Sashe 63
Ƙayar Ruwa 2&3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na haɗiye dunƙulallan yawu, mutumin ya fita nima na fito sai rawar jiki na ke yi, na ciro kuɗi na bawa me adaidaitar na wuce zan iya cewa ina jin yanda ƙwayar ido ta manne a jikina.
Muryar Abbaa tuni ta cika kofar gidan da faɗansa akan tahowar da nayi ni kaɗai, ga layin yay tsit ƙarfe tara da arba'in a lokacin, faɗi yake da uban dare na kamo hanya na taho ina matsayin mace, da ba zan iya jiran Imam ɗin ba me yasa ban kira Yashaik ko Al'amin sun je sun taho da ni ba. Hannu ya kawo zai buge ni nayi saurin shigewa cikin gidan, Ummani ma na tsakar gida na shiga tace,"Ya za ki mana haka, ba dole ayi miki faɗa ba ga wayarki anata faman kira ba ki ɗaga ba".
Idona a waje nace,"Wallahi banji kiran ba na sakata a silent".
Abbaa ya shigo yana ci gaba da faɗin,"Idan kika kuma tahowa ke ɗaya sai ranki yayi mugun ɓaci, kuma faɗa min gidan uban wa kika tafi?".
Jikina ya kama ɓari na shiga wallacewa ina faɗin,"Allah Abbaa babu inda na je".
"Ƙarya kike yi in ba haka ba me ya hana ki ɗaga waya? Kin san Allah zan soke fita aikin nan? Ba dai kin yi karatun ba kin samu na tsira da mutunci, to aikin ba dole ba ne zan hana ki".
Tuni na durƙusa ƙasa hawayen idona na neman sakkowa nace,"Wallahi Abbaa babu inda na je, kayi haƙuri don girman Allah".
Uwa me tausayin ƴaƴanta tuni ta shiga bawa Abbaa haƙuri da tausarsa akan yay ƙasa da murya dare yayi, cikin gida ana jinsa haka maƙota ma duk suna ji. Ya watsa min wani mugun kallo da cewa,"Ba zan ɗauki sakarci irin haka ba, kike jira duk dare za'a zo a ɗauke ki, amma wallahi kika ƙara kuskuren tahowa ke ɗaya daga ranar kin gama aiki".
Yana faɗa ya shige ciki, nima na miƙe na wuce ɗakina, Ummani na leƙowa tace,"Abincinki yana ɗakina".
Ko takalmi ban iya cirewa ba na zauna ina goge hawayena tare da danasanin tahowar da nayi. Ko kayan ban cire ba na tashi na fita zuwa ɗakin Abbaa, sai da na tabbatar ya haƙura ya daina fushin kana nayi masa sallamar sai da safe na wuce ɗakin Ummani na ci abinci.
Wajen sha ɗaya har na rufe ido naji wayata na ringing, da sauri na tashi na rarumota gudun kar Abbaa ya jiyo ƙararta, nifa mahaifina is very strict, bai ƙi ya zo ya ƙwace wayar ba, ban ɗaga ba sai da naga kiran yay yawa har sau uku sannan na ɗaga ana huɗun.
Nayi sallama aka amsa, shiru for some seconds sai aka ce,"Nurse Sa'ida ce?".
Na ce,"Ehh ita ce". Na faÉ—a ina jin muryan kaman na santa duk da cewan muryan namiji ne.
Sai aka ƙara cewa,"Sorry don Allah na kira ki da daddare, ɗazu na zo asibiti ne Dr Samuel yake bani number na ki yace duk sanda na zo na dinga nemanki, domin ke ɗin ƙwararriya ce wacca ta san makamar aikinta".
