Sashe 63
Abinda Ke Cikin Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Na farko an samu shaidar mutane kusan arba'in wanda daga ciki har da makusanta Maimartaba, sannan dukkanin gawarwakin mutanen an same su ne a wani dakin sirri na Maimartaba din, wanda babu wanda yake shiga wajen sai shi Sarkin shi kad'ai."
"Hmm..." Wadda ake bawa labarin taja doguwar ajiyar zuciya
"Bayan nan me ya faru?"
"Bayan nan komai ya kare, mutanen wannan Masarautar da kansu suka yi wa Sarki da Gimbiya korar kare, korar da ba'a taba yiwa ko da bawa bane irin sa balle Sarki, sai dai babu al'ummar da zasu kama Sarkin da ya kasance shugaba a gare su da wannan laifin su kyale ba."
"Kina nufin tun ranar babu wanda ya sake jin labarin Sarkin da gimbiyar?"
"Babu wanda ya sake ji?"
"Toh amma ya akayi kika samu kanki anan? Ina jariran ya akayi dasu?"
Kuka ta saka sosai ta kasa magana, tana tuna yadda komai ya kasance bayan ta basu yardar ta, ashe Amfani Kawai sukayi da ita don cimma manufar su.
"Da kansa Sarki Usman ya dauki yaran ya damka su a hannu na, ya kuma umarce ni da na tafi, nayi nisa da kowa na fara sabuwar rayuwa. Ya kuma gargade ni da kar na kuskura na dawo komai runtsi. Nayi abinda yace na dauki yaran da Yabi da nufin barin Masarautar. A hanyar mu ta tafiya ne muka hadu da wani me suna Mahdi, ya tsaidamu sannan ya umarce mu da mu zo ya kaimu inda zamu zauna xuwa gobe saboda kar mu tafi yanzu dare yayi mana, muka yarda dashi ya kaimu wani gida. Cikin dare muna kwance naji kamar kakarin mutum, na tashi da sauri na haska yar karamar fitilar, Yabi na gani a kwance tana kakarin mutuwa, da sauri na yi kanta ina kiran sunanta, bata iya amsawa ba sai dai ta dauki hannu na ta saka wani abu a ciki, ta dan hasken na kalla sai naga zobe me me tsananin haske, muryar ta na fita da k'yar tace
"Ki dauki yaran ku gudu, zasu kashe su."
"Su waye zasu kashe su? Me mukayi musu?" Na hau tambayar ta ina kuka sosai ganin yadda cikin ta ke fidda jini.
"Karki bata lokaci Aminatu, kiyi hakuri ba zan rayu ba, amma duk yadda zakiyi ki tabbatar yaran sun rayu, ki tabbatar sun kai lokacin da ya kamata su kai."
Tashi nayi da sauri jin motsin an taba kofa, nayi kan yaran na dauke su na yi saurin neman hanyar da zan gudu, window na kalla naga tsawon ba zai yiwu na iya hawa ba, na dawo ciki ina kuka Ina tunanin yadda zanyi na tseratar da yaran ko da ni bazan rayu ba. Da sauri na shinfida mayafi na wanda ya kasance babba kuma me kauri na daure su a ciki na bar musu yar hanyar da zasu sha iska. Daga chan gefe na hangi wata igiya, ba tare da dogon nazari ba na jawo igiyar na daura ta a jikin mayafin nawa,sannan nayi wajen window na leka naga iya zurfin wajen, nayi addu'a sannan na zura su ta window Ina jan igiyar hankali na a tashe duk yadda ake buga kofar wadda sai a sannan na gane Yabi rufe kofar tayi. Kamar an rik'e igiyar haka naji, na kama tagar na leka,sai naga inuwar mutum a tsaye a wajen, ban iya tantance mace ko namiji ba a lokacin sai da ta juya don barin wajen da mugun sauri, ina kallo ta kwance igiyar daka jiki ta rungume su tsam a jikinta, sannan cikin dakikun da basu wuce uku ba ta bace wa gani na, a daidai lokacin suka balla kofar suka shigo, a kuma lokacin ne zoben dake hannu na ya subuce ya fad'i, naji karar faduwar sa nayi saurin durkushewa a wajen na hau lalubawa, 'bari daya hannu na ya samu nasarar dauka, na dunkule shi ina mamakin yadda akayi zoben ya rabe."
"Tun daga ranar, na cinci kaina a cikin wannan wajen da ban taba saka ran fita ba, na rasa kakata a ranar, na rasa yarana."
