Sashe 20
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari da sassafe na tashi, na shiga kitchen naga cook din mu tana ta kokarin hada breakfast. Pancakes na yi irin yadda naga mommy tana yiwa dadday, na hada masa coffee shima irin yadda yake so. Na hada da cup da komai akan tray na hau saman daddy. A balcony dinsa nagan shi kamar yadda nayi tsammani. Yana zaune yana karatun news paper. Na durkusa na gaishe shi sannan na koma falonsa na dauko stool na dawo na dora masa tray din da na kawo akai. Na zauna a kasa a gefen sa. Sai da ya fara shan coffee dinsa sannan yace "ya akayi ne maimunatu?" Na sunkuyar da kaina na kasa magana. Ya ajiye cup din hannunsa ya bani dukkan attention dinsa yace "You know I can do anything for you, in dai bai sabawa addini ba, just say it and it will be done" a hankali na fara magana "daddy ba akai na bane" "OK, akan waye?" "Dama wani copper ne a makarantarmu" sai kuma nayi shiru "ina jinki" "dama wani copper ne a makarantar mu, to sun gama service dinsu wannan watan, to daddy mun saba dashi sosai kuma yana taimaka mana sosai, gashi soon zamu fara SSCE" na sake yin shiru kirjina yana bugawa, saboda is simple amma baya tolerating nonsense, bai ce komai ba amma ni yake kallo, naci gaba "daddy so nake yi ko zaka saka baki a bashi aiki a school din mu" yayi shiru yana cigaba da shan coffee dinsa, na daga kaina naga idonsa yana kaina, da alama studying dina yake yi. Can ya nisa yace "maimunatu shi copper din shi yace miki yana son aiki a school din ku?" Nayi sauri nace "eh daddy shi yace yana so" "kuma yace ki nema masa?" Na girgiza kaina, " yace dai yayi wa pc din mu magana in da akwai vacancy yana so" "then that's all, in suna da vacancy, in he is as good as you said he is, za su bashi ba sai nayi magana ba" nayi shiru kuma naki tashi daga durkushen da nake, daddy yace "menene qualifications dinsa?" Nayi sauri na zaro CV din Ibrahim dana boye a jikin rigata, daddy ya karba da mamaki a fuskarsa yace " How did you get his CV?" Nan fa ido na ya raina fa ta, idonsa har yanzu a kaina yake kuma ni kaina nasan nayi alamar rashin gaskiya. Ya sake tambaya "Maimunatu how did you get his CV?" Nace " He just mentioned it in class cewa yana neman aiki a school din mu, to rannan na ari book dinsa sai naga CV din a ciki shine nayi tunanin in kawo maka ko zaka taimaka masa" na fada bakina yana rawa, a nutse daddy yace min "you are lying" wani daci naji a cikin bakina, nan danan zuciyata ta fara bugawa a cikin makogwaro na. "What tribe is he?" A sanyaye nace "he is a Muslim dad" yace "OK, naji musulmine, what tribe is he" can kasan makoshina nace "yaroba" kalmar yaroban kamar wani garwashi naji ta a bakina. Daddy ya ninke takardar dana bashi ya ajiye sannan yace "Hafsat ta tashi?" Nace "a'a" yace " tashi ki tafi, in Hafsat ta tashk ki turo min ita" jiki a sanyaye na tashi na koma saman mu. Ina shiga toilet na shiga na rufe kaina, nan da nan hawayen da nake rikewa suka fara zuba. I was a fool to think I can fool daddy. Shikenan tawa ta kare, yanzu da Hafsat taje zai tambayeta ita kuma zata gaya masa gaskiya, shikenan mommy tana zuwa zai gaya mata ita kuma zata sakani a turmi da daka. Hafsat ce tayi knocking kofar tana jira na, na wanke fuskata na fito ina sussunne fuska. Tana kallona tace "kuka kuma da sassafen nan?" Nayi banza na rabu da ita. Sai da ta fito tana saka kaya na gaya mata kiran daddy, ta zura hijab dinta zata fita na sha gabanta nan da nan wani kukan ya taho min tace "lafiyar ki kuwa Moon?" Cikin