Sashe 83
Ƙayar Ruwa 2&3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbaa yace shi ba zai ƙarya ba amma zai iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin ya fitar da ƴarsa kunya, haka ya yankewa Yayyuna kuɗi suka haɗa dubu ɗari biyu su huɗu, aka haɗa da kuɗin aurena dubu ɗari biyar, sai kuɗin kayan lefena da aka rage Ummani ta kaiwa Sale dubu ɗari uku tace don Allah yay min furnitures masu na miliyan ɗaya irin wanda ake yayi.
To da yake ma aiki ya mayar da shi Delta state satin baya aka yi masa ƙarin girma, Kudrat ma da ta kira ni a waya tana zolayana wai ni ƴar sa'a ce, dama sun gaji da zaman Edo ɗin, ba yanda ba su yi ba a tashi a gidan yaƙi sai ga shi dole tasa an tashi babu shiri, ita da yarana suna min godiya.
Salim ɗin na cewa ba sai anyi min kayan ɗaki ba, nayi karaf kuwa nace sam bai isa ba, na wani hasala kamar wanda ya zage ni, na dinka fifiƙa ina masa masifar ai ba'a gidan babu ya tarar da ni ba, Abbaa ma ba zai yarda da zance ba, mahaifina zai yi min kayan ɗakina idan ma ya san ya siya ya aje ya kwashe abinsa ya fitar da su idan kuwa ba haka sai dai idan ba zan zauna a gidan nasa ba, ni kuwa ai ban manta gorin da Nazifi yay min ba sanda zai ƙara aure na cewan iyayen matarsa har kayan ɗaki sun mata ba irin iyayena ba da suka bar miji da ɗawainiyan komai.
Saboda yanayin nisa zuwa can garin sai Sale yace zai ɗiba mutanensa suje Delta ɗin a haɗa kayan acan maimakon ace daga nan za'a a tafi, kuɗin mota ma kansa wani babban lamarin ne, hakan kuwa aka yi aka tafi da Yaya Al'amin da Abbayo, Salim ɗin yace akwai wurin zama a gidan nasa ba sai sun nemi hayan wajen kwana ba, Abbaa yace to gwara ayi tafiya ɗaya kawai tunda bikin ƴan kwanaki ya rage a tafi ayi jere gaba ɗaya, sanda ake fito da bahhunan kwanuka sai da nayi matuƙar mamaki, Ummani ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba har sai da na tambayeta ina ta samu kuɗi haka tace rufin asirin Allah ɗan abinda take tarawa ne, sai kuma gudumawar da ƙannenta da yayyunta suka aiko mata, kayan kitchen masu kyau da tsada ni har ce nayi ma ina zan kai su.
Kwanansu biyar a can, ranar da suka dawo kuwa suna bawa Ummani labarin gidan, sai santinsa suke yi su maza ma kenan, Anty Shafa da su Anty Lubna da Maman Khairi duk sai lokacin suka ji rashin jin daÉ—in da Abbaa bai bari sun je tare ba, shi kuma yace ne da akwai Æ´an uwa acan ne sai a tafi da su, to ba za'ai rashin hankali ba kawai aje a tarewa mutum a gida, matarsa ma ba zata ji daÉ—i ba.
Abbayo na faɗin wallahi Matar Salim ɗin tana da matuƙar kirki, haka ta karrama su kamar ƴan uwanta, motsi kaɗan sai ta aiko yaranta su tambaye su ko suna da buƙatar wani abun, abinci kuwa har ci suka yi suka ture, yace kuma idan suka yi aiki suka gaji da kanta take zuwa tace musu ga babban falo can ta buɗe musu ko za su yi kallo, iya kwanakin da su kai sun mata shaida me kyau.
Da daddare na samu Abbayo ina tambayansa ya fasalin gidan yake, yace min babban gida ne flat ba bene, ɓangarena bedroom uku ne kowanne da banɗaki a ciki, sai falo biyu da kitchen, amma fa kowanne ɗaki tafkeke ne, Yace babu laifi Sale yayi ƙoƙarin yin kaya masu kyau don duk zubin kayan turkey yayi sai kallon ƙurulla ne ma zai sai za a gane b kayan ƙasar waje ba ne, kuma bedroom biyu dukka an zuba kaya a ciki, dama yanda muka yi da su nace idan sunje sunga bedroom yafi ɗaya su kirani su faɗa min sai na tura kuɗi ayi min na ɗaya ɗakin ko ba mai tsada ba, hakan kuwa aka yi da ike ina dashi kuma ina adani na tura dubu ɗari biyar nace sai ɗakin ya zama shi ne nawa wancan kuma masu tsadar sai ya zama nasa.
