bansan abinda nayi ba, duk dokokin da aka kafa min ina binsu, to me nayi ne ni Ibrahim?" Na kalle shi da fada nace "sai yaushe kake planning zaka gaya min in ka tafi gida ba dawowa zakayi ba?" Nan take murmushin fuskarsa ya bace. Ya taso ya dawo kusa dani ya zauna yace "maimunatu ina so muyi maganar amma so nake in tsaida tsayayyiyar magana tukun" nace "bangane ba" yace "bana son komawa Ibadan, ina son in nemi aiki anan ko cikin abuja ko school dinnan, inda dai zan ringa ganin ki. To nayi wa principal dinku maganar inda akwai vacancy inaso amma bata bani amsa ba tukun, to ni tunda nazo ba shiga cikin gari nake yi ba sosai sai last two weeks muka fara zuwa da victor muna raba CV din mu. In har na samu job a Abuja zan dawo nan da zama saboda ke, in ban samu ba kuma babu yadda zanyi maimunatu dole in koma Ibadan" naji dadin maganar sa har cikin raina, cewa zai iya dawo wa Abuja da zama saboda ni alhalin family dinsa suna Ibadan. Nace "amma familyn ka fa? Don't you want to go back to them" yace "family na ina zuwa ganin su ai duk weekend. Bature yace home is where the heart is, and u are my heart maimunatu. I want to be with you" na sunkuyar da kaina kasa ina lissafin maganar sa. Tabbas ina son zamansa a abuja saboda bana son yayi nisa dani amma kuma family dinsa fa? Nayi musu adalci? Amma kuma ta wani bangaren samun aikin sa a abuja ai cigaban sane, duk da bansan salaryn sa na Ibadan ba amma nasan nan nan sai yafi na can. Wata idea ce tazo min raina kuma nayi alkawarin zanyi trying. Muna zaune wasu staff suka shigo suna kallon mu, sai kawai naji ban damu ba. It doesn't matter tunda barin school din ma zaiyi. Tun daga ranar kullum muna tare da Ibrahim gani nake kamar in muka rabu bazan sake ganin saba, shi kuma kullum yana assuring dina da cewa koda bai samu aiki a abuja ba to kullum zai ke zama a hanyar zuwa gurina.

Ana saura kwana biyu hutu mun fito daga exams muna zaune akan veranda ni da Ibrahim muna ta hirar mu muna dariya, yanzu ban damu kowa ya ganmu tare ba tunda it's almost over. Sai nake tambayar shi maganar auren sister dinshi Hadiza, yace "Hadiza ta jama kanta ai, yanzu wani cousin din mu za'a aura mata kuma bata so, data hakura da wancan ta fito da wani da shikenan ai" na sunkuyar da kaina nace "do u think it is easy?" Yace "what?" Nace "idan kana son wata kuma parents dinka suka ce no, do u think it will be that easy ka hakura da ita ka samu wata?' Yanzu ya fahimci cewa ba maganar Hadiza nake yi ba, ina magana ne akan abunda zamu iya fuskanta anan gaba. Yayi shiru bai ce min komai ba, har nayi tunanin ba zai amsa ba sai kuma yace "they will not say no. Maganar Hadiza is different, wanda take so ba mutumin kirki bane. They only need to get to know you zasu soki sosai" nayi murmushi a raina ina cewa naka mai sauki ne Ibrahim nawa nake ji, a fili kuma sai nace "idan kuma basu soni ba fa?" Yace "they will" na sake cewa "what if they don't?" Kamar wanda aka mintsina sai ya mike tsaye yace "dan Allah ki bar maganar nan, we will cross that bridge when we come to it " a raina nace Allah ya bamu ikon tsallake wa lafiya.

Dama da akwai plan din da nake shiryawa na abinda zanyi. Na jawo school bag dinsa da ya ajiye a tsakanin mu na bude na fara yi masa bincike, ya dawo ya zauna yana cewa "me kike nema a jakar tawa kuma" nace "wasikar budurwar ka nake nema" yayi dariya yace "ai ba"a nan zaki samu ba, kin ganta a nan" ya fada yana zaro pink and purple handkerchief dina daga aljihunsa. Nasa hannu na rufe fuskata ina dariya nace "kai yanzu ajiye shi kai?" Yace "eh mana, kuma ajjiyarsa zanyi tayi as a reminder" nayi shiru ban bashi amsa ba, yace "seriously, what are u looking for a jaka ta?" Nace "CV dinka nake nema" yace "me zakiyi da CV dina" nace "ajiyewa zanyi nima as a reminder" yayi dariya yana karbe jakarsa daga hannuna. Nace masa "da gaske so nake in ajiye duk sanda na tashi rubuta CV sai in duba taka" ya jima yana kallona da alama bai yarda da bayani na ba sai kuma ya daga kafada ya dauko ya miko min, na karba nace "nace thank you " "you are welcome"

Ranar hutu daga ni har shi kamar marasa lafiya muka zama, tun da sassafe na fito muna tare dashi har akayi assembly aka fara shigo wa daukan students. Yace min "kina da number dana baki" nace "yes" yace "you can call me anytime" nace "to" duk mun rasa kalaman da zamuyi sallama dasu kawai dai muna enjoying company din each other. Ina ta addu'ah a raina Allah yasa kar azo daukan mu da wuri sai na hango motar gidan mu tana shigowa, gaba na ne ya fadi saboda naga motar mommy ce sabuwar benz dinta, bana son Ibrahim ya ga motar tunda har yanzu bai san gidan mu muna da kudi sosai ba. Nace "ga daddyn mu chan yazo, would you like to meet him?" Nan da nan naga fuskarsa ta chanza alamar tsoro, yace "no, not now" dama nasan haka zaice shi yasa na gayyace shi din. Yace "look at me " na daga kai ina kallon cikin idonsa da yayi kalar tausayi, yace "please in kinje gida call me, da akwai abubuwa da nake so in gaya miki" nace masa to amma still ya kasa tafiya nima kuma na kasa tafiya, sai ga Hafsat nan tazo tana kirana, dole na dauke ido na daga cikin nasa na dau hanyar gate ina hadiye kuka na. Ina jiyo shi yana bawa Hafsat amana ta, ga mamakina sai naji ta biye masa har da dariya.

Episode Twenty: The New Job
Chapter 18 · 0% Book details