Sashe 60
Ƙayar Ruwa 2&3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yaron yace,"Ehh mota biyu ce har da sojoji".
Gaban Ummani ya yanke ya faɗi ya bada rasss, tayi saurin dafe ƙirji tana faɗin,"Sojoji kuma ɗan nan? An ya ba makuwa ka yi ba kuwa, ko can ɗaya gidan aka aika ka kusa da me kayan miya".
Yace,"A'a ni dai nan suka ce min".
"To shikenan je ka kace musu bai dawo daga kasuwa ba sai dare".
Yaron ya juya ya fita ita kuma ta dawo cikin É—aki, ta kasa zaune tayi tsaye tana tunanin lafiya? Me zai kawo sojoji neman Abbaan su? Sai tayi maza ta É—auki wayarta ta yiwa Sa'ida flashing, Sa'ida ta biyo bayan kiran, ta É—aga tana ce mata,"Ke sako min kati zan kira Abban ku".
Yanayin fitar muryan nata yasa Sa'ida cewa"Lafiya Ummani?".
"Lafiya lau sauri sako min zan ba shi sallahu ne a kasuwa kar ya riga ya taho".
Within one minutes sai ga shigowan katin ɗari biyar a wayar, ta lalubo sunan Abbaan Sa'id ta kira. Abbaa a lokacin na bakin titi ya ɗaga kiran wanda hayaniyar ƙarar ababen hawa bai barin sa yaji me take cewa itama ɗin kuma bata jinsa sosai, haka tayi ta faman kira ƙarshe sai haƙura tayi, ta fito tsakar gida ta zauna tayi jugum, har sai da ta leƙa ƙofar gidan taga tabbacin maganar yaron, soja ɗaya na tsaye bakin mota da bindiga a hannu, wannan fa yasa ta daɗa tsurewa ta kama safa da marwa a tsakar gida tana ta faɗin Allah sa lafiya.
Bayan kusan rabin awa sai ga Abbaa ya shigo gidan a gaggauce yana ƙwala kiran,"Sa'a! Sa'a! miƙo min babbar tabarma maza maza".
Irin yanda yake ƙwala kiran bana lafiya ba, Ummani ta fito daga ɗaki fuskar hijabi a juye jiki duk sai ɓari yake yi, ganin yanda Abbaan yake shima da ruɗani ta tsaya tambayan,"Abbaa lafiya? Kaga baƙin ƙofar gidan ne kaima?".
Bai amsa mata ba yaci gaba da ɗauraye ƙafarsa da duk tayi ƙura tare da wanke fuskarsa ma. "Ni dai sauri miƙo min tabarmar tukunna, ni kaina ba na ce miki lafiya ko ba lafiya ba Sa'a, amma hankalina duk ya tashi".
"Abbaa to kaje wurin su kuwa? Ko na aika a kira Yashaik yau yana gida bai fita ba".
"A'a ƙyale su Sa'a, bara na fara jin me ke tafe da su sun ce sun jima waje, maza miƙo min tabarmar dai, kin san irin mutanen ba'a barin su da jira".
Ganin ta tsaya kawai ya wuceta yay ɗakinsa ya buɗe ya yayibo tabarma ya fito yay waje da hanzari, duk ya rikice tafiyar tamkar zai kifa ƙasa. A soro ya baza ƙatuwar tabarmar, takalamansa ma a baibai ya saka ya leƙa yana ce musu,"Bismillah ku shigo daga ciki".
Zatonsa iyaka waɗannan sojoji biyun na waje ne sai yaga an buɗe mota manyan mutane dattawan arziƙi suna fitowa, da kallo ɗaya ba sai ka ƙara na biyu zaka shaida duniya ta san su ta san da zaman su, matsayi kuma an same shi sai wanda ake kan rabawa, kuma masu faɗa ne aji a ƙasar da suke ciki.
Sojojin na basu kariya har suka shigo soron wanda duk Abbaa ya daɗa hargitsewa yana duban tabarmar da duk ta ɗan sha jiki, da shi kansa soron gidan wanda yake ganin sun girmi su ko rakuɓe a cikinsa balle zama.
