Sashe 62
Ƙayar Ruwa 2&3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummani tayi wani lakato tana dubansa kafin tace,"Amma kuwa banda na san waye mijina wallahi sai in ce mutumin nan siyeka yayi da kuɗi, yanzu tsakani da Allah sai ka bar Babangida ya auri ƴarka? Kenan kaima a wannan shekarun naka tsofe tsofe zaka iya zuwa neman auren ƙaramar yarinya ƴar cikinka ta kusan nawa? Ko da ike zamu ce ta tadda muje".
Abbaa ya buɗe ba ki da mamaki ƙarara yana dubanta yanda duk ta mayar da maganar gaske.
"Ka saki baki kana kallona, to ni dai ba dani za'ai wannan zalunci ba, yarinyata da sauran ƙuruciyarta don tana bazawara ba zai yiwu a laƙaƙa mata auren tsoho ba, daga nan har hizba wallahi, mene wani Babangida daga ya ɗan taimaka mana sai ya wani kwaso ƙafafunsa na marasa kunya yace ya zo neman auren ƴar cikinsa".
Abbaa yace,"Babangida kai tsaye ma babu Alhajin".
"Yo wanne Alhaji bayan ya zubar da girmansa, neman aurar Æ´ar cikinsa fa yake yi kuma daÉ—in abin kunyar ma aminiyar Æ´arsa".
Ganin fa ta haƙiƙance har tana ɗaukan fushi da shi sai mita take yi yace,"Kinga ke ba ki tsaya kin gama jin bayanin da zan miki ba kawai kin hau kan wata maganar, Aure fa ɗan su suka zo nemawa ba kansa ba".
Ƙyam Ummani ta tsaya ko ƙyafta ido babu. "Ɗansa?". Sai kuma ta dawo ta zauna tana cewa,"Kar dai kace min yaron nan Khalid me hankali, ka san ƴaƴansa maza biyu ɗayan kurma ɗayan kuma shi ne lafiyayye".
Abbaa yace,"To ai bama a nasa Æ´aÆ´an ba ne, É—an Yayar matarsa ne yaron nan Salim da suka nemi aurenta tun tana budurwa".
Ummani ta ware ido akansa ƙwaƙwalwarta na auna maganarsa kafin tace,"Wai kana nufin yaron da ya kawo kuɗi suka dawo suka karɓa?".
Abbaa ya jinjina kai yana Faɗin,"Ƙwarai shi fa".
"Abbaa sojan nan fa da kace min babba ne da gwamnatin tarayya yake aiki".
"Shi dai Sa'a".
Nan Abbaa ya shiga bata Labarin duk abunda ya faru tsakaninsa da su Baban Safiyya, Ummani bata jira ƙarashen zancen ba ma ta rangaɗa guɗa a hankali. Ta ɗaga hannu sama tana faɗin,"Allah gatan bawansa, Allah mun gode maka, Allah maji roƙon bawa".
Bakin Abbaa buɗe yake kallonta, mamaki sosai ya kama shi, kar dai abin da ke ransa ne a nata ran itama? Kawai sai yaji tana ƙara faɗin,"Bayan wuya sai daɗi, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, Rabo daga sarkin da ba ya zalunci, bijahi rasulillahi wannan yaron alkhairin Sa'ida ne".
Abbaa yace,"To ke wai kin san yaron nan ne da kike ta farin ciki haka".
"Abbaa ya ba zan yi farin ciki ba, ɗan gidan manya mutane fa, to ni dai wallahi ba don kuɗi ko matsayi ba zaɓin Allah na ke ta nemawa yarinyar nan kuma ina da yaƙinin Salim shi ne Allah ya zaɓo mana, domin kuwa tunda ta fito zaurawa ke ta sintiri akanta ban ji ina farin ciki da zuwan wani ko naji sha'awar ta ƙara yin wani auren ba sai da wannan batu ya afku".
Tayi maganar baki dukka a buÉ—e kamar zai yage saboda murna.
"Yanzu a wacca matsaya ku ka kwana da su? Na san halinka Allah sa suma ba ce kayi su kama gabansu ba, don ni dai ban sani ba Abbaa ko kwaÉ—a Sa'ida zamu yi muci ba".
Yay murmushi yana cewa,"Ba haka ba ne Sa'a, aurenta na baya ne har yanzu abinda ya faru bai gushe min ba, shiyasa na ke ta jin tsoro ban san da wa zan kuma haÉ—ata ba".
"To ya za'ai na faÉ—a maka ba dukka aka taru aka zama É—aya ba, adu'a zamu ta mata ya bata wanda yafi wancan".
