Sashe 35
Abinda Ke Cikin Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda Kawu daddy yace zamu yi magana daren ranar ban runtsa ba har wayewar gari. Kasan cewar asabar ce, Ina malale akan gado gaba na sai dukan uku-uku yake. Shin akan me zamu tattauna? Nasan tabbas lefi nayi. Kuma duk yadda akai akan bana bari TK ya dakko ni wani lokacin idan na fita. Ko kuma su Mami ne suka qulla min qullalliya a gurinsa? Ko kuma zancen iyayen Mas'oud zai min kila yace nace ya turo. Ganin sha biyu ta kusa ban ci abincin safe ba hakan yasa na diro daga gado ina mika, Band’aki na shige nayo wanka na canza kaya cikin doguwar rigar A line marar shape. Na taje kai na dakyar saboda inayi yana zamewa saboda santsi da cikar sa, Na d’aure da ribbon. Dauri me sauki nayi na shafa man baki na sauka kasa. A dinning area na tarar da Mami dasu Ya Shukrah suna cin abinci suna hira.
“Mami ina kwana..? An tashi lapia.”
“Lapia lou..” Ta bani amsa a tak’aice tana mai cigaba da kurbar tea dinta.
“Ya Shukra ina kwana? Ya Hameeda ina kwana.”
Kowannen su ya amsa babu yabo babu fallasa. Ganin haka na mike na daddebi abinda zan ci a plate na koma k’arshen parlorn nakeci acan. Sai bayan na kammala ina zaune ina karanta wani book na wajen aiki sai ga Kawu daddy yafito. Sanye cikin jallabiya.
“Kawu daddy...Barka da safiya Kawu daddy! An tashi lapia?”
“Alhamdulillah Khadija.. Muje ko?”
“Toh Kawu..”
Su Mami suka bimu da kallo, Yana gaba ina biye da shi ya shiga parlorn sa ya zauna akan babbar kujera ni kuma na tsakure a gefe,
“Hau kujera ki zauna mana.”
“Nan ya isa Kawu....”
Gyaran murya yai. Ya rage volume din CNN dake faman yi,
“Kafin dai mu fara magana ina son tabbatarwa kai na Kamar yadda kika sani, wannan maganar da muka yi dake a baya na aure ita ce ta kuma tasowa. Amman Shin ki na da saurayi ne dake zuwa neman ki gidan nan? Kai bama wannan ba. Akwai wanda ya taba yi miki zancen aure? Dan ni dai nasan da akwai zan sani ko kuwa..? Dan naje munyi magana da dangin mahaifinki, sun kuma bar min komai a hannuna cewar na yi komai da komai a game da auranki.”
Wani daskararren abu naji ya tokare min a wuya. Shin menene yake shirin faruwa dani.? Ko wani sharrin aka kullamin?
“Magana nake miki Khadija kin yi shiru...”
“Kawu daddy.. Ba.. babu!” Na samu kai na da bashi amsa haka! Kawu daddy ya sake yin shiru na dan wani lokacin kafin yace,
“Tun wannan dai wanda nazo nace miki na yaba da hankali da tunaninsa, gashi kai tsaye ni ya nema kinga kenan da gaske yake yi ko?”
Sake samun Kai na nayi da kada kai. To me zance? Shi kansa Mas’oud din yana namiji ya boye alakar mu bare ni Mace?
“Toh shikenan! Alhamdulillah tunda babu wata magana tsakanin ku da wani. Kinsan babu kyau neman aure akan aure. Wannan yaro me hankali da dattako ne, ya fito daga gidan mutunci. Yana neman auren ki.. Kuma azahirin gaskia ma nace na bashi. Saboda ko da kina da wanda kike so din a matsayina na mahaifi agare ki. Babu wanda ya zo ya same ni. Manya basu shigo ciki ba, Dama already blood sample/genotype dinki sunyi kyau. Kowa zaki iya aura, Kuma Khadija...”