"Lallai kin fuskanci abubuwa masu yawan gaske, sai dai Ina miki albishir da kwanakin da suka rage miki anan kad'an ne."
"Ta yaya zan fita daga gidan nan?"
"Allah ne zai yi ikon sa akan Azzalumai."
Rano
[5/20, 9:05 AM] Maman Maryam: Hafsat Rano
Page 27
***Kasancewar Gate din a bud'e yake ya basu damar ganin duk shige da fitan dake faruwa tsakanin gidajen biyu, Afrah ce ta matsa mata akan lallai sai sun fito compound din sunyi hoto, suna tsaye suna hotunan ta hangi fitowar sa daga gidan nasu, hankalin ta, ta tattara gaba daya tana kallon sanda yayi wajen motar sa. Tana tsaye jikin kofar da zai shiga motar, ta zubo da attachment din dake kanta yazo fiye da rabin bayan ta, sai kuma ta daura dan siririn dankwali a saman gashin, riga da skirt ne a jikin ta sai dai zaka rantse da Allah fitted gown ce yadda suka bi suka tafi da tsarin jikinta, kamar dama chan tare da jikin nata a ka yi su.
"Who's she?" Ta zunguri Afrah tana nuna mata Umaimah dake tsaye suna magana da Sultan din ta, duk da bata ji me suke cewa ba amma sai taji ranta ya sosu, ko dan ganin yanayin yarinyar, duk kuwa da zaman ta a k'asar turai amma zata iya banbance tsakanin me tarbiyya da mara shi.
"Wace ita?" Ta sake tambayar Afrah
"Wata lowclass girl ce, sanda muka zo da Abba itama tazo hutu gidan Mah-Mah, kamar ko niece din Mah-Mah ce a yadda naji, ta fiya jin kanta shiyasa ni sam bata min ba, sannan naga alamu da take taken ta, ya sultan take so."
"Ok yayi." Ta amsa a dakile, gaba d'aya sai taji hoton ya fita kanta, ta kasa dauke ido daga kansu har sai da ta ga SULTAN din ya shiga mota ya tafi, ita kuma ta juya zuwa cikin gidan, fuskar ta dauke da murmushin da ta barwa Amrah tunanin murmushiin menene?
"Karma ki bata lokacin ki akan irin wannan tsohuwar."
"Ba zaki gane ba Afrah, irin su zasu iya yin komai domin samun abinda suke so."
"Ya Sultan baya son ta, ba kuma zai taba son ta ba nasan, kalle ta fa kamar wata masara babu kyawun gani."
"Ke kike ganin haka."
"Comman, karki bata ranar ki da kanki da tunanin abinda ba me yiwu wa bane."
"Naji...Mu koma ciki Toh."
Ciki suka shiga still Afrah na cigaba da son ganin tayi convincing dinta ta kuma nuna mata dole sai ta yi shining idon ta, idan ta tsaya sanyi da salo salo sai dai taji anayi ba ita, dan yanzu mata akan namiji babu abinda ba zasu iya ba to win him over.
***Hannun sa daya na saman steering, daya kuma yana rik'e da wayar sa wadda yake kokarin kiran numbers din da yazo ya tarar da misscalls bayan barin wayar ta da yayi a mota ta kwana, jiya da ya dawo gidan be shiga da komai ba, abincin da ya tsaya yayi order ya dauka kawai shima kuma chacchakala kawai yayi ya rufe shi yayi kwanciyar sa. Bin kiran ya fara yi daya bayan daya wanda yawanci na abokan su ne sai yan asibiti. Yana gamawa dasu ya nemo number Amrah zai kira ta kiran mai gadin gidan Alhaji Safiyanu Madaki ya shigo, be daga ba sai da ta gama ringing sanñan yabi kiran.
"Hello..."
"Nine Sultan, na kikkiraka da layi na baka daga ba, idan ka samu lokaci kazo gida akwai maganar da nake so na fad'a maka."
"Ina wani abu me muhimmanci ne, maganar ba zata yiwu a waya ba?"
"Eh gaskiya."
"Shikenan zanzo."
Ya katse kiran be jira amsar sa ba, ya rasa me yasa kawai yake jin haushin Alhaji Safiyanu, ko dan tunanin da yake akansa na son Amfani dashi domin cimma manufar sa ne yasa hakan? Ko kuma dai akwai dalili? Ba zai dai taba bari yayi amfani dashi ba for his selfish interest.
