Sashe 67
Ƙayar Ruwa 2&3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya yunƙura zai miƙe sai ga wani baƙon ya shigo, Abbaa ya kalle shi cikin faɗaɗa fara'ar fuskarsa yay saurin miƙewa yana miƙawa Baba hannu yace,"A'a Alhaji Babangida kai ne da kanka a gidan nawa, barka da zuwa".
Baban su Safiyya shima cikin fara'ar da ke wadatuwa saman fuskarsa yake cewa da Abbaa,"Malam Salman ka ganni kwatsam ko, to ya za'ai zuwa ya zamar mana dole".
"Wallahi fa, kar dai kace min tare ku ke da waÉ—annan bayin Allah'n?".
Baban su Safiyya yace,"Tare muke da su, da yake ni uzuri ya ɗan riƙe ni a hanya ne shiyasa suka riga ni isowa, tafiyar ai tawa ce ma gaba ɗaya, na ke ce musu ai gida muka nufa su isa kafin na ƙaraso".
Baban su Safiyya ya nemi waje ya zauna yana magana da jama'arsa, yayin da Abbaa ya shiga daga cikin gidan yana kiran sunan Ummani a hankali saboda ana iyo jiyo maganar tsakar gida daga soron. Ummani kuwa na kitchen a lokacin ta rafka tagumi tana jinsa ta taso da sauri tana buÉ—a masa hannu alamun ya ake ciki.
"To bana ce ba amma dai sun ce lafiya lau alkhairi ya kawo su, don tafiyar ma har da Alhaji Babangida".
"Alhaji Babangida dai?".
"Baban yarinyar nan ƙawar Sa'ida, bani sunanta nan, yauwa Safiyya".
Ummani ta sauke nauyayyan numfashi da cewar,"Ohhh har na samu Sa'ida amma da hankalina duk ya tashi ina ta tunanin me zai kawo mana sojoji wajenka, don wallahi har na fara zargin ko matsalar rumfar nan ce".
Yanayin fuskan Abbaan dai gata nan yace,"Samu faranti ki zubo lemu da ruwa".
Ummani ta koma kicin ta ɗauko farantai guda biyu, shi kuma Abbaa ya shiga ɗakin Sa'ida inda firiji ke ajiye ya kwaso kunun aya da ruwa. Yasmin ta shigo Abbaan ya bata faranti ɗaya yace ta kaiwa baƙin waje, Ummani kuma na cewa da shi,"To ai kai musu waɗancan kofunan robar kuwa? Da dai an bar musu a jarkunan? Ko na aika Yusra ta bada kofunan tangaran ɗinta".
"Bar shi akai musu hakan ai sun san inda suka zo".
"To shikenan Allah sa khairan É—in da gaske".
Ta faɗa tana bin bayan Abbaa da kallo har ya fice. Kafin ta shiga daga ɗaki tana cewa bari ta kira Sa'ida ta faɗa mata ko zata siyo kofunan ƴan gayu a hanya saboda zuwan manyan baƙi irin haka, ranar nan ma haka ta zo da ma'aikatan asibitinsu duk sai taji kunya saboda irin farantin da aka zuba musu abinci, to da yake dai baka kunya da matsayin da Allah ya aje ka.
Abbaa ya zauna suna ƙara gaisawa da juna, bayan an taɓa ƴar hira tsakanin Abbaa da Baban su Safiyya sai Alhaji Surajo ke cewa,"Tom Babangida kayi masa bayanin me ke tafe da mu ko".
Baban su Safiyya na jijjiga kai yace,"Ƙwarai haka ne, bama biyewa hirarmu da ba zata ƙare ba, zumunci yay ƙaranci wai don ma Allah ya haɗa kan ƴaƴan namu sunata na su zumuncin".
Abbaa yace,"Wallahi fa Alhajin Allah, da sai a wuce shekaru masu yawan gaske ma ba'a gaisa ba ko ta wayar, zumuncin zamanin sai adu'a sai mutum yayi da gaske zai samu ladansa".
Baban su Safiyya ya numfasa kana ya dubi Abbaa yana yi masa nuni da babban mutumin da ke tsakiya me cikar kamala da dattako, wanda Abbaa zai iya cewa dama tun zuwansu yaji mutumin ya cika wurin da haibarsa, kuma yana da tabbacin ƙamshinsa ne ya gauraye dukka wajen tun daga ƙofar gida har cikin gida.
