Sashe 1
Maimoon Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Compiled By Umar Dalha Funtua
MAIMOON
By
Maman Maama
Bismillahir Rahmanir Rahim
Episode One : The Beginning of the Beginning
Shin ta ina zan fara ne, in fara ta haduwa ta da Ibrahim ne ko kuma ta haduwa ta da Sultan? Ko kuma in fara da baku tarihi na ni kaina?
Sunana Maimuna Muhammad Dikko. An haifeni kuma na tashi garin Abuja, Nigeria. Mahaifina Alhaji Muhammad Dikko bafulatanin garin 'yalleman ne dake jahar Jigawa. Garin 'yalleman garin Fulani ne kyawawan gaske wadanda kuma Allah yayi musu arziki sosai har suka watsu a duk fadin Nigeria, musamman garin Lagos da port hercourt tunda yawancin arzikin su na chanjin kudi ne. Mahaifina bai bi family tradition ba saboda shi ya kasance dan boko ne. Yayi primary school dinsa a nan garin 'yalleman tamkar sauran 'yan uwansa amma saboda hazakarsa sai head master dinsu ya bawa mahaifinsa Alh Lawan Dikko shawarar in dai da hali gwara a tura shi kasar waje Dan ya fi samun karatu mai kyau.
Da yake kakan mu mai hali ne tun a wancan lokacin, sai ya tattara makuden kudade ya dauko yaro ya tafi dashi Lagos, da taimakon 'yan uwansu da suke can aka samar wa Muhammad biza zuwa England inda a can ne aka samar masa admission a makarantar Gifted International College inda ya fara karatunsa na secondary school.Duk bayan shekara ake basu hutun session, Muhammad yakan zo Nigeria ya ga iyayensa da 'yanuwansa ya koma, shi kuma Alh Lawan duk sanda Muhammad zai koma sai ya hada kudade masu yawa ya bashi saboda harkar registration da kuma bukatunsa na yau da kullum. Mahaifiyar Muhammad ma Hajiya Adama ba'a barta a baya ba domin tana iya kacin kokarinta dan har shanun ta na gado take sawa a sayar mata a boye bada sanin mai gidanta ba ta tattara kudi ta bawa Muhammad.
Kwanci tashi har Allah yasa ya gama sec sch dinsa kuma a take ya samu scholarship na karatu a Oxford University inda ya karanci business administration saboda burinsa na ganin ya gama karatu ya dawo gida yana taimakawa mahaifinsa a harkar kasuwancinsa. Daga lokacin ne ya gayawa mahaifansa cewa babu zancen biyan kudin makaranta kuma tunda yanzu he is on scholarship, amma duk da haka Alh Lawan yakan aika masa da kudade dan ya biya bukatunsa. A lokacin da ya gama first degree dinsa ne ya dawo gida da niyyar cika burinsa na karbar garkar business din mahaifinsa amma hakan bai samu ba saboda rigimar data barke a familyn su inda kishiyar mamansa wacce ake kira da Hajja tayi tsalle ta dire tace sam ba zata sabu ba bindiga a ruwa. A cewar ta duk wahalar da aka sha da makudan kudaden da aka kashe akan karatunsa sannan ya dawo kuma yace zai karbi dukiyar gida? Ta kara da cewa" inace cewa a kayi shi mai kwakwalwa ne ba zai yi kasuwanci ba karatu zai yi, sai da aka gama kashe kudi a karatun nasa sannan kuma zai zo yace zai yi kasuwancin to ba'a isa ba wallahi, suma sauran yaran gidan ai 'ya'yane".
Da wannan Muhammad ya tattara ya koma England ya dora karatun masters dinsa, yana gamawa ya wuce pH D. Bayan ya gama ne kuma ya karbi aikin lecturing a makarantar. Shekarunsa biyar yana lecturing a Oxford aka bashi award na professorship. A shekarar ne kuma mahaifansa suka dage akan lallai ya dawo Nigeria yayi settling down kaman sauran 'yan uwansa. Saboda gogewarsa a harkar ilimin kasuwanci da mu'amala da kasashen waje yasa yana dawowa Nigeria government din wancan lokacin ta bashi mukamin ambassador. Kasar da aka fara turashi itace makociyar mu, Niger.