Ai bai karasa magana ba na fashe da kuka, Me yasa su Ya shukra da Hameeda su ba za’ai musu auren ba sai ni? Okay! saboda ni ba yar gidan bace ba ko kuwa? Ko dan banda gata ne? Tsana ce wannan kome? Wayyo Allah na ni Khadija..Ashe daman ba Mas'oud aka zaba min ba? Kuka Sosai nake yi ina rike kai na. Duk duniya babu d'a namijin da nake so, gangar jiki na keson mallaka irin Mas'oud ba. Ina son Mas’oud saboda shine first love dina. Ina son Mas’oud saboda shi ya koya min so har nasan menene so? Ina son Mas’oud saboda shi ya rai ni zucia ta ya koya mata abinda take so. Ina son Mas’oud saboda yana so na so mai wuyar fassarawa.
“Innalillahi wa inna ilaihir raji’un...”
Shi naketa nanatawa a fili ina bubbuga kai na ajikin kujera, Kawu daddy ya sauke zuciya ina jiyo sautin ta,
“Kiyi hak’uri Khadija. Na rantse da Allah ban amince da aura miki shi ba don na cuce ki. Wallahil azim ba zan kai ki inda zaki wahala ba don na lalata miki rayuwa ba Khadija. Wallahi Khadija wannan auren ni inaji ajiki na alkhairi ne a gareki damu gabaki d'aya. Saboda Ina ji ajiki na nan gaba zaki ya ba min wannan rana..”
Kuka nake sosai shabe shabe ina fyace majina da kasan dankwali na.
“Kawu Mas'oud fa.. Mas’oud Kawu! Ina son Mas’oud.”
“Wanene haka kuma Khadija.?”
“Kawu shine wanda ya ke sona. Tun service dina muke tare Kawu daddy. Munyi alk’awarin aure dashi wallahi Kawu daddy..”
“Khadija me yasa be zo ya same ni da zancen ba? Akalla kafin ya fara neman ki sai ya nemi yarjewa ta kamar yadda wannan ya yi. Amman Me yasa bai turo Manya sunzo ba idan har da gaske yake yi Eh?”
Shiru nayi ina ajiyar zuciya.
“Yace ne.. Ko wansa bai yi aure ba kuma shine karami. Sannan bai gama ginin sa ba..”
“Sai Yaushe kenan zai fadawa manyan ki Uhm!? Ko kuwa zama za kiyi tayi kina jiran sa kina faman tsufa agida? Shi kuma yana bata miki lokaci? Daga karshe ma yazo yace miki an hada shi aure da yar uwar sa! Uhm? Shikenan tunda baki dauke ni amatsayin uba ba Khadija. Na ky’ale ki sa..”
Riko kafafun sa nayi ina Kuka, Ni din banza zan ki amincewa da maganar Kawu daddy? Mutumin da ya mayemin gurbin uwa da uba? Halacci d’aya zanyi shine na amince. Ba Wai don ina son wanda za’a daura min aure dashi ba. Kawai dai saboda Kawu daddy ne. A duniya banida mafiyin sa idan ka tsame sauran yayyun Umma ta.
“Bar Kuka Khadija.. Na kyaleki wallahi. Zan ku..”
“Na amince Kawu daddy.. Na amince wayyo Allah karkai fushi dani.”
“Allah ubangiji ya miki albarka. Ya biya miki bukatun ki na alkhairi, Allah yasa wannan auren ya zamo wanzuwar farin cikin ki, Yasa ki zama wata aba a rayuwa, Allah yasa ayi a sa’a. Nan da sati d’aya wato mai kamawa za’ayi in Shaa Allah!..”
Kasa magana nayi, Ni wallahi ji nake tamkar bacci nake yi. Gaba d’aya bana gane me kawun yake fada. Na sandai nace na amince amma gaba d’aya wani dishi dishi ma nake gani. Zucia ya da idanu na Mas’oud kawai suke nuna min, Sanye cikin kananun kaya yana rataye da ID card dinsa na wajen aiki. Cikin haka Mami ta banko kofa ta shigo,
“Meye haka ne? Koke-koken me aketayi ne uhm? Tun daga karamin parlor nake juyowa, Me akai ne?”