Abbayo har da tsokanata wai Kudrat ta fini kyau ita fara ce ƙal kamar ba ƴar ƙasar nan ba, mene mene ɗinsa dai, sai naji bala'in kishi da haushi ya kama ni har da guntuwar ƙwallana, ranar kuwa har fushi nayi da Salim yana ta kirana naƙi ɗagawa, yayo text nayi kamar ban gani ba.
_________________________
_Kuyi haƙuri don Allah wallahi banji daɗin rashin post na jiya ba, tafiya nayi garin sakkowa a mota na faɗi na yi buguwan ƙashi a hannu, duk yanda na so na ƙoƙarta wallahi abin ya faskara, naga adu'oin ku na gode sosai da sosai Allah ya saka da alkhairi._
[2/2, 07:47] Hlm: *B3ƘR09FT5*
Maman Khairi da Maman Yasmin haka suka miƙe tsaye wajen gyara ni ciki da waje, kayan mata kamar hauka Maman Yasmin tasa na tura uban kuɗi aka yo aike tun daga niger, ga Safiyya ma da nata tasa aka kawo min daga sokoto, sam ba'a son raina na ke amfani da magungunan ba, haka na ke shansu a dole wani da daɗi wani ba daɗi, wani ma sai na kusa amai ma na ke iya sha, haka zan ta yiwa Safiyya ƙorafi Maman Yasmin ma na yita mata nurƙufanci, don ni a nawa ganin wannan abubuwan duk ba su da amfani duba da irin rayuwan da nayi a baya, amfanin da na dinƙi yi da su a banza.
Safiyya ce ma me cewa ai yanzu zan san amfaninsu tunda sai yanzu ne zan yi auren, in daina lissafin wancan buhun a sahun maza, in bari in zan maganar ƴan iska mahaukata sai na ke sako shi a ciki, amma na bar tuna na taɓa aure a baya tunda dai ban haifa na baro ba.
Da Safiyya muke ta shige da ficen abubuwan da na ke siya ta ɓangarena, itama haka ta tura min 100k ta account a matsayin gudunmawa, naji daɗi sosai da kuɗin na bawa Yaya Imam nace ya siyo buhun shinkafa da fulawa sai ya bawa Abbaa. Shima yay ta min godiya har da ƙwallata don ce masa nayi sirri ne tsakanina da shi.
Na siya shadda nayi mana anko iri ɗaya ni da Ummani da Abbaa, sannan na siya wani kalan daban na ɗinkawa yayyuna da matansu da ƴanƴansu har da budurwan Yaya Al'amin ma, shigar da na ke so muyi ranar ɗaurin aure kenan, Uwata kuwa kayanta sunan sai ana gobe ɗaurin aure zan ɗakko in bata, don so na ke farin cikin saman fuskarta ya ninku sau dubun dubata, danƙararen less ne na siya mata guda biyu mai shegen tsada kuma nasa aka yi mata ɗinki na zamani, atamfofi biyu kowanne da shigar takalmi da mayafinsa, Abbaa nah ba da kala ɗaya na barsa ba bayan shaddar ɗaurin aure har da set biyu na yi masa na boyel.