Wannan kenan;
Mahaifiyata Hajiya Fatima wadda ake kira da Bintou, buzuwa ce ta asali, mutuniyar kasar Niger ce. Mahaifinta ya rasu run tana yarinya kuma dama it's kadai Allah ya bawa mahaifanta. Mahaifiyarta wacce sunanta aka saka min (Maimoon) ita ce ke kula da ita da karatunta har ta kammala sec sch dinta. Anan suka fara chuku chukun turo ta Nigeria dan tayi jamia anan amma saboda rashin hanya da rashin abun hannu sai abun ya gagara. A nan ne Allah ya hada su da mahaifina lokacin yana matsayin ambassador na Nigeria a Niger. Farko tausayinta ya fara ji da sha'awar yadda take da son karatu, daga baya kuma sai soyayya ta fara shiga tsakanin su duk ya cewa ya girme mata sosai. Dama kuma a lokacin Inna (haj. Adama) ta takura masa akan maganar aure dan haka bai samu matsala ba akayi aure ya taho da ita Nigeria ya ajiye ta a gidanmu dake Abuja unguwar Aso drive inda har yau anan muke da zama.
Episode Two: Meet my Family
Gidan mu katon gida ne saboda sanda daddy ya gina shi yayi niyyar dauko iyayensa ya dawo dasu Abuja amma Baffa (Alh Lawan) yace sam shi bazai bar 'yalleman ba, wannan ya saka daddy ya tsantsara musu gida a can wanda duk da kudin da 'yan garin suke ji dashi sai da gidan ya zama abin kallo. Sannan ya kawo ma'aikata ya zuba musu tundaga kan masu shara har zuwa kuku. Saboda yace lokaci yayi suma da zasu huta, kuma duk abinda yayi inna sai yayi wa Hajja. Ai kuwa suna hutawar dan babu abinda suke yi illa su ci su koshi su kwanta, kuma duk shekara sai sunje aikin hajji, sannan al'adar daddy ce duk sanda aka turashi wata kasa a matsayin ambassador sai ya debe mu munje munyi wata daya har su Baffa da Inna saboda yana so mu samu wayewa irin ta zamani amma yace ba zamu rayu a can ba saboda tarbiyya.
Mu biyar Allah ya bawa mahaifanmu, uku maza; ya Lawan, ya Habeeb sai Faruk, biyu mata; Hafsat da Ni. Ya Lawan ne babba sai ya Habeeb, sai Hafsat sannan Ni sai dan autan mu Faruk. Da yake mommy kwanika tayi sai ya zama babu tazara sosai a tsakanin mu, dukkan mu a shekaru bakwai ta haifemu sai kuma haihuwar ta tsaya mata, daddy kuma yace mun ishe shi fatan shi Allah yayi mana albarka. Zo gidan mu kaga kyau, saboda mix ne aka samu na Fulani da Buzaye, dan haka in ka ganmu sai ka kasa tantance wanne kabila ne mu, tundaga ma zan mu har matan mu haka muke dan sauda yawa inna takan aiko mana da rubutu tace maganin baki.
Ni maimunatu wadda ake kira da maimoon kamar yadda ake kiran wacce aka saka min sunanta wato maternal grandmother dina, nice ta hudu a gidan mu, nice kuma auta a mata. Fara ce ni tas, fatata mai sheki silkin Fulani da Buzaye, ina da tsaho amma ba sosai ba, fuskata oval shape ce mai dauke da dara-daran idanu kwantattu masu yalwataccen eye lashes, girata kamar an zana ki min ita. Hancina dai-dai misali, lips dina sirara masu kalar pink mai haske, gashin kaina mai cikane kuma mai tsaho, Wanda yazo har kan kafadu na. Ina da dimples a both chicks dina masu lotsawa koda magana nakeyi ballantana kuma ace nayi murmushi.
A gidan mu muna magana da daddy n mu da fulfulde, mommy da buzanci, sannan a tsakanin mu muna magana da English, a school ma English dinne dan haka sai kuma tashi babu Hausa sosai sai dai muji a gurin neighbours ko kuma in munyi 'yan aiki hausawa.