A hankali Baban su Safiyya yace,"Malam Salman wannan shi ne Major Sadiq Oluwa Ibrahim, Yayar Matata ne uwa ɗaya uba ɗaya domin a wurinsa ma na karɓi auren ƙanwarsa, na kusa da shi kuma kusan mahaifi ne a wurinmu sunansa Captain Adebisi Oluwa...waɗannan kuma duk da kake gani abokai ne sai wancan". Ya faɗa yana nuni ma Abbaa da na kusa da shi yace,"Shi ƙane ne a wajen Major, sunansa Alhaji Mukhtar Oluwa".
Abbaa yana ƙara rissinar da kai yace,"To masha Allahu, madallah dukkanku ina ƙara yi muku maraba, ayi haƙuri dai da irin wajen da aka samu".
Captain Adebisi yace,"A haba dai haba dai muma duk irin namu muhallin kenan".
Baban su Safiyya ya ƙara cewa,"To Malam Salman abin da yake tafe da mu muhimmin abu ne, magana ce babba, kuma alkhairi ne ya kawo mu gareka, sai dai bamu san a yanda zaka karɓi al'amarin ba, duba da cewa mun sake dawowa ne a karo na biyu da buƙata iri ɗaya, amma a wannan karan muna fatan samun karɓuwar tayin mu saɓanin baya da bamu samu karɓuwa ba".
Abbaa yace,"To Alhajin Allah a ɗan warware ni ko, an saka ni a duhu". Ya faɗu haƙoransa a waje fuskarsa washe da fara'a.
Major Sadiq wato Sir kamar yanda ƴaƴansa ke kiransa yay nisa tare da numfasawa, yana daɗa kallon fuskar Abbaa da ke kama da ta Sa'ida sak wadda ya gani a cikin jirgi ranar da zasu kaita makaranta, kafin ya fara magana a cikin birkitacciyar hausarsa ta yarabawa yace,"Ammm Malam Salman mun zo wurinka ne a dalilin Yarona, wato dai mun zo nema masa auren ƴarka da ya gani yake so, idan ba'a rigada an tsayar mata da mijin aure ba shi yana da buƙatar aurenta, aure nan kusa ba tare da anja lokaci ba".
Abbaa ya ɗaga kai a karo na biyu yaywa Major kallo na ƙurulla, sai kawai yaji kwarjinin mutumin ya dake shi, haka kuma nauyinsa ya kama shi, yay saurin ɗauke ƙwayar idonsa akansa yana me ƙara sunkuyar da kai ƙasa yace,"Ina sauraronka Ranka shi daɗe".
Major yaci gaba da cewa,"My son Salim na ɗaya daga cikin manema auren ƴarka a shekarun baya masu yawa da suka wuce, to kuma sai ubangiji ya ƙadarta cewa ba zata zama matarsa ba a wancan lokacin, shi ne a wannan karon ya turo mu gare ku da ƙoƙon bararsa yace a taimaka masa idan har wani bai riga shi ba".
Kan Abbaa ya É—aure, kafin ya kalli Baban su Safiyya yace,"Alhajin Allah ni ai har yanzu na kasa shaida É—an namu da kuke magana akai".
Baban su Safiyya yace,"Ehh to da yake a wancan karan ba mune muka zo ba gaskiya, amma ai ba zaka mance yaron da ya kawo kuɗin aure daga baya kuma aka karɓa da cewar ba zai iya jiran yarinya ta kammala karatun da aka ce masa ba, wanda kuma hakan ta faru ne duk ba da son ran zuƙatan kowa ba musamman shi yaron".
Abbaan yayi ƙayattacen murmushi da cewa,"Na tuna, na tuna hakan, to amma shi da yay wancan magana a lokacin baya ai ce na ke an wuce babin...".
Sai yay shiru kamar yanda duk suma suka yi shiru suna kallonsa. Zuciyar Major cike da fargaba da zullumin kar su ƙi amsar tayin su, don shi kansa ya kwaɗaitu wa ɗansa auren Sa'ida.