Salim ya tura min dubu hamsin na kuɗin gyaran jiki da lalle da kitso, ranar kuwa Safiyya ta dinƙa masifa wai yaushe Brother ya koyi tsumulmula basu sani ba, zata kira shi na hanata sai ta kira Ummansu ta faɗa mata, Umman nasu ma ta kama faɗa wai ko bai da shi ai ba ya bani 50k a matsayin kuɗin gyaran jiki ba balle kuma yana da shi, itama tace zata kira shi taci mutuncinsa nayi ta roƙonta da ƙyar ta haƙura ta ƙyale, ko kusa bana sawa Salim ido musamman akan kuɗinsa, ni yanda yake nuna min bai da wani kuɗi, ko hira muke yi zai ce in koyi haƙurin zama da shi a yanda yake, shi ba mai kuɗi ba ne amma insha Allahu zai yi ƙoƙarin ganin ban nemi wani abu daga gare shi na rasa ba, ba zan yi kukan babu ba in Allah ya yarda, saɓanin yacca na san labarin kuɗinsa a wurin Safiyya, to nima dai a haka na ke binsa dama ni abun hannun namiji ba damuna yay ba, har ce yay min motan da yake zuwa da shi ma na ogansa ne, wannan dai na jisa ne kawai ban wani yarda ba, kawai dai na san kyauta a soyayya da daɗi musamman ma a wurin wanda zaka aura, to ni zan iya cewa bai taɓa kawo min wani abu da sunan kyauta ba, kuma ko da na faɗawa Ummani ma ce tayi kar in sa hakan a raina, ƙila tsarinsa ne a haka sai na shiga cikin gidansa tukunna zai buɗe min aljihunsa, kuma gwara ma hakan akan ya buɗa min a waje sai na shiga daga ciki kuma ya matse kayansa, idan kuwa na nuna masa ban damu ba babu ƙorafi babu tambaye tambamye balle sa ido sai nafi kima a idonsa, shi kansa sai yafi jin daɗin yi min, balle ma mene na damun kai tunda ina aikina ina samu sosai kuma ga kasuwancin da na ke na kawo min kuɗi.
Yau dai ƴan uwa sun ƙara cika gidanmu, Hajiya Ummani an kasa zaune an kasa tsaye, ayi can ayi nan, gidan ya kacame da hayaniya, ni da ban son hayaniya duk sai kaina ya ɗauka yay nauyi, na ƙagu ma ayi a gama taron a watse, du da ina ta faman mita akan me ma za'a tsaya yin wani taro aure ba auren budurwa ba, Maman Yasmin ta danno min zagi tace in ci gaba da maida kaina baya hakan yana da kyau ai.
Yau tun asuba da na tashi kasa komawa bacci nayi, Maman Khairi ma da ta ganni da duku dukun Safiya a gidan Maman Yasmin sai ta kama tsokanata wai ta lura na zaƙu dai a ɗaura auren nan, yau ni ce babu baccin asuba. Nayi dariya kawai na shige ciki ni bata san me nake wa ba, ai kuwa na sha tsiya a wurin su Adama da duk mutanenmu dai na ƙauye da suke kwana gidan Maman Yasmin, ni da naje na ƙarasa haɗa kayayyakina takurawarsu ta hana ni sai baro gidan nayi na dawo gidanmu.
To da yake ma aiki ya mayar da shi Delta state satin baya aka yi masa ƙarin girma, Kudrat ma da ta kira ni a waya tana zolayana wai ni ƴar sa'a ce, dama sun gaji da zaman Edo ɗin, ba yanda ba su yi ba a tashi a gidan yaƙi sai ga shi dole tasa an tashi babu shiri, ita da yarana suna min godiya.
Salim ɗin na cewa ba sai anyi min kayan ɗaki ba, nayi karaf kuwa nace sam bai isa ba, na wani hasala kamar wanda ya zage ni, na dinka fifiƙa ina masa masifar ai ba'a gidan babu ya tarar da ni ba, Abbaa ma ba zai yarda da zance ba, mahaifina zai yi min kayan ɗakina idan ma ya san ya siya ya aje ya kwashe abinsa ya fitar da su idan kuwa ba haka sai dai idan ba zan zauna a gidan nasa ba, ni kuwa ai ban manta gorin da Nazifi yay min ba sanda zai ƙara aure na cewan iyayen matarsa har kayan ɗaki sun mata ba irin iyayena ba da suka bar miji da ɗawainiyan komai.
Saboda yanayin nisa zuwa can garin sai Sale yace zai ɗiba mutanensa suje Delta ɗin a haɗa kayan acan maimakon ace daga nan za'a a tafi, kuɗin mota ma kansa wani babban lamarin ne, hakan kuwa aka yi aka tafi da Yaya Al'amin da Abbayo, Salim ɗin yace akwai wurin zama a gidan nasa ba sai sun nemi hayan wajen kwana ba, Abbaa yace to gwara ayi tafiya ɗaya kawai tunda bikin ƴan kwanaki ya rage a tafi ayi jere gaba ɗaya, sanda ake fito da bahhunan kwanuka sai da nayi matuƙar mamaki, Ummani ba ƙaramin ƙoƙari tayi ba har sai da na tambayeta ina ta samu kuɗi haka tace rufin asirin Allah ɗan abinda take tarawa ne, sai kuma gudumawar da ƙannenta da yayyunta suka aiko mata, kayan kitchen masu kyau da tsada ni har ce nayi ma ina zan kai su.