Duk a cikin 'yan'uwana na fisu surutu dan ya Walid parrot yake ce min tun ina yarinya, da yake shi ba mai son magana bane, kullum sai yayi ta korata yana cemin parrot, ni kuwa duk abinda na gani sai na tambaya, in ba'a bani amsa bama in yi ta tambayar har sai an bani amsa sai in sake tambayar wani abun daban. Tun sanda na shiga kindergarten daddy ya fahimci duk cikin 'ya'yansa nafi daukan kwakwalwarsa duk da suma sauran ba baya bane wajen karatu. Tun daga lokacin sai yake biyemin inyi tayi tambayoyi yana amsamin har ya zamanto mun shaku sosai fiye da yadda muka shaku da mommy. Mommy n mu wacce a yanzu lawyer ce takance ko ita zan gada ne in zama lawyer saboda yawan tambayoyi na.
Ina shiga basic school na zama tauraruwa, ga kyau, ga kokari, ga surutu mai shiga rai. Sai ya zama kowa yana ji dani a school din. Bani da fada sam- sam, kuma ina da tsoro, ko juniors dina nayi wa wani abu by mistake sai in basu hakuri saboda ina bala'in lallaba jikina. A basic school na samu nickname din MOON saboda shape din fuskata da bright dimpled smile dina, ga kuma yanayin sunana MAIMOON. Wasa wasa sunana har ya fara bata in ba'a register din makaranta ba. Moon kowa yake kira na dashi.
Kasancewar mommy n mu ita kadai ce a gurin mahaifiyarta (daada) yasa ta dauko ta ta dawo da ita Nigeria cikin gidan mu, akayi mata part dinta a kusa da part din su inna, mu kuma sai ya zamanto bamu da gurin hira sai gurinta tunda Allah bai bata haihuwa da yawa ba sai kuma ya dora mata son mu. Kullum tana cikin kula damu, kunshi da kitso a kan mu ni da Hafsat baya tsufa sai an sake wani, duk da muna da gashi amma kullum kanmu a kitse yake ganin sha'awa.
Episode Three: Loved by All
MAIMOON
By
Maman Maama
Bismillahir Rahmanir Rahim
Episode One : The Beginning of the Beginning
Shin ta ina zan fara ne, in fara ta haduwa ta da Ibrahim ne ko kuma ta haduwa ta da Sultan? Ko kuma in fara da baku tarihi na ni kaina?
Sunana Maimuna Muhammad Dikko. An haifeni kuma na tashi garin Abuja, Nigeria. Mahaifina Alhaji Muhammad Dikko bafulatanin garin 'yalleman ne dake jahar Jigawa. Garin 'yalleman garin Fulani ne kyawawan gaske wadanda kuma Allah yayi musu arziki sosai har suka watsu a duk fadin Nigeria, musamman garin Lagos da port hercourt tunda yawancin arzikin su na chanjin kudi ne. Mahaifina bai bi family tradition ba saboda shi ya kasance dan boko ne. Yayi primary school dinsa a nan garin 'yalleman tamkar sauran 'yan uwansa amma saboda hazakarsa sai head master dinsu ya bawa mahaifinsa Alh Lawan Dikko shawarar in dai da hali gwara a tura shi kasar waje Dan ya fi samun karatu mai kyau.
Da yake kakan mu mai hali ne tun a wancan lokacin, sai ya tattara makuden kudade ya dauko yaro ya tafi dashi Lagos, da taimakon 'yan uwansu da suke can aka samar wa Muhammad biza zuwa England inda a can ne aka samar masa admission a makarantar Gifted International College inda ya fara karatunsa na secondary school.Duk bayan shekara ake basu hutun session, Muhammad yakan zo Nigeria ya ga iyayensa da 'yanuwansa ya koma, shi kuma Alh Lawan duk sanda Muhammad zai koma sai ya hada kudade masu yawa ya bashi saboda harkar registration da kuma bukatunsa na yau da kullum. Mahaifiyar Muhammad ma Hajiya Adama ba'a barta a baya ba domin tana iya kacin kokarinta dan har shanun ta na gado take sawa a sayar mata a boye bada sanin mai gidanta ba ta tattara kudi ta bawa Muhammad.