A lokacin ne kuma aka yi kiran sallar magriba, don haka duk suka miƙe Abbaa ya shiga gida Ummani ta zuba ruwa a buta guda biyu ta ba shi ya fita da ita, ta aika Yasmin wurin Umman su Hindatu ta ƙaro buta aka ƙara musu kafin Abbaan ya dawo ya karɓa masu sallaya, ita dai Ummani ganin yanayinsa na yanda yay sanyi kamar jikinsa ya mutu sai duk ta shiga damuwa da fargaba, tana tayi masa magana ma bai tsaya ya saurareta ba.
Don haka da sauri ta ɗauka waya ta kira Yashaik tace idan yana gida yay sauri ya leƙo gidan.
Ko a wajen sallah ma babu yanda Abbaa bai yi ba akan wani cikin su ya ja su sallar suka dage masa akan lallai shi ne zai ja su, haka yaja su sallar bayan sun idar kuma suka komo soron suka zauna, Abba ya amso fitila a cikin gida ya saka musu saboda soron yayi duhu a lokacin.
Bayan zaman nasu Alhaji Mukhtar yace,"Malam Salman na san kana tunani ne akan abun da ya faru a baya ko, to idan wannn ne kar ka damu, wallahi tallahi ko a baya Salim ba ya janye maganar aurensa da ƴarku ba ne saboda dalilin da aka faɗa, hasalima danne zuciyarsa yay ya haƙura a babu yanda zai yi saboda nuna masa da tayi na bata sonsa, shi kuma bai zai iya auran macen da bata sonsa ba, yana ganin idan ya nace aka yi auren zaman ba zai yi musu daɗi ba, saboda wannan dalilin a lokacin ya zo ya same ni muka yi magana ya faɗa min duk yanda suka yi da yarinya har ma ya fahimci akwai wanda ita take so, amma bai karɓi kuɗinsa don yay wulaƙanci ko tozarci ba, kum ahatta maganar da akayi a lokacin na cewa ya samu wata matar wallahi a lokacin babu wannan zancen anyi hakan ne duk don samun mafita".
Abbaa ya sake jinjina kai kafin yace,"To da wannan da wannan, don bayanin da ka min yanzu shi ne nake so na tambaya. Sai dai duk da haka akwai wani hanzari ba gudu ba, ƴata ba budurwa ba ce yanzu bazawara ce ita, wataƙila kuma bai san da hakan ba ne".
Baban su Safiyya shima cikin fara'ar da ke wadatuwa saman fuskarsa yake cewa da Abbaa,"Malam Salman ka ganni kwatsam ko, to ya za'ai zuwa ya zamar mana dole".
"Wallahi fa, kar dai kace min tare ku ke da waÉ—annan bayin Allah'n?".
Baban su Safiyya yace,"Tare muke da su, da yake ni uzuri ya ɗan riƙe ni a hanya ne shiyasa suka riga ni isowa, tafiyar ai tawa ce ma gaba ɗaya, na ke ce musu ai gida muka nufa su isa kafin na ƙaraso".
Baban su Safiyya ya nemi waje ya zauna yana magana da jama'arsa, yayin da Abbaa ya shiga daga cikin gidan yana kiran sunan Ummani a hankali saboda ana iyo jiyo maganar tsakar gida daga soron. Ummani kuwa na kitchen a lokacin ta rafka tagumi tana jinsa ta taso da sauri tana buÉ—a masa hannu alamun ya ake ciki.
"To bana ce ba amma dai sun ce lafiya lau alkhairi ya kawo su, don tafiyar ma har da Alhaji Babangida".
"Alhaji Babangida dai?".
"Baban yarinyar nan ƙawar Sa'ida, bani sunanta nan, yauwa Safiyya".
Ummani ta sauke nauyayyan numfashi da cewar,"Ohhh har na samu Sa'ida amma da hankalina duk ya tashi ina ta tunanin me zai kawo mana sojoji wajenka, don wallahi har na fara zargin ko matsalar rumfar nan ce".
Yanayin fuskan Abbaan dai gata nan yace,"Samu faranti ki zubo lemu da ruwa".