Jujjuya wayar take a hannun ta, zuciyar ta duk babu dadi, a zaton ta zai dawo bayan tafiyar tasa jiya, ko da bazata tare ba ya kamata ya dawo ya ganta kafin ya kwanta, kuma ta kirashi sau biyu be daga ba be kuma biyo kiran ba, duk sai taji ta damu da hakan, har sai da damuwar ta nuna a cikin yanayin ta.
Wayar ce tayi kara, har ta dan tsorata dan bata yi zato ba, ta kalli sunan me kiran tana sake bata fuskar ta alamun tayi fushi kamar yana gabanta. Sai da ta kusa tsinkewa sannan ta d'aga muryar ta a chunkushe tace
"Hello?"
"Assalamu alaikum."
"Wa alaikasalam, goodmorning."
"Morning my wife, kin tashi lafiya?"
"Lafiya Lou."
"Ya naji ki haka haka? Are you ok?"
"Umm."
"Toh waye ya taba min ke? Umm? Tell me, adunanu ne ko afiruwa?"
"You, you, you."
"Ni kuma? Me nayi ni kuma? Bawan Allah."
"Baka dawo jiya ba, na kira no answer, kuma baka kira back ba sai yanzu."
"God! I'm so sorry kinji,wallahi jiyan nan ba zaki gane ba, anyway gani a kofar gida, kizo dakin Adnan sai muyi magana."
"Ok." Tace tayi hanging kiran ta tashi da sauri, sabuwar atamfar dake jikin ta wadda akayi ma dinkin simple gown ta sake dubawa, tayi mata kyau sosai ta karbi kalar fatar ta, dan lip balm ta shafa ta sake fesa turare ta fito,a falo ta ga Amrah da sauran bakin da basu tafi ba taja hannun ta suka fito.
"Rakani dan Allah."
"Ina kuma?"
"Ya Sultan ne yake dakin ya Adnan."
Da sauri Afrah ta kwace hannun ta tana ja baya.
"Wallahi ba zan je ba, an gaya miki wai ana raka mata ne wajen mijin ta, kiji ki da wani zance."
"Haba Afrah, dan Allah ki rakani."
"Kai you most be kidding me, yasin ban zuwa, zan iya kaiki bakin boarder dai, daga nan sai na yo kwana na barki ki karasa."
"Bakin boarder kuma?"
"Eh mana, iya kata bakin dakin."
"Muje naji." Tace tana sake jan hannun ta. Suna zuwa kofar dakin Afrah ta warce hannun ta, ta yi tafiyar ta tana mata dariyar mugunta.
"Hmm..." Wadda ake bawa labarin taja doguwar ajiyar zuciya
"Bayan nan me ya faru?"
"Bayan nan komai ya kare, mutanen wannan Masarautar da kansu suka yi wa Sarki da Gimbiya korar kare, korar da ba'a taba yiwa ko da bawa bane irin sa balle Sarki, sai dai babu al'ummar da zasu kama Sarkin da ya kasance shugaba a gare su da wannan laifin su kyale ba."
"Kina nufin tun ranar babu wanda ya sake jin labarin Sarkin da gimbiyar?"
"Babu wanda ya sake ji?"
"Toh amma ya akayi kika samu kanki anan? Ina jariran ya akayi dasu?"
Kuka ta saka sosai ta kasa magana, tana tuna yadda komai ya kasance bayan ta basu yardar ta, ashe Amfani Kawai sukayi da ita don cimma manufar su.
"Da kansa Sarki Usman ya dauki yaran ya damka su a hannu na, ya kuma umarce ni da na tafi, nayi nisa da kowa na fara sabuwar rayuwa. Ya kuma gargade ni da kar na kuskura na dawo komai runtsi. Nayi abinda yace na dauki yaran da Yabi da nufin barin Masarautar. A hanyar mu ta tafiya ne muka hadu da wani me suna Mahdi, ya tsaidamu sannan ya umarce mu da mu zo ya kaimu inda zamu zauna xuwa gobe saboda kar mu tafi yanzu dare yayi mana, muka yarda dashi ya kaimu wani gida. Cikin dare muna kwance naji kamar kakarin mutum, na tashi da sauri na haska yar karamar fitilar, Yabi na gani a kwance tana kakarin mutuwa, da sauri na yi kanta ina kiran sunanta, bata iya amsawa ba sai dai ta dauki hannu na ta saka wani abu a ciki, ta dan hasken na kalla sai naga zobe me me tsananin haske, muryar ta na fita da k'yar tace
"Ki dauki yaran ku gudu, zasu kashe su."
"Su waye zasu kashe su? Me mukayi musu?" Na hau tambayar ta ina kuka sosai ganin yadda cikin ta ke fidda jini.