Sai dai ga mamakinsa babu wani yanayi na ƙyama ko jin kai a tare da su, duk sai yake jin wani iri, bai taɓa yin baƙo yana jin ya ƙasƙantar da shi duba da irin muhallinsa ba sai waɗannan mutanen.
"To ko kujera za a samo muku?".
ÆŠaya daga cikin su yace,"A'a babu komai Malam, ai nan É—in ma Alhamdulillahi ya isa, ga shi duk mun zauna, muna godiya da karramawa".
Sai da duk suka gama zama sannan ya zauna yana mai fuskantarsu, ya ranƙwafa kamar bafaden sarki, da firgicin da ke tare da shi ya shiga miƙa musu hannu wanda a farko sai da yaji shakkar hakan, sai kuma yaga saɓanin fa yanda yake tunaninsu ne domin da kansu suka miƙo masa nasu suna gaisawa da girmama junansu da kuma mutuntawa.
Cikin wani yanayi Abbaa da bai taɓa shigansa ba yake kallon tsohon mutumin da ke cewa da shi,"Da ka natsu naga duk ka dabarbarce da ganin namu".
Abbaa yace,"To ai ranka ya daÉ—e ganin mutane irinku dole mutum ya shiga irin wannan yanayin na ruÉ—ani, ni dai fatana Allah yasa lafiya, Allah yasa lafiya don cikin gida ma kanta iyalina a tsaye take".
Alhaji Sama'ila ya murmusa yana duban Abbaa da kyau yace,"Kar ka samu damuwa lafiya lau, Alkhairi ne ya kawo mu gare ka, saboda haka ka bar tunanin ko ba lafiya ba ne".
Sai sannan Abbaan ya samu ya ɗan sauke ajiyar zuciya ta salama yace,"To masha Allahu, bara a miƙo muku ruwa".
Ya yunƙura zai miƙe sai ga wani baƙon ya shigo, Abbaa ya kalle shi cikin faɗaɗa fara'ar fuskarsa yay saurin miƙewa yana miƙawa Baba hannu yace,"A'a Alhaji Babangida kai ne da kanka a gidan nawa, barka da zuwa".
Baban su Safiyya shima cikin fara'ar da ke wadatuwa saman fuskarsa yake cewa da Abbaa,"Malam Salman ka ganni kwatsam ko, to ya za'ai zuwa ya zamar mana dole".
"Wallahi fa, kar dai kace min tare ku ke da waÉ—annan bayin Allah'n?".
Baban su Safiyya yace,"Tare muke da su, da yake ni uzuri ya ɗan riƙe ni a hanya ne shiyasa suka riga ni isowa, tafiyar ai tawa ce ma gaba ɗaya, na ke ce musu ai gida muka nufa su isa kafin na ƙaraso".
Baban su Safiyya ya nemi waje ya zauna yana magana da jama'arsa, yayin da Abbaa ya shiga daga cikin gidan yana kiran sunan Ummani a hankali saboda ana iyo jiyo maganar tsakar gida daga soron. Ummani kuwa na kitchen a lokacin ta rafka tagumi tana jinsa ta taso da sauri tana buÉ—a masa hannu alamun ya ake ciki.
"To bana ce ba amma dai sun ce lafiya lau alkhairi ya kawo su, don tafiyar ma har da Alhaji Babangida".
"Alhaji Babangida dai?".
"Baban yarinyar nan ƙawar Sa'ida, bani sunanta nan, yauwa Safiyya".
Ummani ta sauke nauyayyan numfashi da cewar,"Ohhh har na samu Sa'ida amma da hankalina duk ya tashi ina ta tunanin me zai kawo mana sojoji wajenka, don wallahi har na fara zargin ko matsalar rumfar nan ce".
Yanayin fuskan Abbaan dai gata nan yace,"Samu faranti ki zubo lemu da ruwa".
Ummani ta koma kicin ta ɗauko farantai guda biyu, shi kuma Abbaa ya shiga ɗakin Sa'ida inda firiji ke ajiye ya kwaso kunun aya da ruwa. Yasmin ta shigo Abbaan ya bata faranti ɗaya yace ta kaiwa baƙin waje, Ummani kuma na cewa da shi,"To ai kai musu waɗancan kofunan robar kuwa? Da dai an bar musu a jarkunan? Ko na aika Yusra ta bada kofunan tangaran ɗinta".