Kwanansu biyar a can, ranar da suka dawo kuwa suna bawa Ummani labarin gidan, sai santinsa suke yi su maza ma kenan, Anty Shafa da su Anty Lubna da Maman Khairi duk sai lokacin suka ji rashin jin daÉ—in da Abbaa bai bari sun je tare ba, shi kuma yace ne da akwai Æ´an uwa acan ne sai a tafi da su, to ba za'ai rashin hankali ba kawai aje a tarewa mutum a gida, matarsa ma ba zata ji daÉ—i ba.
Abbayo na faɗin wallahi Matar Salim ɗin tana da matuƙar kirki, haka ta karrama su kamar ƴan uwanta, motsi kaɗan sai ta aiko yaranta su tambaye su ko suna da buƙatar wani abun, abinci kuwa har ci suka yi suka ture, yace kuma idan suka yi aiki suka gaji da kanta take zuwa tace musu ga babban falo can ta buɗe musu ko za su yi kallo, iya kwanakin da su kai sun mata shaida me kyau.
Da daddare na samu Abbayo ina tambayansa ya fasalin gidan yake, yace min babban gida ne flat ba bene, ɓangarena bedroom uku ne kowanne da banɗaki a ciki, sai falo biyu da kitchen, amma fa kowanne ɗaki tafkeke ne, Yace babu laifi Sale yayi ƙoƙarin yin kaya masu kyau don duk zubin kayan turkey yayi sai kallon ƙurulla ne ma zai sai za a gane b kayan ƙasar waje ba ne, kuma bedroom biyu dukka an zuba kaya a ciki, dama yanda muka yi da su nace idan sunje sunga bedroom yafi ɗaya su kirani su faɗa min sai na tura kuɗi ayi min na ɗaya ɗakin ko ba mai tsada ba, hakan kuwa aka yi da ike ina dashi kuma ina adani na tura dubu ɗari biyar nace sai ɗakin ya zama shi ne nawa wancan kuma masu tsadar sai ya zama nasa.
Abbayo har da tsokanata wai Kudrat ta fini kyau ita fara ce ƙal kamar ba ƴar ƙasar nan ba, mene mene ɗinsa dai, sai naji bala'in kishi da haushi ya kama ni har da guntuwar ƙwallana, ranar kuwa har fushi nayi da Salim yana ta kirana naƙi ɗagawa, yayo text nayi kamar ban gani ba.
_________________________
_Kuyi haƙuri don Allah wallahi banji daɗin rashin post na jiya ba, tafiya nayi garin sakkowa a mota na faɗi na yi buguwan ƙashi a hannu, duk yanda na so na ƙoƙarta wallahi abin ya faskara, naga adu'oin ku na gode sosai da sosai Allah ya saka da alkhairi._
[2/2, 07:47] Hlm: *B3ƘR09FT5*
Maman Khairi da Maman Yasmin haka suka miƙe tsaye wajen gyara ni ciki da waje, kayan mata kamar hauka Maman Yasmin tasa na tura uban kuɗi aka yo aike tun daga niger, ga Safiyya ma da nata tasa aka kawo min daga sokoto, sam ba'a son raina na ke amfani da magungunan ba, haka na ke shansu a dole wani da daɗi wani ba daɗi, wani ma sai na kusa amai ma na ke iya sha, haka zan ta yiwa Safiyya ƙorafi Maman Yasmin ma na yita mata nurƙufanci, don ni a nawa ganin wannan abubuwan duk ba su da amfani duba da irin rayuwan da nayi a baya, amfanin da na dinƙi yi da su a banza.
Safiyya ce ma me cewa ai yanzu zan san amfaninsu tunda sai yanzu ne zan yi auren, in daina lissafin wancan buhun a sahun maza, in bari in zan maganar ƴan iska mahaukata sai na ke sako shi a ciki, amma na bar tuna na taɓa aure a baya tunda dai ban haifa na baro ba.