kuka nace "Hafsat please, akan maganar Ibrahim daddy zai tambaye ki, dan Allah kar kice komai" tana kallona da mamaki tace "saboda me?" Tambayar ta ta bani mamaki nima, ban gane saboda me ba? Ita ai tasan saboda menene. Tacigaba da cewa "bakya ganin cewa it will be easier for you both in aka gayawa daddy in za'ayi yace eh in kuma baza'ayi ba yace a'a? The longer kuka jira the more painful it will be in aka hana ku aure, ni bazan ce da daddy komai ba, it is not my call, amma shawara ce nake baki" daga haka ta juya tayi tafiyar ta. Sam Hafsat bata gaya min yadda suka yi da daddy ba kuma shima bai ce min komai ba. Washegari muna breakfast daddy yace min "Moon na duba takardun copper din ku, naga yana da first class a maths kuma yana da experience a teaching, zan kira PC dinku in suna da vacancy zanyi endorsing dinsa" daga haka bai kuma cewa komai ba, Hafsat ta mintsine ni a bom bom nayi kara muka saka dariya muna godewa daddy. Mommy ta tsaya tana kallon mu tace "maganar me kuke yi ne?" Hafsat ce tayi mata bayani, mommy tace "ok, wanda kuke extra lessons dashi?" Nace mata "eh" tace "OK, Allah ya sanya alkhairi, adaiyi hankali, the youth of nowadays are not to be trusted" daddy ya kalleta yace "extra lessons kuma?" Nan mommy ta bashi labarin yadda suka yi da pc din mu. Daddy ya kallemu da serious face yace "I want the extra lessons to stop, in zai maku lesson yayi fixing kuyi a class da sauran dalibai, bana son any special treatment a tsakanin ku, da banyi niyyar ne ma masa aikin ba sai da Hafsat tace min shi ya roke ku a class akan duk wacce tasan baban ta zai iya samar masa aiki ta kai masa takardunsa" nayi sauri na kalli Hafsat ita kuma ta daga kafada. Har cikin raina banji dadin abinda Hafsat ta gayawa daddy ba, Ibrahim is a very proud person amma ta ce wai shi ya roke mu mu samar masa aiki. Daddy ya cigaba da cewa "zan taimaka masa ne saboda bana son in discouraging dinku akan taimako, amma no strings will be attached, shi yasa zance da pc din kar ta gaya masa baban ku ne, saboda bana son wani special something. Allah yayi muku albarka baki daya" muka ce amin.
Kamar yadda al'adar makarantar mu take, duk second day na first term ake yin speech and prize giving. Wannan session din ma haka. Muna shiga hall na tuna cewa shekara guda kenan da haduwa ta da Ibrahim. Muka gaida su mommy muka zauna. Yana shigowa idona ya sauka akan sa, ya saka complete yaroba attire har wannan hular tasu. Ina binsa da kallo har ya zauna a side din baki. Muna ta karbar gift duk gift din da za'a bani sai na kalleshi shi kuma sai yayi min 👍 har aka tashi. Ban je gurinsa ba na wuce gurin su mommy muka basu gifts din mu suka tafi gida. Ina komawa hall din naga students sun zagaye shi ana ta tambayarsa me ya dawo dashi. Na tsaya daga gefe kawai ina kallonsa. Yana gani na ta taso ya kara so inda nake bakinsa har kunne. Sai kuma muka rasa abin cewa "you didn't call me" yace yana dan bata fuska, na rufe tawa fuskar nace "sorry". Muka sake yin shiru nace "ashe baka manta yau speech and prize giving ba" yace "I wouldn't miss it for the world, ko da kuwa da rarrafe zan taho" nayi dariya nace "thank You". Can ya sake cewa "I also wanted to tell you, principal din ku tace next week inzo interview, wai wani ambassador ne ya nema min aikin, bansan ko waye ba" na kirkiro mamakin karya nace "congratulations, amma naji dadi sosai" shima yace min "thank You " sannan yace "by the way, Happy Anniversary to Us" na saka hijab dina na rufe fuskata na tafi na bar shi a gurin.