"Bar shi akai musu hakan ai sun san inda suka zo".
"To shikenan Allah sa khairan É—in da gaske".
Ta faɗa tana bin bayan Abbaa da kallo har ya fice. Kafin ta shiga daga ɗaki tana cewa bari ta kira Sa'ida ta faɗa mata ko zata siyo kofunan ƴan gayu a hanya saboda zuwan manyan baƙi irin haka, ranar nan ma haka ta zo da ma'aikatan asibitinsu duk sai taji kunya saboda irin farantin da aka zuba musu abinci, to da yake dai baka kunya da matsayin da Allah ya aje ka.
Abbaa ya zauna suna ƙara gaisawa da juna, bayan an taɓa ƴar hira tsakanin Abbaa da Baban su Safiyya sai Alhaji Surajo ke cewa,"Tom Babangida kayi masa bayanin me ke tafe da mu ko".
Baban su Safiyya na jijjiga kai yace,"Ƙwarai haka ne, bama biyewa hirarmu da ba zata ƙare ba, zumunci yay ƙaranci wai don ma Allah ya haɗa kan ƴaƴan namu sunata na su zumuncin".
Abbaa yace,"Wallahi fa Alhajin Allah, da sai a wuce shekaru masu yawan gaske ma ba'a gaisa ba ko ta wayar, zumuncin zamanin sai adu'a sai mutum yayi da gaske zai samu ladansa".
Baban su Safiyya ya numfasa kana ya dubi Abbaa yana yi masa nuni da babban mutumin da ke tsakiya me cikar kamala da dattako, wanda Abbaa zai iya cewa dama tun zuwansu yaji mutumin ya cika wurin da haibarsa, kuma yana da tabbacin ƙamshinsa ne ya gauraye dukka wajen tun daga ƙofar gida har cikin gida.
A hankali Baban su Safiyya yace,"Malam Salman wannan shi ne Major Sadiq Oluwa Ibrahim, Yayar Matata ne uwa ɗaya uba ɗaya domin a wurinsa ma na karɓi auren ƙanwarsa, na kusa da shi kuma kusan mahaifi ne a wurinmu sunansa Captain Adebisi Oluwa...waɗannan kuma duk da kake gani abokai ne sai wancan". Ya faɗa yana nuni ma Abbaa da na kusa da shi yace,"Shi ƙane ne a wajen Major, sunansa Alhaji Mukhtar Oluwa".
Abbaa yana ƙara rissinar da kai yace,"To masha Allahu, madallah dukkanku ina ƙara yi muku maraba, ayi haƙuri dai da irin wajen da aka samu".
Captain Adebisi yace,"A haba dai haba dai muma duk irin namu muhallin kenan".
Baban su Safiyya ya ƙara cewa,"To Malam Salman abin da yake tafe da mu muhimmin abu ne, magana ce babba, kuma alkhairi ne ya kawo mu gareka, sai dai bamu san a yanda zaka karɓi al'amarin ba, duba da cewa mun sake dawowa ne a karo na biyu da buƙata iri ɗaya, amma a wannan karan muna fatan samun karɓuwar tayin mu saɓanin baya da bamu samu karɓuwa ba".
Abbaa yace,"To Alhajin Allah a ɗan warware ni ko, an saka ni a duhu". Ya faɗu haƙoransa a waje fuskarsa washe da fara'a.
Major Sadiq wato Sir kamar yanda ƴaƴansa ke kiransa yay nisa tare da numfasawa, yana daɗa kallon fuskar Abbaa da ke kama da ta Sa'ida sak wadda ya gani a cikin jirgi ranar da zasu kaita makaranta, kafin ya fara magana a cikin birkitacciyar hausarsa ta yarabawa yace,"Ammm Malam Salman mun zo wurinka ne a dalilin Yarona, wato dai mun zo nema masa auren ƴarka da ya gani yake so, idan ba'a rigada an tsayar mata da mijin aure ba shi yana da buƙatar aurenta, aure nan kusa ba tare da anja lokaci ba".