Da Safiyya muke ta shige da ficen abubuwan da na ke siya ta ɓangarena, itama haka ta tura min 100k ta account a matsayin gudunmawa, naji daɗi sosai da kuɗin na bawa Yaya Imam nace ya siyo buhun shinkafa da fulawa sai ya bawa Abbaa. Shima yay ta min godiya har da ƙwallata don ce masa nayi sirri ne tsakanina da shi.
Na siya shadda nayi mana anko iri ɗaya ni da Ummani da Abbaa, sannan na siya wani kalan daban na ɗinkawa yayyuna da matansu da ƴanƴansu har da budurwan Yaya Al'amin ma, shigar da na ke so muyi ranar ɗaurin aure kenan, Uwata kuwa kayanta sunan sai ana gobe ɗaurin aure zan ɗakko in bata, don so na ke farin cikin saman fuskarta ya ninku sau dubun dubata, danƙararen less ne na siya mata guda biyu mai shegen tsada kuma nasa aka yi mata ɗinki na zamani, atamfofi biyu kowanne da shigar takalmi da mayafinsa, Abbaa nah ba da kala ɗaya na barsa ba bayan shaddar ɗaurin aure har da set biyu na yi masa na boyel.
Salim ya tura min dubu hamsin na kuɗin gyaran jiki da lalle da kitso, ranar kuwa Safiyya ta dinƙa masifa wai yaushe Brother ya koyi tsumulmula basu sani ba, zata kira shi na hanata sai ta kira Ummansu ta faɗa mata, Umman nasu ma ta kama faɗa wai ko bai da shi ai ba ya bani 50k a matsayin kuɗin gyaran jiki ba balle kuma yana da shi, itama tace zata kira shi taci mutuncinsa nayi ta roƙonta da ƙyar ta haƙura ta ƙyale, ko kusa bana sawa Salim ido musamman akan kuɗinsa, ni yanda yake nuna min bai da wani kuɗi, ko hira muke yi zai ce in koyi haƙurin zama da shi a yanda yake, shi ba mai kuɗi ba ne amma insha Allahu zai yi ƙoƙarin ganin ban nemi wani abu daga gare shi na rasa ba, ba zan yi kukan babu ba in Allah ya yarda, saɓanin yacca na san labarin kuɗinsa a wurin Safiyya, to nima dai a haka na ke binsa dama ni abun hannun namiji ba damuna yay ba, har ce yay min motan da yake zuwa da shi ma na ogansa ne, wannan dai na jisa ne kawai ban wani yarda ba, kawai dai na san kyauta a soyayya da daɗi musamman ma a wurin wanda zaka aura, to ni zan iya cewa bai taɓa kawo min wani abu da sunan kyauta ba, kuma ko da na faɗawa Ummani ma ce tayi kar in sa hakan a raina, ƙila tsarinsa ne a haka sai na shiga cikin gidansa tukunna zai buɗe min aljihunsa, kuma gwara ma hakan akan ya buɗa min a waje sai na shiga daga ciki kuma ya matse kayansa, idan kuwa na nuna masa ban damu ba babu ƙorafi babu tambaye tambamye balle sa ido sai nafi kima a idonsa, shi kansa sai yafi jin daɗin yi min, balle ma mene na damun kai tunda ina aikina ina samu sosai kuma ga kasuwancin da na ke na kawo min kuɗi.
Yau dai ƴan uwa sun ƙara cika gidanmu, Hajiya Ummani an kasa zaune an kasa tsaye, ayi can ayi nan, gidan ya kacame da hayaniya, ni da ban son hayaniya duk sai kaina ya ɗauka yay nauyi, na ƙagu ma ayi a gama taron a watse, du da ina ta faman mita akan me ma za'a tsaya yin wani taro aure ba auren budurwa ba, Maman Yasmin ta danno min zagi tace in ci gaba da maida kaina baya hakan yana da kyau ai.
Yau tun asuba da na tashi kasa komawa bacci nayi, Maman Khairi ma da ta ganni da duku dukun Safiya a gidan Maman Yasmin sai ta kama tsokanata wai ta lura na zaƙu dai a ɗaura auren nan, yau ni ce babu baccin asuba. Nayi dariya kawai na shige ciki ni bata san me nake wa ba, ai kuwa na sha tsiya a wurin su Adama da duk mutanenmu dai na ƙauye da suke kwana gidan Maman Yasmin, ni da naje na ƙarasa haɗa kayayyakina takurawarsu ta hana ni sai baro gidan nayi na dawo gidanmu.