"To yanzu dai na ce musu su turo yaron ya same ni zuwa jibi idan Allah ya kaimu saboda bana so a saka wasa a lamarin, sai dai ita É—in bamu sani ba ko ta amince".
"Kai rabu da ita yanzu ai ba shashasha bace da hankalinta ta san inda ke mata ciwo, a bayan ma ƙuruciya ce ta hanata gane wanda ya kamata ta aura".
****"Maman Nana ni zan wuce". Na faɗa a sa'ilin da na ke ɗaukan jakata ƴar ƙarama na riƙe a hannu. Maman Nana tace min,"To Sister Sa'ida sai Allah ya kaimu, ki gaida gida ki gaida su Ummani".
Na amsa mata yayin da Khadija ke tsokanata da cewa,"Wai ke don Allah ko ki É—an gwada soliderity watarana ki ce za ki kwana".
Ina murmushi na ce,"To madam indai za ki bar min albashinki na watanni biyu ni kuma zan dinga haÉ—awa da aikin ki".
"Ehh lallai da ya ke ni bani son kuÉ—in".
Ina dariya kamar yanda kowa yay na ce,"A'a to ke fa kin je saudiya, ni kuma so na ke nayi nayi na kwashe iyayena na kaisu su sauke farali, kinga idan na samu Æ´ar 380 duk wata ai tuni zasu wuce umra".
Maman Nana tace,"To Allah dai ya cika buri, ki yi maza kinga Ummani ta bani amanarki yau kin yi dare".
Nace,"Wallahi fa kinga Yaya Imam É—in ne ma har yanzu bai kira ni ba, É—azu ya kira nace masa Dr yace in tsaya saboda waccan matar da akai wa operation to ina ga ko tunani yake bamu gama ba".
"To ki kira shi mana".
Na ɗan karayar da wuya ina cewa,"Wallahi Maman Nana bana son takura mi shi, komai yake yi yanzu hankalinsa na kaina, Abbaa ne ma yaƙi ya bari na ke komawata ni ɗaya ni banga wani abu a ciki ba".
Suka haÉ—a baki wurin cewa,"Gata ne suka miki wallahi, mace yar tsaro ce sai da kulawa, ki gode Allah da ya ba ki iyayen da idon su yake akan ki".
"To bari naje, ni na manta ma daga yau nayi off ni da shigowa sai laraba".
Khadija da tsokana tace,"Dama kullum ana ba ki na goron albishir ai dole kike son zuwa aiki kullum".
Sauran pure water É—in da ke hannuna na jefa mata.
Da haka na fito daga Nursing station ɗin, Metrom na zaune muka yi sallama da ita, har na fito compound ɗin asibitin sai gata ta biyo ni tana ƙwala min kira da cewa,"Kinga ajiyar ki kin mance nima zan manta kuma".
"Sauri na ke ta yi kinga ƙarfe tara ta kawo kai, na gode".
Wasu hulunan sanyi ne da safuna Sister Hauwa ke siyarwa daga turkey ake kawo mata, shi ne na siya mana ni da Ummani da Safiyya, da yake safunan ma har da na maza sai na siya har Abbaa da Kaka.
Ina tafe zuciyata nata tunanin in kira Yaya Imam ko na ƙyale shi, har dai na fito bakin gate, tunda bai kira ni ba na tabbata wani babban uzurin ne ya riƙe shi, iyaka koƙari suna yi akaina, Abbaa zai rako ni kullum sai mun ci rabin hanya yake komawa, in dai kuma nayi evening to ya sakawa Yayyuna duty yau idan wannan ya ɗauko ni gobe wannan ne zai ɗauko ni.
Ina tsaye bakin gate na buɗe jaka ina laluben wayata sai naji gate man na ce min na matsa za'a wuce. Nayi gefe ce na ke ma ko Dr ne zai tafi sai naga ba motarsa ba ce. Na ɗaga waya na kira Yaya Imam yace,"Kin ganni na taho mashin ɗin nawa ya samu matsala yanzu haka ina wurin masu gyara, kiyi haƙuri gani nan zuwa kin ji".
Nace,"'To Yaya kana ta wajen ina? Na gaji ne wallahi yunwa ma na ke ji".
Yace,"Zan taho yanzu yi haƙuri".
Na kashe wayar ina sanyawa a jaka, na fara tafiyata ni É—aya cikin tsoron da ya fara kama ni, kafin na gama fita a layin ne Allah ya taimake ni na samu me adaidaita sahu na kuwa yi saurin tsayar da shi, na faÉ—a masa inda zai kai ni yace na bayar da É—ari takwas.