Gaban Ummani ya yanke ya faɗi ya bada rasss, tayi saurin dafe ƙirji tana faɗin,"Sojoji kuma ɗan nan? An ya ba makuwa ka yi ba kuwa, ko can ɗaya gidan aka aika ka kusa da me kayan miya".
Yace,"A'a ni dai nan suka ce min".
"To shikenan je ka kace musu bai dawo daga kasuwa ba sai dare".
Yaron ya juya ya fita ita kuma ta dawo cikin É—aki, ta kasa zaune tayi tsaye tana tunanin lafiya? Me zai kawo sojoji neman Abbaan su? Sai tayi maza ta É—auki wayarta ta yiwa Sa'ida flashing, Sa'ida ta biyo bayan kiran, ta É—aga tana ce mata,"Ke sako min kati zan kira Abban ku".
Yanayin fitar muryan nata yasa Sa'ida cewa"Lafiya Ummani?".
"Lafiya lau sauri sako min zan ba shi sallahu ne a kasuwa kar ya riga ya taho".
Within one minutes sai ga shigowan katin ɗari biyar a wayar, ta lalubo sunan Abbaan Sa'id ta kira. Abbaa a lokacin na bakin titi ya ɗaga kiran wanda hayaniyar ƙarar ababen hawa bai barin sa yaji me take cewa itama ɗin kuma bata jinsa sosai, haka tayi ta faman kira ƙarshe sai haƙura tayi, ta fito tsakar gida ta zauna tayi jugum, har sai da ta leƙa ƙofar gidan taga tabbacin maganar yaron, soja ɗaya na tsaye bakin mota da bindiga a hannu, wannan fa yasa ta daɗa tsurewa ta kama safa da marwa a tsakar gida tana ta faɗin Allah sa lafiya.
Bayan kusan rabin awa sai ga Abbaa ya shigo gidan a gaggauce yana ƙwala kiran,"Sa'a! Sa'a! miƙo min babbar tabarma maza maza".
Irin yanda yake ƙwala kiran bana lafiya ba, Ummani ta fito daga ɗaki fuskar hijabi a juye jiki duk sai ɓari yake yi, ganin yanda Abbaan yake shima da ruɗani ta tsaya tambayan,"Abbaa lafiya? Kaga baƙin ƙofar gidan ne kaima?".
Bai amsa mata ba yaci gaba da ɗauraye ƙafarsa da duk tayi ƙura tare da wanke fuskarsa ma. "Ni dai sauri miƙo min tabarmar tukunna, ni kaina ba na ce miki lafiya ko ba lafiya ba Sa'a, amma hankalina duk ya tashi".
"Abbaa to kaje wurin su kuwa? Ko na aika a kira Yashaik yau yana gida bai fita ba".
"A'a ƙyale su Sa'a, bara na fara jin me ke tafe da su sun ce sun jima waje, maza miƙo min tabarmar dai, kin san irin mutanen ba'a barin su da jira".
Ganin ta tsaya kawai ya wuceta yay ɗakinsa ya buɗe ya yayibo tabarma ya fito yay waje da hanzari, duk ya rikice tafiyar tamkar zai kifa ƙasa. A soro ya baza ƙatuwar tabarmar, takalamansa ma a baibai ya saka ya leƙa yana ce musu,"Bismillah ku shigo daga ciki".
Zatonsa iyaka waɗannan sojoji biyun na waje ne sai yaga an buɗe mota manyan mutane dattawan arziƙi suna fitowa, da kallo ɗaya ba sai ka ƙara na biyu zaka shaida duniya ta san su ta san da zaman su, matsayi kuma an same shi sai wanda ake kan rabawa, kuma masu faɗa ne aji a ƙasar da suke ciki.
Sojojin na basu kariya har suka shigo soron wanda duk Abbaa ya daɗa hargitsewa yana duban tabarmar da duk ta ɗan sha jiki, da shi kansa soron gidan wanda yake ganin sun girmi su ko rakuɓe a cikinsa balle zama.