Tana magana tana sakace hakorin ta da toothpick.
“Babu komai ya akai..?”
Kawu daddy ya tambayeta yana duban ta da kyau .
“Koke koken da muketa jiyowa ne shysa na shigo ganin Lapia? Kar ma’kota su fara lek’owa suna tambaya.”
“Lapia Alhamdulillah Hajia. Ba kukan wani abun bane na farin ciki ne.”
“Toh faa! Tooo”
Mami tace hakan tana mai zama a gefen sa.
“Tashi kije Khadija. Allah ya miki albarka Khadija!”
“Aamin Kawu daddy..”
Mikewa nai dakyar ina tafiya. Ina jiyo mami nata tambayar sa menene?
“Wai meke faruwa ne alhaji. Alkhairin menene?”
“Hajia.. aure ne! Wani bawan Allah ne ke neman auren ta ya biyo ta kai na.”
“Aure..”
Mami tafada tana dafe da kirjin ta, Ni kuwa sauri nayi Na fita na jawo musu kofar. Ina fita na haye sama ina mai bude sabon shafin wani kukan. Mami ta muskuta kusa da Kawu daddy,
“Alhaji bangane me kunnuwa na suke jiye min ba, aure? Aure fa kace? Waye zai auri wa?”
“Hajjaju da hausa fa nake miki magana. Nace neman auren ta akazo waje na.”
“Au ashe da saninta ma shine take kukan munafurci kuma?”
“A’a Hajia wanda takeso daban. Wanda kuma yai tambaya daban.”
“Toh fa! Alhaji Kai wa ka bata kenan..?”
“Wanda ya fara magana mana.”
“Shi din wanene shi! Wai ka na nufin bada masaniyar ta ka bayar da auren nata ba? “
“Eh ban isa bane? Ni ba mahaifin ta bane.?”
Yatsina fuska Hajia Abeeda tayi tana sosa idon ta,
“Toh shi wannan Waye manemin kenan? Dan wanene?”
“Wallahi wani bawan Allah ne kawai nutsatstse ya kwanta min arai kuma.”
“Ya'yan abokan ka Wai..?”
“Ko d’aya wallahi.. wani ne daban. Marainiya ce gwara na aurar da ita hankali na yafi kwanciya.”
“Dankari Makari.. Ai shikenan! Toh su Shukra Alhaji ka nemo musu mana acikin yaran abokanan ka. Ko Yayan commissioners dinnan da kukayi makarnta.”
“Ai nagaya miki inde sai dan wane da wane zaki bari su aura ni babu ruwana na tsame hannu na, Muyi ta zama ana k’irga mana shekaru tare.”
“Wai dan anbiyo takan ka ance anason Dije? Tab Alhaji ai wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa, Dai dai ruwa dai dai tsaki. Su ana ganin kai ne mahaifin su babu kasakantaccen da zai biyo takan ka yace yana neman auren su.. “
Dr. Ismael yayi daria yana kurbar ruwan hannun sa, Yasan halin matar sa sarai, Shi yasa bazai taba gaya mata gidan da dije Zata shiga ba sai an daura aure ko kuma an kawo kayan aure abu ya kusan tabbata. Yasan kuma Zata titsiye Dijen da tambaya shiysa bai sanarwa Dijen bama, Duk ya tattara ya rufe su a fai-fai. Mami ta jima tana neman bugar cikin Dr. ismael don jin waye? amma tsabar zurfin ciki irin nasa duk nacinta haka ta hakura bataji Waye manemin na dije ba. Data dame shi ma sai ya rufe fuskar sa da jarida wai kansa ciwo yake. Tashi Tai ta fice ta kyale shi.
“Mami ya akai kuma..?”
“Kukan me take Mami.?”
Shukra da Hameeda suka tasata a gaba da tambaya ganinta fito daga wajen Dr. Ismael
“Hmm! Makira algunguma aure Zata yi fa..”
“Aure! Wa Zata aura Mami..?”