Babu shakka na san muryar sai dai ba zan ce ga inda na santa ba ko kuma ta wacece ba, a hankali yaci gaba da magana yana ce min yana fama da ciwon baya ne da ƙafa ko zan taimaka na recommending masa maganin da zai sha yanzu kafin zuwa da safe yaje asibiti. Na zage na buɗe murya ina ta kora masa bayani da tambayan ya yake ji, kusan minti goma haka sai naji ya katse ni da tambayan,"Babu dai wani damuwa ko?".
Na ce masa,"A'a babu, duk sanda kake neman taimako irin haka zaka iya kira na".
Sai ya sake cewa,"Thank you so much, but still ba ki cikin wani matsala dai ko?".
With confusion na ce,"Babu komai, kawai na dawo daga aiki ne yanzu na gaji ina so zan yi bacci".
Na faÉ—a ina sauke wayan daga kunnena na kashe bayan ya cika ni da godiya.
Daga can ɓangaren Salim ya sauke ajiyan zuciya, sai yanzu ya samu relief jin muryanta ba cikin yanayi na damuwa ba kamar yanda ya tsammata, kenan babu wata matsala saboda sosai ya damu da yanayin da yaga Abbaa a ɗazu, ya san dole zata sha faɗa kam, don faɗan da Abbaa ya dinga mata a lokacin ji yay kaman ya fito ya ba da haƙuri, shi kansa ji yay ba zai iya barinta ta tafi ita ɗaya ba a wannan daren shiyasa ya aje motarsa ya shiga napep ɗin domin ya san idan yace ta zo ya rage mata hanya ba yarda zata yi ba.
Ya sauke a jiyan zuciyayana aje wayarsa, tare da jingina kai a gadon ta gefen ƙwayar idonsa kuma yana kallon Kudrat da ke gefensa tana bacci.
******Bayan kwana biyu yau tun tashina Ummani tace da na gama komai na gyara ɗakin Al'amin akwai baƙin da za'a yi anjima. Ban tsaya tambayarta ba ni dai ina gama wanke wanke na shiga na gyara tass, na sanya turaran wuta me bala'in ƙamshi da nasa ordarsa daga meduguri. Gidan duka ya ɗauka har Ummansu Hindatu sai da ta leƙo tana faɗin kamar gidan haihuwa ko sabuwar amarya.
Ummani tace na shirya zan rakata unguwa, nayi wanka na saka rigar bubu sai ce tayi lallai sai na sauya in ɗauko abayata da na siya kwanaki mana. Na ce an gama ranki ya daɗe, haka na ɗauko na saka na zauna zaman jiranta sai ƙorafi na ke ina Ummani ki zo mu tafi kin san ba wuri ɗaya kike zuwa ba, an ta shige shige kenan yanzu za ki ga yamma tayi.
Tace kar na dameta in ban rakata Yasmin zata rakata. Ban ƙara magana ba na fito da keken ɗinkina tsakar gida na hau ɗinka kayan wasu da za'a kaiwa bauchi.
Lokacin yaro ya shigo yana cewa ana sallama da Abbaa, na tashi na leƙa ɗakin na faɗa masa, babu jimawa ya fito ya fita, can ya kuma dawowa yace da ni na ɗauko masa tabarma. Da kaina na kai soro na shimfiɗa kana na dawo ciki.
Abbaa ya leƙa daga waje, tsaye ya hangi Salim jingine da motarsa hannayensa harɗe saman ƙirji, cikin kamilalliyar shigarsa ta cofee ɗin yadi da ɗinkin irin na yare, shigarsa tayi masa bala'in kyau.
Abbaa dai murmushi ya suɓuce masa, tun asubahin yau ko kuma yace tun a lokacin da yay sujjada ga ubangiji a cikin dare yana me neman zaɓinsa akan lamarin Salim da Ƴarsa yaji fargaba ya barsa yayin da ƙwarin gwiwan aurama Salim ƴarsa ya shige shi, kuma a yanzu da idanunsa ke kan yaron sai yake jin yana samun salama a cikin ransa dangane da lamarin.
