Sashe 27
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daddy ya fara magana da cewa "maganar da nake son inyi muku akan Hafsatu ne da Maimunatu. Tunda Allah yasa kun gama secondary school, ina son in san plan din ku for the future. Aure kuke so kuyi ko kuma karatu kuke son yi?" Muka juya muka kalli juna ni da Hafsat, saboda bamu taba tsammanin wannan tambayar daga gare shi ba, mun riga mun yi zeroing mind din mu cewa karatu zaice muyi, la'akari da irin zurfin ilminsa sannan yayun mu suna gama sec sch suke wucewa university. Mommy ma ta saki baki tana kallonsa tace "aure? Aure fa kace Dear?" Ya kalleta da murmushi yace "yes, aure" ta nuna mu da hannu tace yanzu wadannan 'yan babies din za'ayiwa aure?" Dariya sosai daddy yayi yace "kwarai da gaske. Babu wacce zan matsawa a cikin su ince tayi aure, amma duk wacce tace min aure ta ke so to babu shakka auren zanyi mata. It's very wrong abinda mutanen mu suke yi yanzu na cewa ba zasuyi wa 'ya'yansu aure ta sai sunyi karatu mai zurfi. Hakan bashi da ma'ana. Indai har yarinya ta isa aure, ta samu miji, kuma tace tana son auren to abu mafi a'ala shine ayi mata auren. In ba haka ba ka shiga hakkin 'yarka kuma in Allah bai kare taba to zaka jefa ta a halaka" mommy ta tabe baki tace "ni dai 'ya'yana basu isa aure ba" daddy yace "cikin su wacece bata period" duk palon kowa yayi shiru, ya cigaba da cewa "shekara nawa nana Aisha ta tare a gidan annabi SAW? Duk abinda annabi yayi a rayuwarsa yayi ne saboda yana so mu kwaikwayeshi, su Westerners din da muke kwaikwayo basa yiwa 'ya'yansu aure da wuri amma ai basa hana 'ya'yansu tare wa a gidan samari ko? Mu tunda addinin mu ya hana hakan mai yasa ba za muyiwa yaranmu aure in sun isa ba?" Mommy ta sauke ajiyar zuciya ta karya murya tace "amma dear karatun fa?" Daddy yace "aure ai baya hana karatu, su kansu mazan yanzu ai sun waye basa hana matan su karatu. Yanzu misali, Prof Rukayyatu Ahmad Rufa'i tana sec sch akayi mata aure amma sai da takai har matsayin professor. Dan haka indai har mazajen su sun amince to za suyi karatu har sai inda suka gaji" yayi shiru for some time. Kamar daga sama yace "Moon ina saurayin nan naki yaroba?" Da sauri na dago kai na na kalle shi sannan na kalli mommy wacce itama shi take kallo da sakakken baki. Ya cigaba da cewa "yes, I know. Tun sanda kika sa na nemar masa aiki nasan there is something between you two. Na yi miki gargadi akansa ne saboda malamin ki ne a boarding school, babu idon mu a kanku, amma nasan in har da gaske yake son ki zai biyo ki gida, kuma naga ya biyo ki din. I thought zai zo ya ganni ranar sai kuma naga bai zo ba, sai na saka a raina cewar he is not ready" mommy ta fara girgiza kanta tana maimaita "no, no, no, not my daughter, not Moon" daddy ya cigaba da cewa "I know your mother will throw her tantrum, but I can handle her" mommy tayi sauri tace "inna da baffa ma ba za su yarda ba, Moon din za'a aura wa bayarabe? Dama munafikin copper dinnan ashe bana Allah bane?" Daddy ya kalleta with serious face yace "menene matsalarki da shi" tayi sauri tace "bayarabe fa kace? Wannan kadai bai isa matsala ba?" Daddy yace "indai har yana sallah, yana da asali, mutumin kirki ne, kuma yana da halin rike mata shikenan. Wannan shine abinda addini ya gindaya mana akan in zamu zaba wa yayan mu mazaje, addini baice mana mu duba kabila ko yare ba" mommy wacce by now ranta ya gama baci tace "I am not looking forward to having yaroba grandchildren, can u even imagine that?" Daddy ya kashingida akan kujerar da yake kwance yace "kinga shikenan sun huta idan ana tribal crisis" Ya Habeeb yayi dariya mommy ta harare shi. Daddy ya kalleni yace seriously"tell him in da gaske yake yazo ya same ni muyi magana dashi, in kuma bada gaske yake ba kar ya sake zuwa gidan nan" ni dai bance komai ba. Ya juya kan Hafsat yace "Hafsat ke kuma fa? Karatu ko aure?" Hafsat ta gyara zama tace "daddy