Hameeda ta tambaya tana raba idanuwa.
“Ba dai Mas’oud ba?”Shukrah ma ta tambayi Mami tana dafe kirji.
“Mami ina kwana..? An tashi lapia.”
“Lapia lou..” Ta bani amsa a tak’aice tana mai cigaba da kurbar tea dinta.
“Ya Shukra ina kwana? Ya Hameeda ina kwana.”
Kowannen su ya amsa babu yabo babu fallasa. Ganin haka na mike na daddebi abinda zan ci a plate na koma k’arshen parlorn nakeci acan. Sai bayan na kammala ina zaune ina karanta wani book na wajen aiki sai ga Kawu daddy yafito. Sanye cikin jallabiya.
“Kawu daddy...Barka da safiya Kawu daddy! An tashi lapia?”
“Alhamdulillah Khadija.. Muje ko?”
“Toh Kawu..”
Su Mami suka bimu da kallo, Yana gaba ina biye da shi ya shiga parlorn sa ya zauna akan babbar kujera ni kuma na tsakure a gefe,
“Hau kujera ki zauna mana.”
“Nan ya isa Kawu....”
Gyaran murya yai. Ya rage volume din CNN dake faman yi,
“Kafin dai mu fara magana ina son tabbatarwa kai na Kamar yadda kika sani, wannan maganar da muka yi dake a baya na aure ita ce ta kuma tasowa. Amman Shin ki na da saurayi ne dake zuwa neman ki gidan nan? Kai bama wannan ba. Akwai wanda ya taba yi miki zancen aure? Dan ni dai nasan da akwai zan sani ko kuwa..? Dan naje munyi magana da dangin mahaifinki, sun kuma bar min komai a hannuna cewar na yi komai da komai a game da auranki.”
Wani daskararren abu naji ya tokare min a wuya. Shin menene yake shirin faruwa dani.? Ko wani sharrin aka kullamin?
“Magana nake miki Khadija kin yi shiru...”
“Kawu daddy.. Ba.. babu!” Na samu kai na da bashi amsa haka! Kawu daddy ya sake yin shiru na dan wani lokacin kafin yace,
“Tun wannan dai wanda nazo nace miki na yaba da hankali da tunaninsa, gashi kai tsaye ni ya nema kinga kenan da gaske yake yi ko?”
Sake samun Kai na nayi da kada kai. To me zance? Shi kansa Mas’oud din yana namiji ya boye alakar mu bare ni Mace?
“Toh shikenan! Alhamdulillah tunda babu wata magana tsakanin ku da wani. Kinsan babu kyau neman aure akan aure. Wannan yaro me hankali da dattako ne, ya fito daga gidan mutunci. Yana neman auren ki.. Kuma azahirin gaskia ma nace na bashi. Saboda ko da kina da wanda kike so din a matsayina na mahaifi agare ki. Babu wanda ya zo ya same ni. Manya basu shigo ciki ba, Dama already blood sample/genotype dinki sunyi kyau. Kowa zaki iya aura, Kuma Khadija...”
Ai bai karasa magana ba na fashe da kuka, Me yasa su Ya shukra da Hameeda su ba za’ai musu auren ba sai ni? Okay! saboda ni ba yar gidan bace ba ko kuwa? Ko dan banda gata ne? Tsana ce wannan kome? Wayyo Allah na ni Khadija..Ashe daman ba Mas'oud aka zaba min ba? Kuka Sosai nake yi ina rike kai na. Duk duniya babu d'a namijin da nake so, gangar jiki na keson mallaka irin Mas'oud ba. Ina son Mas’oud saboda shine first love dina. Ina son Mas’oud saboda shi ya koya min so har nasan menene so? Ina son Mas’oud saboda shi ya rai ni zucia ta ya koya mata abinda take so. Ina son Mas’oud saboda yana so na so mai wuyar fassarawa.
“Innalillahi wa inna ilaihir raji’un...”