Yaywa Salim izinin shigowa, ya tako cikin tafiyarsa ta namiji me cikar zati da kamala ya shigo soron lokacin Abbaa har ya zauna akan tabarmar, ya cire takalma ya nemi waje ya zauna, zaman nasa ma har sai da Abbaa yace masa tukunna don da tsugunawa yayi cikin jin nauyin zama a inda surukinsa ke zaune.
Ya gurfanar da kansa gaban Abbaa kamar me neman gafara, da girmamawa da ladabi ya sake gaida Abbaa a karo na biyu, Abbaa ya amsa ƙwayar idonsa ƙyam akansa tun a ɗazun.
Abbaa yay nisa tare da sauke numfashi ya kira yi sunansa. "Salim ka ke ko?".
"Ehhh Abaa".
"To ya kake ya aiki?".
"Alhamdulillahi Abbaa, fatan na same ku lafiya".
"Lafiya lau, Salim ko za ki iya faÉ—a min dalilin zuwanka wurina?".
Da wani ƙwarin gwiwa da jarumta irin tasa ta sojan gaske yace,"Abbaa na zo gare ka ne da ƙoƙon baran ka bani amanar rayuwar ƴarka Sa'ida...".
Abbaa ya katse shi,"Amana dai Salim? Ka kuwa san amana?".
"Na sani Abbaa, ni musulmi ne cikakke, kuma ina da yaƙinin zan riƙe amanar shiyasa na ce aba ni ita".
"Salim amana tana da girma, wutar Allah na cin wanda bai riƙeta ba".
"Bana fatan na kasance cikin sahun maciya amana Abbaa, ka yarda da ni zan riƙe amanar da zaka bani tsakani da Allah".
Abbaa ya sake cewa,"Kai ka turo iyayenka kenan ko kuwa sun yi zuwan kan su ne?".
"A'a Abbaa ni naje musu da maganar".
"Amma me yasa baka fara zuwa da kan ka ba? Ko kuma kana ganin kawai don mahaifanka sun zo sai na ce musu na baka ƴata? Shin ka taɓa neman soyayyarta ne?".
Ya ƙara yin ƙasa da kai kafin a hankali yace,"Bamu da ƙarfin ikon da zamu zo kai tsaye mu ce zamu ne abu a bamu ta yanda muke so, na fi so ne a duk sanda wani babban lamari ya shiga gabana na fara saka manyana a ciki, musamman sha'ani me girman gaske irin wannan. Sa'ida kuma ban taɓa tunkararta ba, kawai dai na san da cewa in har iyaye suka amince min na nemi soyayyarta da sannu...".
Sai yay shiru bai iya ƙarasa faɗin abin da zai ce ba. Abbaa yace,"Da sannu me? Yi min bayani ina jinka".
Ya sarƙe yatsunsa da ƙyar ya iya cewa,"In har ta bani dama na shiga sahun manema aurenta da sannu zan koyar da ita so...". Sai kuma ya canja kalamin da cewa,"Da sannu zata aminta da ni".
Abbaa ya jinjina kai sannan yace,"To amma kai da kake da iyali mene naka na son ƙara aure Salim? Ba ku zaman lafiya ne ko kuwa dai lamarin wasu mazan na son wulaƙanta matayen su ne?".
Abbaa yay maganar wajen bugun cikin Salim ɗin. A hankali kuma cikin natsuwa Salim yace,"Babu ko ɗaya Abbaa, ina dai da sha'awan ƙara aure ne domin ko addini ya bamu damar yin hakan, idan har muna da iko kuma zamu yi adalci zamu iya ƙara aure. Sannan zaman lafiya iyaka gwargwado akwai shi tsakanina da iyalina, bani da nufin na ƙara aure don na ci mutuncin iyalina, ba zan ƙara aure don na cutar da wani ɓangaren ba, lamarin aure abinda Allah ya nufa shi ke kasancewa".
[2/2, 07:48] Hlm: *B3ƘR04FT5*
"Masha Allah! Abbaa ya faÉ—a yana jinjina kai.