Kwanci tashi har Allah yasa ya gama sec sch dinsa kuma a take ya samu scholarship na karatu a Oxford University inda ya karanci business administration saboda burinsa na ganin ya gama karatu ya dawo gida yana taimakawa mahaifinsa a harkar kasuwancinsa. Daga lokacin ne ya gayawa mahaifansa cewa babu zancen biyan kudin makaranta kuma tunda yanzu he is on scholarship, amma duk da haka Alh Lawan yakan aika masa da kudade dan ya biya bukatunsa. A lokacin da ya gama first degree dinsa ne ya dawo gida da niyyar cika burinsa na karbar garkar business din mahaifinsa amma hakan bai samu ba saboda rigimar data barke a familyn su inda kishiyar mamansa wacce ake kira da Hajja tayi tsalle ta dire tace sam ba zata sabu ba bindiga a ruwa. A cewar ta duk wahalar da aka sha da makudan kudaden da aka kashe akan karatunsa sannan ya dawo kuma yace zai karbi dukiyar gida? Ta kara da cewa" inace cewa a kayi shi mai kwakwalwa ne ba zai yi kasuwanci ba karatu zai yi, sai da aka gama kashe kudi a karatun nasa sannan kuma zai zo yace zai yi kasuwancin to ba'a isa ba wallahi, suma sauran yaran gidan ai 'ya'yane".
Da wannan Muhammad ya tattara ya koma England ya dora karatun masters dinsa, yana gamawa ya wuce pH D. Bayan ya gama ne kuma ya karbi aikin lecturing a makarantar. Shekarunsa biyar yana lecturing a Oxford aka bashi award na professorship. A shekarar ne kuma mahaifansa suka dage akan lallai ya dawo Nigeria yayi settling down kaman sauran 'yan uwansa. Saboda gogewarsa a harkar ilimin kasuwanci da mu'amala da kasashen waje yasa yana dawowa Nigeria government din wancan lokacin ta bashi mukamin ambassador. Kasar da aka fara turashi itace makociyar mu, Niger.
Wannan kenan;
Mahaifiyata Hajiya Fatima wadda ake kira da Bintou, buzuwa ce ta asali, mutuniyar kasar Niger ce. Mahaifinta ya rasu run tana yarinya kuma dama it's kadai Allah ya bawa mahaifanta. Mahaifiyarta wacce sunanta aka saka min (Maimoon) ita ce ke kula da ita da karatunta har ta kammala sec sch dinta. Anan suka fara chuku chukun turo ta Nigeria dan tayi jamia anan amma saboda rashin hanya da rashin abun hannu sai abun ya gagara. A nan ne Allah ya hada su da mahaifina lokacin yana matsayin ambassador na Nigeria a Niger. Farko tausayinta ya fara ji da sha'awar yadda take da son karatu, daga baya kuma sai soyayya ta fara shiga tsakanin su duk ya cewa ya girme mata sosai. Dama kuma a lokacin Inna (haj. Adama) ta takura masa akan maganar aure dan haka bai samu matsala ba akayi aure ya taho da ita Nigeria ya ajiye ta a gidanmu dake Abuja unguwar Aso drive inda har yau anan muke da zama.
Episode Two: Meet my Family
Gidan mu katon gida ne saboda sanda daddy ya gina shi yayi niyyar dauko iyayensa ya dawo dasu Abuja amma Baffa (Alh Lawan) yace sam shi bazai bar 'yalleman ba, wannan ya saka daddy ya tsantsara musu gida a can wanda duk da kudin da 'yan garin suke ji dashi sai da gidan ya zama abin kallo. Sannan ya kawo ma'aikata ya zuba musu tundaga kan masu shara har zuwa kuku. Saboda yace lokaci yayi suma da zasu huta, kuma duk abinda yayi inna sai yayi wa Hajja. Ai kuwa suna hutawar dan babu abinda suke yi illa su ci su koshi su kwanta, kuma duk shekara sai sunje aikin hajji, sannan al'adar daddy ce duk sanda aka turashi wata kasa a matsayin ambassador sai ya debe mu munje munyi wata daya har su Baffa da Inna saboda yana so mu samu wayewa irin ta zamani amma yace ba zamu rayu a can ba saboda tarbiyya.