Episode Twenty one: Amira
Ibrahim ya kawo mana kaya babu lefi, kayan tea, biscuits, cosmetics da drinks. It must have cost him dukkan albashinsa. Yazo yayi interview din, kuma bayan wata daya aka aika masa da offer dinsa har ibadan. A week after that, ya tattaro ta dawo abuja. An bashi gida a staff quarters. Nan take ya fara siyayyar kayan gida, kusan komai ya saya sai ya gayamin ni kuma sai in gaya masa menene next abinda ya kamata ya saya. I wanted to help him with money amma nasan ba zai karba ba, kuma bama nason yasan financial status din family na. Farko sai aka bashi ss2 shi kuma ya dage lallai baya so shi ss3 yake so, a cewar sa ya saba damu tunda mu ya dauka sanda yana service. Sai da kyar suka bashi SS3 din, ranar bakinsa har kunne yana murna yazo yake gaya mana, sannan kuma an bashi sports master. Yanzu kam da yawa daga 'yan ajin mu sun san alaka ta da Ibrahim tunda sam yanzu baya boye abinda yake ranshi, ni ce dai nake dan ja da baya.A haka har muka yi hutun first term. A cikin hutun abubuwa da yawa sun faru, na farko Allah yayi wa baban Amira rasuwa.
Kamar yadda al'adar makarantar mu take, duk second day na first term ake yin speech and prize giving. Wannan session din ma haka. Muna shiga hall na tuna cewa shekara guda kenan da haduwa ta da Ibrahim. Muka gaida su mommy muka zauna. Yana shigowa idona ya sauka akan sa, ya saka complete yaroba attire har wannan hular tasu. Ina binsa da kallo har ya zauna a side din baki. Muna ta karbar gift duk gift din da za'a bani sai na kalleshi shi kuma sai yayi min 👍 har aka tashi. Ban je gurinsa ba na wuce gurin su mommy muka basu gifts din mu suka tafi gida. Ina komawa hall din naga students sun zagaye shi ana ta tambayarsa me ya dawo dashi. Na tsaya daga gefe kawai ina kallonsa. Yana gani na ta taso ya kara so inda nake bakinsa har kunne. Sai kuma muka rasa abin cewa "you didn't call me" yace yana dan bata fuska, na rufe tawa fuskar nace "sorry". Muka sake yin shiru nace "ashe baka manta yau speech and prize giving ba" yace "I wouldn't miss it for the world, ko da kuwa da rarrafe zan taho" nayi dariya nace "thank You". Can ya sake cewa "I also wanted to tell you, principal din ku tace next week inzo interview, wai wani ambassador ne ya nema min aikin, bansan ko waye ba" na kirkiro mamakin karya nace "congratulations, amma naji dadi sosai" shima yace min "thank You " sannan yace "by the way, Happy Anniversary to Us" na saka hijab dina na rufe fuskata na tafi na bar shi a gurin.
Episode Twenty one: Amira
Ibrahim ya kawo mana kaya babu lefi, kayan tea, biscuits, cosmetics da drinks. It must have cost him dukkan albashinsa. Yazo yayi interview din, kuma bayan wata daya aka aika masa da offer dinsa har ibadan. A week after that, ya tattaro ta dawo abuja. An bashi gida a staff quarters. Nan take ya fara siyayyar kayan gida, kusan komai ya saya sai ya gayamin ni kuma sai in gaya masa menene next abinda ya kamata ya saya. I wanted to help him with money amma nasan ba zai karba ba, kuma bama nason yasan financial status din family na. Farko sai aka bashi ss2 shi kuma ya dage lallai baya so shi ss3 yake so, a cewar sa ya saba damu tunda mu ya dauka sanda yana service. Sai da kyar suka bashi SS3 din, ranar bakinsa har kunne yana murna yazo yake gaya mana, sannan kuma an bashi sports master. Yanzu kam da yawa daga 'yan ajin mu sun san alaka ta da Ibrahim tunda sam yanzu baya boye abinda yake ranshi, ni ce dai nake dan ja da baya.A haka har muka yi hutun first term. A cikin hutun abubuwa da yawa sun faru, na farko Allah yayi wa baban Amira rasuwa.