"Salim da gaske kake kana son Æ´ata tsakaninka da Allah ba domin wata manufa ba?".
Muryar Abbaa tuni ta cika kofar gidan da faɗansa akan tahowar da nayi ni kaɗai, ga layin yay tsit ƙarfe tara da arba'in a lokacin, faɗi yake da uban dare na kamo hanya na taho ina matsayin mace, da ba zan iya jiran Imam ɗin ba me yasa ban kira Yashaik ko Al'amin sun je sun taho da ni ba. Hannu ya kawo zai buge ni nayi saurin shigewa cikin gidan, Ummani ma na tsakar gida na shiga tace,"Ya za ki mana haka, ba dole ayi miki faɗa ba ga wayarki anata faman kira ba ki ɗaga ba".
Idona a waje nace,"Wallahi banji kiran ba na sakata a silent".
Abbaa ya shigo yana ci gaba da faɗin,"Idan kika kuma tahowa ke ɗaya sai ranki yayi mugun ɓaci, kuma faɗa min gidan uban wa kika tafi?".
Jikina ya kama ɓari na shiga wallacewa ina faɗin,"Allah Abbaa babu inda na je".
"Ƙarya kike yi in ba haka ba me ya hana ki ɗaga waya? Kin san Allah zan soke fita aikin nan? Ba dai kin yi karatun ba kin samu na tsira da mutunci, to aikin ba dole ba ne zan hana ki".
Tuni na durƙusa ƙasa hawayen idona na neman sakkowa nace,"Wallahi Abbaa babu inda na je, kayi haƙuri don girman Allah".
Uwa me tausayin ƴaƴanta tuni ta shiga bawa Abbaa haƙuri da tausarsa akan yay ƙasa da murya dare yayi, cikin gida ana jinsa haka maƙota ma duk suna ji. Ya watsa min wani mugun kallo da cewa,"Ba zan ɗauki sakarci irin haka ba, kike jira duk dare za'a zo a ɗauke ki, amma wallahi kika ƙara kuskuren tahowa ke ɗaya daga ranar kin gama aiki".
Yana faɗa ya shige ciki, nima na miƙe na wuce ɗakina, Ummani na leƙowa tace,"Abincinki yana ɗakina".
Ko takalmi ban iya cirewa ba na zauna ina goge hawayena tare da danasanin tahowar da nayi. Ko kayan ban cire ba na tashi na fita zuwa ɗakin Abbaa, sai da na tabbatar ya haƙura ya daina fushin kana nayi masa sallamar sai da safe na wuce ɗakin Ummani na ci abinci.
Wajen sha ɗaya har na rufe ido naji wayata na ringing, da sauri na tashi na rarumota gudun kar Abbaa ya jiyo ƙararta, nifa mahaifina is very strict, bai ƙi ya zo ya ƙwace wayar ba, ban ɗaga ba sai da naga kiran yay yawa har sau uku sannan na ɗaga ana huɗun.
Nayi sallama aka amsa, shiru for some seconds sai aka ce,"Nurse Sa'ida ce?".
Na ce,"Ehh ita ce". Na faÉ—a ina jin muryan kaman na santa duk da cewan muryan namiji ne.
Sai aka ƙara cewa,"Sorry don Allah na kira ki da daddare, ɗazu na zo asibiti ne Dr Samuel yake bani number na ki yace duk sanda na zo na dinga nemanki, domin ke ɗin ƙwararriya ce wacca ta san makamar aikinta".
Babu shakka na san muryar sai dai ba zan ce ga inda na santa ba ko kuma ta wacece ba, a hankali yaci gaba da magana yana ce min yana fama da ciwon baya ne da ƙafa ko zan taimaka na recommending masa maganin da zai sha yanzu kafin zuwa da safe yaje asibiti. Na zage na buɗe murya ina ta kora masa bayani da tambayan ya yake ji, kusan minti goma haka sai naji ya katse ni da tambayan,"Babu dai wani damuwa ko?".