Ummani ta koma kicin ta ɗauko farantai guda biyu, shi kuma Abbaa ya shiga ɗakin Sa'ida inda firiji ke ajiye ya kwaso kunun aya da ruwa. Yasmin ta shigo Abbaan ya bata faranti ɗaya yace ta kaiwa baƙin waje, Ummani kuma na cewa da shi,"To ai kai musu waɗancan kofunan robar kuwa? Da dai an bar musu a jarkunan? Ko na aika Yusra ta bada kofunan tangaran ɗinta".
"Bar shi akai musu hakan ai sun san inda suka zo".
"To shikenan Allah sa khairan É—in da gaske".
Ta faɗa tana bin bayan Abbaa da kallo har ya fice. Kafin ta shiga daga ɗaki tana cewa bari ta kira Sa'ida ta faɗa mata ko zata siyo kofunan ƴan gayu a hanya saboda zuwan manyan baƙi irin haka, ranar nan ma haka ta zo da ma'aikatan asibitinsu duk sai taji kunya saboda irin farantin da aka zuba musu abinci, to da yake dai baka kunya da matsayin da Allah ya aje ka.
Abbaa ya zauna suna ƙara gaisawa da juna, bayan an taɓa ƴar hira tsakanin Abbaa da Baban su Safiyya sai Alhaji Surajo ke cewa,"Tom Babangida kayi masa bayanin me ke tafe da mu ko".
Baban su Safiyya na jijjiga kai yace,"Ƙwarai haka ne, bama biyewa hirarmu da ba zata ƙare ba, zumunci yay ƙaranci wai don ma Allah ya haɗa kan ƴaƴan namu sunata na su zumuncin".
Abbaa yace,"Wallahi fa Alhajin Allah, da sai a wuce shekaru masu yawan gaske ma ba'a gaisa ba ko ta wayar, zumuncin zamanin sai adu'a sai mutum yayi da gaske zai samu ladansa".
Baban su Safiyya ya numfasa kana ya dubi Abbaa yana yi masa nuni da babban mutumin da ke tsakiya me cikar kamala da dattako, wanda Abbaa zai iya cewa dama tun zuwansu yaji mutumin ya cika wurin da haibarsa, kuma yana da tabbacin ƙamshinsa ne ya gauraye dukka wajen tun daga ƙofar gida har cikin gida.
A hankali Baban su Safiyya yace,"Malam Salman wannan shi ne Major Sadiq Oluwa Ibrahim, Yayar Matata ne uwa ɗaya uba ɗaya domin a wurinsa ma na karɓi auren ƙanwarsa, na kusa da shi kuma kusan mahaifi ne a wurinmu sunansa Captain Adebisi Oluwa...waɗannan kuma duk da kake gani abokai ne sai wancan". Ya faɗa yana nuni ma Abbaa da na kusa da shi yace,"Shi ƙane ne a wajen Major, sunansa Alhaji Mukhtar Oluwa".
Abbaa yana ƙara rissinar da kai yace,"To masha Allahu, madallah dukkanku ina ƙara yi muku maraba, ayi haƙuri dai da irin wajen da aka samu".
Captain Adebisi yace,"A haba dai haba dai muma duk irin namu muhallin kenan".
Baban su Safiyya ya ƙara cewa,"To Malam Salman abin da yake tafe da mu muhimmin abu ne, magana ce babba, kuma alkhairi ne ya kawo mu gareka, sai dai bamu san a yanda zaka karɓi al'amarin ba, duba da cewa mun sake dawowa ne a karo na biyu da buƙata iri ɗaya, amma a wannan karan muna fatan samun karɓuwar tayin mu saɓanin baya da bamu samu karɓuwa ba".
Abbaa yace,"To Alhajin Allah a ɗan warware ni ko, an saka ni a duhu". Ya faɗu haƙoransa a waje fuskarsa washe da fara'a.
Major Sadiq wato Sir kamar yanda ƴaƴansa ke kiransa yay nisa tare da numfasawa, yana daɗa kallon fuskar Abbaa da ke kama da ta Sa'ida sak wadda ya gani a cikin jirgi ranar da zasu kaita makaranta, kafin ya fara magana a cikin birkitacciyar hausarsa ta yarabawa yace,"Ammm Malam Salman mun zo wurinka ne a dalilin Yarona, wato dai mun zo nema masa auren ƴarka da ya gani yake so, idan ba'a rigada an tsayar mata da mijin aure ba shi yana da buƙatar aurenta, aure nan kusa ba tare da anja lokaci ba".