Na shiga ina faɗin Allah ya sauke mu lafiya, ban manta da adu'ar zama cikin mota ba, a koƙarinsa na tayar da babur ɗin motar da ke gefenmu tayi masa horn, na ɗan leƙa na kalla sai naga motar da ta fito daga asibiti ce ɗazu.
Mutumin da ke cikin motar ya fito ya ƙaraso yana cewa me adaidaitar,"Ina kayi?".
Yace masa,"Cikin gari nayi can wajen gidan sarki".
Yace,"Ok to nima can É—in nayi motana ne kaga ya samu matsala, samun bakaniken da zai zo ma yanzu aiki ne".
Na ɗan saci ido na kalle shi jin yanda yake hausar gwari, kananun kaya ne jikinsa blue riga me dogon hannu da baƙin wando, yasa bakin gilashi da face mask da sam ba zaka gane fuskarsa ba, zubinsa ma ba na hausawa ba ne duk da fuskarsa a ɓoye take.
Zan fito ya fara shiga sai naji yace,"Noo shige daga ciki".
Na matsa ciki ya shigo, ƙamshin turarensa ya daki hancina sai naji zuciyata ta motsa, kuma ban aune ba na tsinci gabana da faɗuwa sosai, yatsun hannuna har ji nayi suna rawa, sai da muka yi nisa sosai a tafiya kana na kira Yaya Imam nace masa ba sai yaje ba nama taho, ya gama min faɗansa ya kashe wayar.
Ni dai na yita mamakin mutumin ganin bai sauka ba duk da cewa bai faÉ—i inda za'a kai shi ba, muna tafen ma me adaidaitar ke daÉ—a tambayarsa yace masa no worry muje kawai idan anzo inda zan sauka zan faÉ—a maka.
Me adadaitar yake ce masa,"Yallaɓai ko dai baƙo ne kai a garin".
Na jiyo sautin karamin murmushin da yay kawai ba tare da yace komai ba.
Muka iso unguwarmu ina ta ma me adaidaitar kwatance har muka zo ƙofar gida, idona ya hasko min Abbaa tsaye a ƙofar gida hannayensa sarƙe a baya, ban san lokacin da na furta,"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, shikenan na kaɗe".
Mutumin ya juyo yana kallona me adaidaitar ma ya juyo, duk da banga ƙwayar idon da ke cikin gilashi ba na san dai ayar tambaya ce a cikinta dangane da furucin da nayi. Me adaidatar yace,"Hajiya akwai matsala ne?".
Ai kuwa kafin na buÉ—e baki Abbaa ya doka min tsawa da cewa,"Ba za ki fito ba ne".
Abbaa ya buɗe ba ki da mamaki ƙarara yana dubanta yanda duk ta mayar da maganar gaske.
"Ka saki baki kana kallona, to ni dai ba dani za'ai wannan zalunci ba, yarinyata da sauran ƙuruciyarta don tana bazawara ba zai yiwu a laƙaƙa mata auren tsoho ba, daga nan har hizba wallahi, mene wani Babangida daga ya ɗan taimaka mana sai ya wani kwaso ƙafafunsa na marasa kunya yace ya zo neman auren ƴar cikinsa".
Abbaa yace,"Babangida kai tsaye ma babu Alhajin".
"Yo wanne Alhaji bayan ya zubar da girmansa, neman aurar Æ´ar cikinsa fa yake yi kuma daÉ—in abin kunyar ma aminiyar Æ´arsa".
Ganin fa ta haƙiƙance har tana ɗaukan fushi da shi sai mita take yi yace,"Kinga ke ba ki tsaya kin gama jin bayanin da zan miki ba kawai kin hau kan wata maganar, Aure fa ɗan su suka zo nemawa ba kansa ba".
Ƙyam Ummani ta tsaya ko ƙyafta ido babu. "Ɗansa?". Sai kuma ta dawo ta zauna tana cewa,"Kar dai kace min yaron nan Khalid me hankali, ka san ƴaƴansa maza biyu ɗayan kurma ɗayan kuma shi ne lafiyayye".
Abbaa yace,"To ai bama a nasa Æ´aÆ´an ba ne, É—an Yayar matarsa ne yaron nan Salim da suka nemi aurenta tun tana budurwa".
Ummani ta ware ido akansa ƙwaƙwalwarta na auna maganarsa kafin tace,"Wai kana nufin yaron da ya kawo kuɗi suka dawo suka karɓa?".
Abbaa ya jinjina kai yana Faɗin,"Ƙwarai shi fa".
"Abbaa sojan nan fa da kace min babba ne da gwamnatin tarayya yake aiki".
"Shi dai Sa'a".