Na ce masa,"A'a babu, duk sanda kake neman taimako irin haka zaka iya kira na".
Sai ya sake cewa,"Thank you so much, but still ba ki cikin wani matsala dai ko?".
With confusion na ce,"Babu komai, kawai na dawo daga aiki ne yanzu na gaji ina so zan yi bacci".
Na faÉ—a ina sauke wayan daga kunnena na kashe bayan ya cika ni da godiya.
Daga can ɓangaren Salim ya sauke ajiyan zuciya, sai yanzu ya samu relief jin muryanta ba cikin yanayi na damuwa ba kamar yanda ya tsammata, kenan babu wata matsala saboda sosai ya damu da yanayin da yaga Abbaa a ɗazu, ya san dole zata sha faɗa kam, don faɗan da Abbaa ya dinga mata a lokacin ji yay kaman ya fito ya ba da haƙuri, shi kansa ji yay ba zai iya barinta ta tafi ita ɗaya ba a wannan daren shiyasa ya aje motarsa ya shiga napep ɗin domin ya san idan yace ta zo ya rage mata hanya ba yarda zata yi ba.
Ya sauke a jiyan zuciyayana aje wayarsa, tare da jingina kai a gadon ta gefen ƙwayar idonsa kuma yana kallon Kudrat da ke gefensa tana bacci.
******Bayan kwana biyu yau tun tashina Ummani tace da na gama komai na gyara ɗakin Al'amin akwai baƙin da za'a yi anjima. Ban tsaya tambayarta ba ni dai ina gama wanke wanke na shiga na gyara tass, na sanya turaran wuta me bala'in ƙamshi da nasa ordarsa daga meduguri. Gidan duka ya ɗauka har Ummansu Hindatu sai da ta leƙo tana faɗin kamar gidan haihuwa ko sabuwar amarya.
Ummani tace na shirya zan rakata unguwa, nayi wanka na saka rigar bubu sai ce tayi lallai sai na sauya in ɗauko abayata da na siya kwanaki mana. Na ce an gama ranki ya daɗe, haka na ɗauko na saka na zauna zaman jiranta sai ƙorafi na ke ina Ummani ki zo mu tafi kin san ba wuri ɗaya kike zuwa ba, an ta shige shige kenan yanzu za ki ga yamma tayi.
Tace kar na dameta in ban rakata Yasmin zata rakata. Ban ƙara magana ba na fito da keken ɗinkina tsakar gida na hau ɗinka kayan wasu da za'a kaiwa bauchi.
Lokacin yaro ya shigo yana cewa ana sallama da Abbaa, na tashi na leƙa ɗakin na faɗa masa, babu jimawa ya fito ya fita, can ya kuma dawowa yace da ni na ɗauko masa tabarma. Da kaina na kai soro na shimfiɗa kana na dawo ciki.
Abbaa ya leƙa daga waje, tsaye ya hangi Salim jingine da motarsa hannayensa harɗe saman ƙirji, cikin kamilalliyar shigarsa ta cofee ɗin yadi da ɗinkin irin na yare, shigarsa tayi masa bala'in kyau.
Abbaa dai murmushi ya suɓuce masa, tun asubahin yau ko kuma yace tun a lokacin da yay sujjada ga ubangiji a cikin dare yana me neman zaɓinsa akan lamarin Salim da Ƴarsa yaji fargaba ya barsa yayin da ƙwarin gwiwan aurama Salim ƴarsa ya shige shi, kuma a yanzu da idanunsa ke kan yaron sai yake jin yana samun salama a cikin ransa dangane da lamarin.
Yaywa Salim izinin shigowa, ya tako cikin tafiyarsa ta namiji me cikar zati da kamala ya shigo soron lokacin Abbaa har ya zauna akan tabarmar, ya cire takalma ya nemi waje ya zauna, zaman nasa ma har sai da Abbaa yace masa tukunna don da tsugunawa yayi cikin jin nauyin zama a inda surukinsa ke zaune.