Abbaa ya ɗaga kai a karo na biyu yaywa Major kallo na ƙurulla, sai kawai yaji kwarjinin mutumin ya dake shi, haka kuma nauyinsa ya kama shi, yay saurin ɗauke ƙwayar idonsa akansa yana me ƙara sunkuyar da kai ƙasa yace,"Ina sauraronka Ranka shi daɗe".
Major yaci gaba da cewa,"My son Salim na ɗaya daga cikin manema auren ƴarka a shekarun baya masu yawa da suka wuce, to kuma sai ubangiji ya ƙadarta cewa ba zata zama matarsa ba a wancan lokacin, shi ne a wannan karon ya turo mu gare ku da ƙoƙon bararsa yace a taimaka masa idan har wani bai riga shi ba".
Kan Abbaa ya É—aure, kafin ya kalli Baban su Safiyya yace,"Alhajin Allah ni ai har yanzu na kasa shaida É—an namu da kuke magana akai".
Baban su Safiyya yace,"Ehh to da yake a wancan karan ba mune muka zo ba gaskiya, amma ai ba zaka mance yaron da ya kawo kuɗin aure daga baya kuma aka karɓa da cewar ba zai iya jiran yarinya ta kammala karatun da aka ce masa ba, wanda kuma hakan ta faru ne duk ba da son ran zuƙatan kowa ba musamman shi yaron".
Abbaan yayi ƙayattacen murmushi da cewa,"Na tuna, na tuna hakan, to amma shi da yay wancan magana a lokacin baya ai ce na ke an wuce babin...".
Sai yay shiru kamar yanda duk suma suka yi shiru suna kallonsa. Zuciyar Major cike da fargaba da zullumin kar su ƙi amsar tayin su, don shi kansa ya kwaɗaitu wa ɗansa auren Sa'ida.
A lokacin ne kuma aka yi kiran sallar magriba, don haka duk suka miƙe Abbaa ya shiga gida Ummani ta zuba ruwa a buta guda biyu ta ba shi ya fita da ita, ta aika Yasmin wurin Umman su Hindatu ta ƙaro buta aka ƙara musu kafin Abbaan ya dawo ya karɓa masu sallaya, ita dai Ummani ganin yanayinsa na yanda yay sanyi kamar jikinsa ya mutu sai duk ta shiga damuwa da fargaba, tana tayi masa magana ma bai tsaya ya saurareta ba.
Don haka da sauri ta ɗauka waya ta kira Yashaik tace idan yana gida yay sauri ya leƙo gidan.
Ko a wajen sallah ma babu yanda Abbaa bai yi ba akan wani cikin su ya ja su sallar suka dage masa akan lallai shi ne zai ja su, haka yaja su sallar bayan sun idar kuma suka komo soron suka zauna, Abba ya amso fitila a cikin gida ya saka musu saboda soron yayi duhu a lokacin.
Bayan zaman nasu Alhaji Mukhtar yace,"Malam Salman na san kana tunani ne akan abun da ya faru a baya ko, to idan wannn ne kar ka damu, wallahi tallahi ko a baya Salim ba ya janye maganar aurensa da ƴarku ba ne saboda dalilin da aka faɗa, hasalima danne zuciyarsa yay ya haƙura a babu yanda zai yi saboda nuna masa da tayi na bata sonsa, shi kuma bai zai iya auran macen da bata sonsa ba, yana ganin idan ya nace aka yi auren zaman ba zai yi musu daɗi ba, saboda wannan dalilin a lokacin ya zo ya same ni muka yi magana ya faɗa min duk yanda suka yi da yarinya har ma ya fahimci akwai wanda ita take so, amma bai karɓi kuɗinsa don yay wulaƙanci ko tozarci ba, kum ahatta maganar da akayi a lokacin na cewa ya samu wata matar wallahi a lokacin babu wannan zancen anyi hakan ne duk don samun mafita".
Abbaa ya sake jinjina kai kafin yace,"To da wannan da wannan, don bayanin da ka min yanzu shi ne nake so na tambaya. Sai dai duk da haka akwai wani hanzari ba gudu ba, ƴata ba budurwa ba ce yanzu bazawara ce ita, wataƙila kuma bai san da hakan ba ne".