"Karki bata lokaci Aminatu, kiyi hakuri ba zan rayu ba, amma duk yadda zakiyi ki tabbatar yaran sun rayu, ki tabbatar sun kai lokacin da ya kamata su kai."
Tashi nayi da sauri jin motsin an taba kofa, nayi kan yaran na dauke su na yi saurin neman hanyar da zan gudu, window na kalla naga tsawon ba zai yiwu na iya hawa ba, na dawo ciki ina kuka Ina tunanin yadda zanyi na tseratar da yaran ko da ni bazan rayu ba. Da sauri na shinfida mayafi na wanda ya kasance babba kuma me kauri na daure su a ciki na bar musu yar hanyar da zasu sha iska. Daga chan gefe na hangi wata igiya, ba tare da dogon nazari ba na jawo igiyar na daura ta a jikin mayafin nawa,sannan nayi wajen window na leka naga iya zurfin wajen, nayi addu'a sannan na zura su ta window Ina jan igiyar hankali na a tashe duk yadda ake buga kofar wadda sai a sannan na gane Yabi rufe kofar tayi. Kamar an rik'e igiyar haka naji, na kama tagar na leka,sai naga inuwar mutum a tsaye a wajen, ban iya tantance mace ko namiji ba a lokacin sai da ta juya don barin wajen da mugun sauri, ina kallo ta kwance igiyar daka jiki ta rungume su tsam a jikinta, sannan cikin dakikun da basu wuce uku ba ta bace wa gani na, a daidai lokacin suka balla kofar suka shigo, a kuma lokacin ne zoben dake hannu na ya subuce ya fad'i, naji karar faduwar sa nayi saurin durkushewa a wajen na hau lalubawa, 'bari daya hannu na ya samu nasarar dauka, na dunkule shi ina mamakin yadda akayi zoben ya rabe."
"Tun daga ranar, na cinci kaina a cikin wannan wajen da ban taba saka ran fita ba, na rasa kakata a ranar, na rasa yarana."
"Lallai kin fuskanci abubuwa masu yawan gaske, sai dai Ina miki albishir da kwanakin da suka rage miki anan kad'an ne."
"Ta yaya zan fita daga gidan nan?"
"Allah ne zai yi ikon sa akan Azzalumai."
Rano
[5/20, 9:05 AM] Maman Maryam: Hafsat Rano
Page 27
***Kasancewar Gate din a bud'e yake ya basu damar ganin duk shige da fitan dake faruwa tsakanin gidajen biyu, Afrah ce ta matsa mata akan lallai sai sun fito compound din sunyi hoto, suna tsaye suna hotunan ta hangi fitowar sa daga gidan nasu, hankalin ta, ta tattara gaba daya tana kallon sanda yayi wajen motar sa. Tana tsaye jikin kofar da zai shiga motar, ta zubo da attachment din dake kanta yazo fiye da rabin bayan ta, sai kuma ta daura dan siririn dankwali a saman gashin, riga da skirt ne a jikin ta sai dai zaka rantse da Allah fitted gown ce yadda suka bi suka tafi da tsarin jikinta, kamar dama chan tare da jikin nata a ka yi su.
"Who's she?" Ta zunguri Afrah tana nuna mata Umaimah dake tsaye suna magana da Sultan din ta, duk da bata ji me suke cewa ba amma sai taji ranta ya sosu, ko dan ganin yanayin yarinyar, duk kuwa da zaman ta a k'asar turai amma zata iya banbance tsakanin me tarbiyya da mara shi.
"Wace ita?" Ta sake tambayar Afrah
"Wata lowclass girl ce, sanda muka zo da Abba itama tazo hutu gidan Mah-Mah, kamar ko niece din Mah-Mah ce a yadda naji, ta fiya jin kanta shiyasa ni sam bata min ba, sannan naga alamu da take taken ta, ya sultan take so."
"Ok yayi." Ta amsa a dakile, gaba d'aya sai taji hoton ya fita kanta, ta kasa dauke ido daga kansu har sai da ta ga SULTAN din ya shiga mota ya tafi, ita kuma ta juya zuwa cikin gidan, fuskar ta dauke da murmushin da ta barwa Amrah tunanin murmushiin menene?
"Karma ki bata lokacin ki akan irin wannan tsohuwar."
"Ba zaki gane ba Afrah, irin su zasu iya yin komai domin samun abinda suke so."