ni dai nafi son karatu" yace "shikenan, Alhamdulillah. Along the line in kina karatun in kinji kina son auren kuma Allah ya kawo mijin shikenan sai kiyi kayanki" Ya Habeeb ya zunguri Hafsat "to dama ba dole kiyi karatu ba, tunda babu mashinshini?" Ta juya ta murguda masa baki, yace "kinga tsiyar ai, rashin kunyar kima ai bazata bar samarin su zo ba" duk akayi dariya banda mommy. Daddy yace "shikenan, kowa ya tafi harkokinsa, next week zamu sake yin magana" da sauri na mike, dama kaman akan kaya nake zaune. Na hau saman mu, ina shiga daki naji tafiyar Hafsat a baya na. Ta shigo ta rufe kofa. Lokacin ina cire kaya na tace "now what?" Nace "now, my dear sister, I am going to look for him" da haka na shiga wanka. Ina wanka ina tunanin abubuwan da suka faru. Look what Ibrahim almost cost us. The Idiot. Na fada a fili. He don't know daddy amma after one look at him yayi deciding ba zai saurare shi ba. The Fool. Har da wani tafiya wai sai yayi kudi zai dawo, ko ina ruwan daddy da kudinsa? The Idiot. Na fito daga wanka na zura doguwar riga nayi rolling vail. Hafsat naga ta yafa mayafi. Nan muka fita tare. A falon mommy muka same ta a zaune ita kadai har yanzu ranta a bace yake. Ta bimu da kallo. Hafsat tace "mommy zamu danje unguwa mu dawo" wani mugun kallo mommy tayi mata tace "wato dan ance za'ayi muku aure shine zaku fara yawo kuma? Ko neman mazajen zakuje yi?" Hafsat tace "mommy gidan su Amira fa zamu je" "oh zakuje ku bata labarin za'ayi muku aure ko?" Mu kayi shiru bamu ce komai ba. Ta kalle ni tace "Maimuna ki kiyaye ni wallahi, ki fita daga ido na in rufe, ko da wasa na sake jin maganar wannan bayaraben wallahi sai kin san bani da dadi" na makale daga bayan Hafsat. A raina nace "oh mommy, da kinsan yadda nake jin bayaraben nan a raina da baki ce haka ba" mun jima a tsaye sannan tace "kar ku kai magrib" daga nan ta tashi ta shige bedroom dinta.
Muna fita driver ya dauko motar da ake kaimu unguwa. Wani security ya zo ya shiga seat din gaba, take nace masa ya fita. After what happend ba zanje gurin Ibrahim da security ba. Mu ka shiga baya Hafsat tace da driver ya kaimu former school din mu.
Muna zuwa staff room muka wuce. Muna shiga seat dinsa na kalla. Lokaci daya na sandare a inda nake tsaye. Babu shi babu alamar sa. Babu komai akan desk dinsa. Not even a single paper. Babu kowa a staff room din sai wani malami guda daya. Hafsat ta karasa gurinsa ta gaishe shi, yace "well3, didn't expect to see you soon" Hafsat tace "sir, malam Ibrahim fa?" Ya maida kallonsa kaina yace "you didn't know? He is gone. He quite his job five days ago, babu wanda yasan mai ya faru, yayi rashin lafiya for two days aka kwantar dashi a clinic, yana fitowa ya rubuta resignation, a day after that ya kwashe kayansa kaf ya koma ibadan"
sama sama naji Hafsat tana masa godiya, naji ta zo ta kama hannuna tana ja na, naji ta sakani a mota ta rufe kofar ta zagaya ta shiga daya side din. Driver ya ja muka tafi. He is gone, He is really gone. Ban taba tambayarsa address dinsa ba. Ban taba tambayarsa phone number din wani nasa ba. Abinda na sani kawai shine a ibadan yake, where in ibadan I don't know. Hanyar da Ibadan take ma bansani ba.
Ina jin driver din mu yayi horn mai gadi ya bude masa get muka shiga gida. Muna fitowa sai ga mai gadi nan ya taho da saurin sa yana yi min magana. "Mai sunan Daada" duk muka tsaya. Ya zo gurina yace "mai sunan daada kinga na manta wallahi sai yanzu dana ganki. Kwanaku hudu da suka wuce wani yazo ya bani sako yace in baki, yana ta jaddada min kar in manta kinga kuwa sai da na manta din, kinsan tsufa sai a hankali" a nutse nace masa "ina sakon yake?" Da gudu ya sake komawa dakinsa sai gashi da wata brown envelope a hannunsa. Hafsat ce ta karba ta gode masa. Ta bare seal din ta saka hannu a ciki sai gashi ta fito da CD a hannunt. A jikin CD din an rubuta da marker I LOVE YOU. Tsaf na gane rubutun sa.