Sai dai ga mamakinsa babu wani yanayi na ƙyama ko jin kai a tare da su, duk sai yake jin wani iri, bai taɓa yin baƙo yana jin ya ƙasƙantar da shi duba da irin muhallinsa ba sai waɗannan mutanen.
"To ko kujera za a samo muku?".
ÆŠaya daga cikin su yace,"A'a babu komai Malam, ai nan É—in ma Alhamdulillahi ya isa, ga shi duk mun zauna, muna godiya da karramawa".
Sai da duk suka gama zama sannan ya zauna yana mai fuskantarsu, ya ranƙwafa kamar bafaden sarki, da firgicin da ke tare da shi ya shiga miƙa musu hannu wanda a farko sai da yaji shakkar hakan, sai kuma yaga saɓanin fa yanda yake tunaninsu ne domin da kansu suka miƙo masa nasu suna gaisawa da girmama junansu da kuma mutuntawa.
Cikin wani yanayi Abbaa da bai taɓa shigansa ba yake kallon tsohon mutumin da ke cewa da shi,"Da ka natsu naga duk ka dabarbarce da ganin namu".
Abbaa yace,"To ai ranka ya daÉ—e ganin mutane irinku dole mutum ya shiga irin wannan yanayin na ruÉ—ani, ni dai fatana Allah yasa lafiya, Allah yasa lafiya don cikin gida ma kanta iyalina a tsaye take".
Alhaji Sama'ila ya murmusa yana duban Abbaa da kyau yace,"Kar ka samu damuwa lafiya lau, Alkhairi ne ya kawo mu gare ka, saboda haka ka bar tunanin ko ba lafiya ba ne".
Sai sannan Abbaan ya samu ya ɗan sauke ajiyar zuciya ta salama yace,"To masha Allahu, bara a miƙo muku ruwa".
Ya yunƙura zai miƙe sai ga wani baƙon ya shigo, Abbaa ya kalle shi cikin faɗaɗa fara'ar fuskarsa yay saurin miƙewa yana miƙawa Baba hannu yace,"A'a Alhaji Babangida kai ne da kanka a gidan nawa, barka da zuwa".
Baban su Safiyya shima cikin fara'ar da ke wadatuwa saman fuskarsa yake cewa da Abbaa,"Malam Salman ka ganni kwatsam ko, to ya za'ai zuwa ya zamar mana dole".
"Wallahi fa, kar dai kace min tare ku ke da waÉ—annan bayin Allah'n?".
Baban su Safiyya yace,"Tare muke da su, da yake ni uzuri ya ɗan riƙe ni a hanya ne shiyasa suka riga ni isowa, tafiyar ai tawa ce ma gaba ɗaya, na ke ce musu ai gida muka nufa su isa kafin na ƙaraso".
Baban su Safiyya ya nemi waje ya zauna yana magana da jama'arsa, yayin da Abbaa ya shiga daga cikin gidan yana kiran sunan Ummani a hankali saboda ana iyo jiyo maganar tsakar gida daga soron. Ummani kuwa na kitchen a lokacin ta rafka tagumi tana jinsa ta taso da sauri tana buÉ—a masa hannu alamun ya ake ciki.
"To bana ce ba amma dai sun ce lafiya lau alkhairi ya kawo su, don tafiyar ma har da Alhaji Babangida".
"Alhaji Babangida dai?".
"Baban yarinyar nan ƙawar Sa'ida, bani sunanta nan, yauwa Safiyya".
Ummani ta sauke nauyayyan numfashi da cewar,"Ohhh har na samu Sa'ida amma da hankalina duk ya tashi ina ta tunanin me zai kawo mana sojoji wajenka, don wallahi har na fara zargin ko matsalar rumfar nan ce".
Yanayin fuskan Abbaan dai gata nan yace,"Samu faranti ki zubo lemu da ruwa".
Ummani ta koma kicin ta ɗauko farantai guda biyu, shi kuma Abbaa ya shiga ɗakin Sa'ida inda firiji ke ajiye ya kwaso kunun aya da ruwa. Yasmin ta shigo Abbaan ya bata faranti ɗaya yace ta kaiwa baƙin waje, Ummani kuma na cewa da shi,"To ai kai musu waɗancan kofunan robar kuwa? Da dai an bar musu a jarkunan? Ko na aika Yusra ta bada kofunan tangaran ɗinta".