"Ya Sultan baya son ta, ba kuma zai taba son ta ba nasan, kalle ta fa kamar wata masara babu kyawun gani."
"Ke kike ganin haka."
"Comman, karki bata ranar ki da kanki da tunanin abinda ba me yiwu wa bane."
"Naji...Mu koma ciki Toh."
Ciki suka shiga still Afrah na cigaba da son ganin tayi convincing dinta ta kuma nuna mata dole sai ta yi shining idon ta, idan ta tsaya sanyi da salo salo sai dai taji anayi ba ita, dan yanzu mata akan namiji babu abinda ba zasu iya ba to win him over.
***Hannun sa daya na saman steering, daya kuma yana rik'e da wayar sa wadda yake kokarin kiran numbers din da yazo ya tarar da misscalls bayan barin wayar ta da yayi a mota ta kwana, jiya da ya dawo gidan be shiga da komai ba, abincin da ya tsaya yayi order ya dauka kawai shima kuma chacchakala kawai yayi ya rufe shi yayi kwanciyar sa. Bin kiran ya fara yi daya bayan daya wanda yawanci na abokan su ne sai yan asibiti. Yana gamawa dasu ya nemo number Amrah zai kira ta kiran mai gadin gidan Alhaji Safiyanu Madaki ya shigo, be daga ba sai da ta gama ringing sanñan yabi kiran.
"Hello..."
"Nine Sultan, na kikkiraka da layi na baka daga ba, idan ka samu lokaci kazo gida akwai maganar da nake so na fad'a maka."
"Ina wani abu me muhimmanci ne, maganar ba zata yiwu a waya ba?"
"Eh gaskiya."
"Shikenan zanzo."
Ya katse kiran be jira amsar sa ba, ya rasa me yasa kawai yake jin haushin Alhaji Safiyanu, ko dan tunanin da yake akansa na son Amfani dashi domin cimma manufar sa ne yasa hakan? Ko kuma dai akwai dalili? Ba zai dai taba bari yayi amfani dashi ba for his selfish interest.
Jujjuya wayar take a hannun ta, zuciyar ta duk babu dadi, a zaton ta zai dawo bayan tafiyar tasa jiya, ko da bazata tare ba ya kamata ya dawo ya ganta kafin ya kwanta, kuma ta kirashi sau biyu be daga ba be kuma biyo kiran ba, duk sai taji ta damu da hakan, har sai da damuwar ta nuna a cikin yanayin ta.
Wayar ce tayi kara, har ta dan tsorata dan bata yi zato ba, ta kalli sunan me kiran tana sake bata fuskar ta alamun tayi fushi kamar yana gabanta. Sai da ta kusa tsinkewa sannan ta d'aga muryar ta a chunkushe tace
"Hello?"
"Assalamu alaikum."
"Wa alaikasalam, goodmorning."
"Morning my wife, kin tashi lafiya?"
"Lafiya Lou."
"Ya naji ki haka haka? Are you ok?"
"Umm."
"Toh waye ya taba min ke? Umm? Tell me, adunanu ne ko afiruwa?"
"You, you, you."
"Ni kuma? Me nayi ni kuma? Bawan Allah."
"Baka dawo jiya ba, na kira no answer, kuma baka kira back ba sai yanzu."
"God! I'm so sorry kinji,wallahi jiyan nan ba zaki gane ba, anyway gani a kofar gida, kizo dakin Adnan sai muyi magana."
"Ok." Tace tayi hanging kiran ta tashi da sauri, sabuwar atamfar dake jikin ta wadda akayi ma dinkin simple gown ta sake dubawa, tayi mata kyau sosai ta karbi kalar fatar ta, dan lip balm ta shafa ta sake fesa turare ta fito,a falo ta ga Amrah da sauran bakin da basu tafi ba taja hannun ta suka fito.
"Rakani dan Allah."
"Ina kuma?"
"Ya Sultan ne yake dakin ya Adnan."
Da sauri Afrah ta kwace hannun ta tana ja baya.
"Wallahi ba zan je ba, an gaya miki wai ana raka mata ne wajen mijin ta, kiji ki da wani zance."
"Haba Afrah, dan Allah ki rakani."
"Kai you most be kidding me, yasin ban zuwa, zan iya kaiki bakin boarder dai, daga nan sai na yo kwana na barki ki karasa."
"Bakin boarder kuma?"
"Eh mana, iya kata bakin dakin."
"Muje naji." Tace tana sake jan hannun ta. Suna zuwa kofar dakin Afrah ta warce hannun ta, ta yi tafiyar ta tana mata dariyar mugunta.