Hafsat ta shiga gida ni kuma na koma motar da muka fito, na zauna a seat din gaba na kunna radio na zura CD din hannuna sannan na danna play. A hankali wakar ta fara tashi.. ......
I don't know when am coming back. I will be gone for a little while, but I will keep myself for me and you, I will be back for you.
I don't know what the future will brings, but I will want you to be with me. I will hope and pray make you wait for me, cos I will come back for you, darling
You are my life, you are my prize, and I went to the finish line. You will be always on my mind.
I will be so far away, promise you will wait for me, I will think of you everyday, my love.
I may not come today, but I will be with you again. I will pray for you everyday, My Love..........
I will think of you tonight, cos I no dey by your side, just for a little while, but know that am alright, and I will see you soon, make you wait for me my dear
Na runtse idona, sannan for the first time tun tafiyarsa, hawaye suka gangaro kan kuncina
Episode Twenty five: The Eclipse
Muna fita driver ya dauko motar da ake kaimu unguwa. Wani security ya zo ya shiga seat din gaba, take nace masa ya fita. After what happend ba zanje gurin Ibrahim da security ba. Mu ka shiga baya Hafsat tace da driver ya kaimu former school din mu.
Muna zuwa staff room muka wuce. Muna shiga seat dinsa na kalla. Lokaci daya na sandare a inda nake tsaye. Babu shi babu alamar sa. Babu komai akan desk dinsa. Not even a single paper. Babu kowa a staff room din sai wani malami guda daya. Hafsat ta karasa gurinsa ta gaishe shi, yace "well3, didn't expect to see you soon" Hafsat tace "sir, malam Ibrahim fa?" Ya maida kallonsa kaina yace "you didn't know? He is gone. He quite his job five days ago, babu wanda yasan mai ya faru, yayi rashin lafiya for two days aka kwantar dashi a clinic, yana fitowa ya rubuta resignation, a day after that ya kwashe kayansa kaf ya koma ibadan"
sama sama naji Hafsat tana masa godiya, naji ta zo ta kama hannuna tana ja na, naji ta sakani a mota ta rufe kofar ta zagaya ta shiga daya side din. Driver ya ja muka tafi. He is gone, He is really gone. Ban taba tambayarsa address dinsa ba. Ban taba tambayarsa phone number din wani nasa ba. Abinda na sani kawai shine a ibadan yake, where in ibadan I don't know. Hanyar da Ibadan take ma bansani ba.
Ina jin driver din mu yayi horn mai gadi ya bude masa get muka shiga gida. Muna fitowa sai ga mai gadi nan ya taho da saurin sa yana yi min magana. "Mai sunan Daada" duk muka tsaya. Ya zo gurina yace "mai sunan daada kinga na manta wallahi sai yanzu dana ganki. Kwanaku hudu da suka wuce wani yazo ya bani sako yace in baki, yana ta jaddada min kar in manta kinga kuwa sai da na manta din, kinsan tsufa sai a hankali" a nutse nace masa "ina sakon yake?" Da gudu ya sake komawa dakinsa sai gashi da wata brown envelope a hannunsa. Hafsat ce ta karba ta gode masa. Ta bare seal din ta saka hannu a ciki sai gashi ta fito da CD a hannunt. A jikin CD din an rubuta da marker I LOVE YOU. Tsaf na gane rubutun sa.
Hafsat ta shiga gida ni kuma na koma motar da muka fito, na zauna a seat din gaba na kunna radio na zura CD din hannuna sannan na danna play. A hankali wakar ta fara tashi.. ......
I don't know when am coming back. I will be gone for a little while, but I will keep myself for me and you, I will be back for you.
I don't know what the future will brings, but I will want you to be with me. I will hope and pray make you wait for me, cos I will come back for you, darling
You are my life, you are my prize, and I went to the finish line. You will be always on my mind.
I will be so far away, promise you will wait for me, I will think of you everyday, my love.
I may not come today, but I will be with you again. I will pray for you everyday, My Love..........
I will think of you tonight, cos I no dey by your side, just for a little while, but know that am alright, and I will see you soon, make you wait for me my dear
Na runtse idona, sannan for the first time tun tafiyarsa, hawaye suka gangaro kan kuncina
Episode Twenty five: The Eclipse