Ya gurfanar da kansa gaban Abbaa kamar me neman gafara, da girmamawa da ladabi ya sake gaida Abbaa a karo na biyu, Abbaa ya amsa ƙwayar idonsa ƙyam akansa tun a ɗazun.
Abbaa yay nisa tare da sauke numfashi ya kira yi sunansa. "Salim ka ke ko?".
"Ehhh Abaa".
"To ya kake ya aiki?".
"Alhamdulillahi Abbaa, fatan na same ku lafiya".
"Lafiya lau, Salim ko za ki iya faÉ—a min dalilin zuwanka wurina?".
Da wani ƙwarin gwiwa da jarumta irin tasa ta sojan gaske yace,"Abbaa na zo gare ka ne da ƙoƙon baran ka bani amanar rayuwar ƴarka Sa'ida...".
Abbaa ya katse shi,"Amana dai Salim? Ka kuwa san amana?".
"Na sani Abbaa, ni musulmi ne cikakke, kuma ina da yaƙinin zan riƙe amanar shiyasa na ce aba ni ita".
"Salim amana tana da girma, wutar Allah na cin wanda bai riƙeta ba".
"Bana fatan na kasance cikin sahun maciya amana Abbaa, ka yarda da ni zan riƙe amanar da zaka bani tsakani da Allah".
Abbaa ya sake cewa,"Kai ka turo iyayenka kenan ko kuwa sun yi zuwan kan su ne?".
"A'a Abbaa ni naje musu da maganar".
"Amma me yasa baka fara zuwa da kan ka ba? Ko kuma kana ganin kawai don mahaifanka sun zo sai na ce musu na baka ƴata? Shin ka taɓa neman soyayyarta ne?".
Ya ƙara yin ƙasa da kai kafin a hankali yace,"Bamu da ƙarfin ikon da zamu zo kai tsaye mu ce zamu ne abu a bamu ta yanda muke so, na fi so ne a duk sanda wani babban lamari ya shiga gabana na fara saka manyana a ciki, musamman sha'ani me girman gaske irin wannan. Sa'ida kuma ban taɓa tunkararta ba, kawai dai na san da cewa in har iyaye suka amince min na nemi soyayyarta da sannu...".
Sai yay shiru bai iya ƙarasa faɗin abin da zai ce ba. Abbaa yace,"Da sannu me? Yi min bayani ina jinka".
Ya sarƙe yatsunsa da ƙyar ya iya cewa,"In har ta bani dama na shiga sahun manema aurenta da sannu zan koyar da ita so...". Sai kuma ya canja kalamin da cewa,"Da sannu zata aminta da ni".
Abbaa ya jinjina kai sannan yace,"To amma kai da kake da iyali mene naka na son ƙara aure Salim? Ba ku zaman lafiya ne ko kuwa dai lamarin wasu mazan na son wulaƙanta matayen su ne?".
Abbaa yay maganar wajen bugun cikin Salim ɗin. A hankali kuma cikin natsuwa Salim yace,"Babu ko ɗaya Abbaa, ina dai da sha'awan ƙara aure ne domin ko addini ya bamu damar yin hakan, idan har muna da iko kuma zamu yi adalci zamu iya ƙara aure. Sannan zaman lafiya iyaka gwargwado akwai shi tsakanina da iyalina, bani da nufin na ƙara aure don na ci mutuncin iyalina, ba zan ƙara aure don na cutar da wani ɓangaren ba, lamarin aure abinda Allah ya nufa shi ke kasancewa".
[2/2, 07:48] Hlm: *B3ƘR04FT5*
"Masha Allah! Abbaa ya faÉ—a yana jinjina kai.
"Salim da gaske kake kana son Æ´ata tsakaninka da Allah ba domin wata manufa ba?".