"Bar shi akai musu hakan ai sun san inda suka zo".
"To shikenan Allah sa khairan É—in da gaske".
Ta faɗa tana bin bayan Abbaa da kallo har ya fice. Kafin ta shiga daga ɗaki tana cewa bari ta kira Sa'ida ta faɗa mata ko zata siyo kofunan ƴan gayu a hanya saboda zuwan manyan baƙi irin haka, ranar nan ma haka ta zo da ma'aikatan asibitinsu duk sai taji kunya saboda irin farantin da aka zuba musu abinci, to da yake dai baka kunya da matsayin da Allah ya aje ka.
Abbaa ya zauna suna ƙara gaisawa da juna, bayan an taɓa ƴar hira tsakanin Abbaa da Baban su Safiyya sai Alhaji Surajo ke cewa,"Tom Babangida kayi masa bayanin me ke tafe da mu ko".
Baban su Safiyya na jijjiga kai yace,"Ƙwarai haka ne, bama biyewa hirarmu da ba zata ƙare ba, zumunci yay ƙaranci wai don ma Allah ya haɗa kan ƴaƴan namu sunata na su zumuncin".
Abbaa yace,"Wallahi fa Alhajin Allah, da sai a wuce shekaru masu yawan gaske ma ba'a gaisa ba ko ta wayar, zumuncin zamanin sai adu'a sai mutum yayi da gaske zai samu ladansa".
Baban su Safiyya ya numfasa kana ya dubi Abbaa yana yi masa nuni da babban mutumin da ke tsakiya me cikar kamala da dattako, wanda Abbaa zai iya cewa dama tun zuwansu yaji mutumin ya cika wurin da haibarsa, kuma yana da tabbacin ƙamshinsa ne ya gauraye dukka wajen tun daga ƙofar gida har cikin gida.
A hankali Baban su Safiyya yace,"Malam Salman wannan shi ne Major Sadiq Oluwa Ibrahim, Yayar Matata ne uwa ɗaya uba ɗaya domin a wurinsa ma na karɓi auren ƙanwarsa, na kusa da shi kuma kusan mahaifi ne a wurinmu sunansa Captain Adebisi Oluwa...waɗannan kuma duk da kake gani abokai ne sai wancan". Ya faɗa yana nuni ma Abbaa da na kusa da shi yace,"Shi ƙane ne a wajen Major, sunansa Alhaji Mukhtar Oluwa".
Abbaa yana ƙara rissinar da kai yace,"To masha Allahu, madallah dukkanku ina ƙara yi muku maraba, ayi haƙuri dai da irin wajen da aka samu".
Captain Adebisi yace,"A haba dai haba dai muma duk irin namu muhallin kenan".
Baban su Safiyya ya ƙara cewa,"To Malam Salman abin da yake tafe da mu muhimmin abu ne, magana ce babba, kuma alkhairi ne ya kawo mu gareka, sai dai bamu san a yanda zaka karɓi al'amarin ba, duba da cewa mun sake dawowa ne a karo na biyu da buƙata iri ɗaya, amma a wannan karan muna fatan samun karɓuwar tayin mu saɓanin baya da bamu samu karɓuwa ba".
Abbaa yace,"To Alhajin Allah a ɗan warware ni ko, an saka ni a duhu". Ya faɗu haƙoransa a waje fuskarsa washe da fara'a.
Major Sadiq wato Sir kamar yanda ƴaƴansa ke kiransa yay nisa tare da numfasawa, yana daɗa kallon fuskar Abbaa da ke kama da ta Sa'ida sak wadda ya gani a cikin jirgi ranar da zasu kaita makaranta, kafin ya fara magana a cikin birkitacciyar hausarsa ta yarabawa yace,"Ammm Malam Salman mun zo wurinka ne a dalilin Yarona, wato dai mun zo nema masa auren ƴarka da ya gani yake so, idan ba'a rigada an tsayar mata da mijin aure ba shi yana da buƙatar aurenta, aure nan kusa ba tare da anja lokaci ba".