Nan Abbaa ya shiga bata Labarin duk abunda ya faru tsakaninsa da su Baban Safiyya, Ummani bata jira ƙarashen zancen ba ma ta rangaɗa guɗa a hankali. Ta ɗaga hannu sama tana faɗin,"Allah gatan bawansa, Allah mun gode maka, Allah maji roƙon bawa".
Bakin Abbaa buɗe yake kallonta, mamaki sosai ya kama shi, kar dai abin da ke ransa ne a nata ran itama? Kawai sai yaji tana ƙara faɗin,"Bayan wuya sai daɗi, kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, Rabo daga sarkin da ba ya zalunci, bijahi rasulillahi wannan yaron alkhairin Sa'ida ne".
Abbaa yace,"To ke wai kin san yaron nan ne da kike ta farin ciki haka".
"Abbaa ya ba zan yi farin ciki ba, ɗan gidan manya mutane fa, to ni dai wallahi ba don kuɗi ko matsayi ba zaɓin Allah na ke ta nemawa yarinyar nan kuma ina da yaƙinin Salim shi ne Allah ya zaɓo mana, domin kuwa tunda ta fito zaurawa ke ta sintiri akanta ban ji ina farin ciki da zuwan wani ko naji sha'awar ta ƙara yin wani auren ba sai da wannan batu ya afku".
Tayi maganar baki dukka a buÉ—e kamar zai yage saboda murna.
"Yanzu a wacca matsaya ku ka kwana da su? Na san halinka Allah sa suma ba ce kayi su kama gabansu ba, don ni dai ban sani ba Abbaa ko kwaÉ—a Sa'ida zamu yi muci ba".
Yay murmushi yana cewa,"Ba haka ba ne Sa'a, aurenta na baya ne har yanzu abinda ya faru bai gushe min ba, shiyasa na ke ta jin tsoro ban san da wa zan kuma haÉ—ata ba".
"To ya za'ai na faÉ—a maka ba dukka aka taru aka zama É—aya ba, adu'a zamu ta mata ya bata wanda yafi wancan".
"To yanzu dai na ce musu su turo yaron ya same ni zuwa jibi idan Allah ya kaimu saboda bana so a saka wasa a lamarin, sai dai ita É—in bamu sani ba ko ta amince".
"Kai rabu da ita yanzu ai ba shashasha bace da hankalinta ta san inda ke mata ciwo, a bayan ma ƙuruciya ce ta hanata gane wanda ya kamata ta aura".
****"Maman Nana ni zan wuce". Na faɗa a sa'ilin da na ke ɗaukan jakata ƴar ƙarama na riƙe a hannu. Maman Nana tace min,"To Sister Sa'ida sai Allah ya kaimu, ki gaida gida ki gaida su Ummani".
Na amsa mata yayin da Khadija ke tsokanata da cewa,"Wai ke don Allah ko ki É—an gwada soliderity watarana ki ce za ki kwana".
Ina murmushi na ce,"To madam indai za ki bar min albashinki na watanni biyu ni kuma zan dinga haÉ—awa da aikin ki".
"Ehh lallai da ya ke ni bani son kuÉ—in".
Ina dariya kamar yanda kowa yay na ce,"A'a to ke fa kin je saudiya, ni kuma so na ke nayi nayi na kwashe iyayena na kaisu su sauke farali, kinga idan na samu Æ´ar 380 duk wata ai tuni zasu wuce umra".
Maman Nana tace,"To Allah dai ya cika buri, ki yi maza kinga Ummani ta bani amanarki yau kin yi dare".
Nace,"Wallahi fa kinga Yaya Imam É—in ne ma har yanzu bai kira ni ba, É—azu ya kira nace masa Dr yace in tsaya saboda waccan matar da akai wa operation to ina ga ko tunani yake bamu gama ba".
"To ki kira shi mana".
Na ɗan karayar da wuya ina cewa,"Wallahi Maman Nana bana son takura mi shi, komai yake yi yanzu hankalinsa na kaina, Abbaa ne ma yaƙi ya bari na ke komawata ni ɗaya ni banga wani abu a ciki ba".
Suka haÉ—a baki wurin cewa,"Gata ne suka miki wallahi, mace yar tsaro ce sai da kulawa, ki gode Allah da ya ba ki iyayen da idon su yake akan ki".
"To bari naje, ni na manta ma daga yau nayi off ni da shigowa sai laraba".
Khadija da tsokana tace,"Dama kullum ana ba ki na goron albishir ai dole kike son zuwa aiki kullum".
Sauran pure water É—in da ke hannuna na jefa mata.