Mu biyar Allah ya bawa mahaifanmu, uku maza; ya Lawan, ya Habeeb sai Faruk, biyu mata; Hafsat da Ni. Ya Lawan ne babba sai ya Habeeb, sai Hafsat sannan Ni sai dan autan mu Faruk. Da yake mommy kwanika tayi sai ya zama babu tazara sosai a tsakanin mu, dukkan mu a shekaru bakwai ta haifemu sai kuma haihuwar ta tsaya mata, daddy kuma yace mun ishe shi fatan shi Allah yayi mana albarka. Zo gidan mu kaga kyau, saboda mix ne aka samu na Fulani da Buzaye, dan haka in ka ganmu sai ka kasa tantance wanne kabila ne mu, tundaga ma zan mu har matan mu haka muke dan sauda yawa inna takan aiko mana da rubutu tace maganin baki.
Ni maimunatu wadda ake kira da maimoon kamar yadda ake kiran wacce aka saka min sunanta wato maternal grandmother dina, nice ta hudu a gidan mu, nice kuma auta a mata. Fara ce ni tas, fatata mai sheki silkin Fulani da Buzaye, ina da tsaho amma ba sosai ba, fuskata oval shape ce mai dauke da dara-daran idanu kwantattu masu yalwataccen eye lashes, girata kamar an zana ki min ita. Hancina dai-dai misali, lips dina sirara masu kalar pink mai haske, gashin kaina mai cikane kuma mai tsaho, Wanda yazo har kan kafadu na. Ina da dimples a both chicks dina masu lotsawa koda magana nakeyi ballantana kuma ace nayi murmushi.
A gidan mu muna magana da daddy n mu da fulfulde, mommy da buzanci, sannan a tsakanin mu muna magana da English, a school ma English dinne dan haka sai kuma tashi babu Hausa sosai sai dai muji a gurin neighbours ko kuma in munyi 'yan aiki hausawa.
Duk a cikin 'yan'uwana na fisu surutu dan ya Walid parrot yake ce min tun ina yarinya, da yake shi ba mai son magana bane, kullum sai yayi ta korata yana cemin parrot, ni kuwa duk abinda na gani sai na tambaya, in ba'a bani amsa bama in yi ta tambayar har sai an bani amsa sai in sake tambayar wani abun daban. Tun sanda na shiga kindergarten daddy ya fahimci duk cikin 'ya'yansa nafi daukan kwakwalwarsa duk da suma sauran ba baya bane wajen karatu. Tun daga lokacin sai yake biyemin inyi tayi tambayoyi yana amsamin har ya zamanto mun shaku sosai fiye da yadda muka shaku da mommy. Mommy n mu wacce a yanzu lawyer ce takance ko ita zan gada ne in zama lawyer saboda yawan tambayoyi na.
Ina shiga basic school na zama tauraruwa, ga kyau, ga kokari, ga surutu mai shiga rai. Sai ya zama kowa yana ji dani a school din. Bani da fada sam- sam, kuma ina da tsoro, ko juniors dina nayi wa wani abu by mistake sai in basu hakuri saboda ina bala'in lallaba jikina. A basic school na samu nickname din MOON saboda shape din fuskata da bright dimpled smile dina, ga kuma yanayin sunana MAIMOON. Wasa wasa sunana har ya fara bata in ba'a register din makaranta ba. Moon kowa yake kira na dashi.
Kasancewar mommy n mu ita kadai ce a gurin mahaifiyarta (daada) yasa ta dauko ta ta dawo da ita Nigeria cikin gidan mu, akayi mata part dinta a kusa da part din su inna, mu kuma sai ya zamanto bamu da gurin hira sai gurinta tunda Allah bai bata haihuwa da yawa ba sai kuma ya dora mata son mu. Kullum tana cikin kula damu, kunshi da kitso a kan mu ni da Hafsat baya tsufa sai an sake wani, duk da muna da gashi amma kullum kanmu a kitse yake ganin sha'awa.
Episode Three: Loved by All