Da haka na fito daga Nursing station ɗin, Metrom na zaune muka yi sallama da ita, har na fito compound ɗin asibitin sai gata ta biyo ni tana ƙwala min kira da cewa,"Kinga ajiyar ki kin mance nima zan manta kuma".
"Sauri na ke ta yi kinga ƙarfe tara ta kawo kai, na gode".
Wasu hulunan sanyi ne da safuna Sister Hauwa ke siyarwa daga turkey ake kawo mata, shi ne na siya mana ni da Ummani da Safiyya, da yake safunan ma har da na maza sai na siya har Abbaa da Kaka.
Ina tafe zuciyata nata tunanin in kira Yaya Imam ko na ƙyale shi, har dai na fito bakin gate, tunda bai kira ni ba na tabbata wani babban uzurin ne ya riƙe shi, iyaka koƙari suna yi akaina, Abbaa zai rako ni kullum sai mun ci rabin hanya yake komawa, in dai kuma nayi evening to ya sakawa Yayyuna duty yau idan wannan ya ɗauko ni gobe wannan ne zai ɗauko ni.
Ina tsaye bakin gate na buɗe jaka ina laluben wayata sai naji gate man na ce min na matsa za'a wuce. Nayi gefe ce na ke ma ko Dr ne zai tafi sai naga ba motarsa ba ce. Na ɗaga waya na kira Yaya Imam yace,"Kin ganni na taho mashin ɗin nawa ya samu matsala yanzu haka ina wurin masu gyara, kiyi haƙuri gani nan zuwa kin ji".
Nace,"'To Yaya kana ta wajen ina? Na gaji ne wallahi yunwa ma na ke ji".
Yace,"Zan taho yanzu yi haƙuri".
Na kashe wayar ina sanyawa a jaka, na fara tafiyata ni É—aya cikin tsoron da ya fara kama ni, kafin na gama fita a layin ne Allah ya taimake ni na samu me adaidaita sahu na kuwa yi saurin tsayar da shi, na faÉ—a masa inda zai kai ni yace na bayar da É—ari takwas.
Na shiga ina faɗin Allah ya sauke mu lafiya, ban manta da adu'ar zama cikin mota ba, a koƙarinsa na tayar da babur ɗin motar da ke gefenmu tayi masa horn, na ɗan leƙa na kalla sai naga motar da ta fito daga asibiti ce ɗazu.
Mutumin da ke cikin motar ya fito ya ƙaraso yana cewa me adaidaitar,"Ina kayi?".
Yace masa,"Cikin gari nayi can wajen gidan sarki".
Yace,"Ok to nima can É—in nayi motana ne kaga ya samu matsala, samun bakaniken da zai zo ma yanzu aiki ne".
Na ɗan saci ido na kalle shi jin yanda yake hausar gwari, kananun kaya ne jikinsa blue riga me dogon hannu da baƙin wando, yasa bakin gilashi da face mask da sam ba zaka gane fuskarsa ba, zubinsa ma ba na hausawa ba ne duk da fuskarsa a ɓoye take.
Zan fito ya fara shiga sai naji yace,"Noo shige daga ciki".
Na matsa ciki ya shigo, ƙamshin turarensa ya daki hancina sai naji zuciyata ta motsa, kuma ban aune ba na tsinci gabana da faɗuwa sosai, yatsun hannuna har ji nayi suna rawa, sai da muka yi nisa sosai a tafiya kana na kira Yaya Imam nace masa ba sai yaje ba nama taho, ya gama min faɗansa ya kashe wayar.
Ni dai na yita mamakin mutumin ganin bai sauka ba duk da cewa bai faÉ—i inda za'a kai shi ba, muna tafen ma me adaidaitar ke daÉ—a tambayarsa yace masa no worry muje kawai idan anzo inda zan sauka zan faÉ—a maka.
Me adadaitar yake ce masa,"Yallaɓai ko dai baƙo ne kai a garin".
Na jiyo sautin karamin murmushin da yay kawai ba tare da yace komai ba.
Muka iso unguwarmu ina ta ma me adaidaitar kwatance har muka zo ƙofar gida, idona ya hasko min Abbaa tsaye a ƙofar gida hannayensa sarƙe a baya, ban san lokacin da na furta,"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, shikenan na kaɗe".
Mutumin ya juyo yana kallona me adaidaitar ma ya juyo, duk da banga ƙwayar idon da ke cikin gilashi ba na san dai ayar tambaya ce a cikinta dangane da furucin da nayi. Me adaidatar yace,"Hajiya akwai matsala ne?".
Ai kuwa kafin na buÉ—e baki Abbaa ya doka min tsawa da cewa,"Ba za ki fito ba ne".