Shi naketa nanatawa a fili ina bubbuga kai na ajikin kujera, Kawu daddy ya sauke zuciya ina jiyo sautin ta,
“Kiyi hak’uri Khadija. Na rantse da Allah ban amince da aura miki shi ba don na cuce ki. Wallahil azim ba zan kai ki inda zaki wahala ba don na lalata miki rayuwa ba Khadija. Wallahi Khadija wannan auren ni inaji ajiki na alkhairi ne a gareki damu gabaki d'aya. Saboda Ina ji ajiki na nan gaba zaki ya ba min wannan rana..”
Kuka nake sosai shabe shabe ina fyace majina da kasan dankwali na.
“Kawu Mas'oud fa.. Mas’oud Kawu! Ina son Mas’oud.”
“Wanene haka kuma Khadija.?”
“Kawu shine wanda ya ke sona. Tun service dina muke tare Kawu daddy. Munyi alk’awarin aure dashi wallahi Kawu daddy..”
“Khadija me yasa be zo ya same ni da zancen ba? Akalla kafin ya fara neman ki sai ya nemi yarjewa ta kamar yadda wannan ya yi. Amman Me yasa bai turo Manya sunzo ba idan har da gaske yake yi Eh?”
Shiru nayi ina ajiyar zuciya.
“Yace ne.. Ko wansa bai yi aure ba kuma shine karami. Sannan bai gama ginin sa ba..”
“Sai Yaushe kenan zai fadawa manyan ki Uhm!? Ko kuwa zama za kiyi tayi kina jiran sa kina faman tsufa agida? Shi kuma yana bata miki lokaci? Daga karshe ma yazo yace miki an hada shi aure da yar uwar sa! Uhm? Shikenan tunda baki dauke ni amatsayin uba ba Khadija. Na ky’ale ki sa..”
Riko kafafun sa nayi ina Kuka, Ni din banza zan ki amincewa da maganar Kawu daddy? Mutumin da ya mayemin gurbin uwa da uba? Halacci d’aya zanyi shine na amince. Ba Wai don ina son wanda za’a daura min aure dashi ba. Kawai dai saboda Kawu daddy ne. A duniya banida mafiyin sa idan ka tsame sauran yayyun Umma ta.
“Bar Kuka Khadija.. Na kyaleki wallahi. Zan ku..”
“Na amince Kawu daddy.. Na amince wayyo Allah karkai fushi dani.”
“Allah ubangiji ya miki albarka. Ya biya miki bukatun ki na alkhairi, Allah yasa wannan auren ya zamo wanzuwar farin cikin ki, Yasa ki zama wata aba a rayuwa, Allah yasa ayi a sa’a. Nan da sati d’aya wato mai kamawa za’ayi in Shaa Allah!..”
Kasa magana nayi, Ni wallahi ji nake tamkar bacci nake yi. Gaba d’aya bana gane me kawun yake fada. Na sandai nace na amince amma gaba d’aya wani dishi dishi ma nake gani. Zucia ya da idanu na Mas’oud kawai suke nuna min, Sanye cikin kananun kaya yana rataye da ID card dinsa na wajen aiki. Cikin haka Mami ta banko kofa ta shigo,
“Meye haka ne? Koke-koken me aketayi ne uhm? Tun daga karamin parlor nake juyowa, Me akai ne?”
Tana magana tana sakace hakorin ta da toothpick.
“Babu komai ya akai..?”
Kawu daddy ya tambayeta yana duban ta da kyau .
“Koke koken da muketa jiyowa ne shysa na shigo ganin Lapia? Kar ma’kota su fara lek’owa suna tambaya.”
“Lapia Alhamdulillah Hajia. Ba kukan wani abun bane na farin ciki ne.”
“Toh faa! Tooo”
Mami tace hakan tana mai zama a gefen sa.
“Tashi kije Khadija. Allah ya miki albarka Khadija!”
“Aamin Kawu daddy..”
Mikewa nai dakyar ina tafiya. Ina jiyo mami nata tambayar sa menene?
“Wai meke faruwa ne alhaji. Alkhairin menene?”
“Hajia.. aure ne! Wani bawan Allah ne ke neman auren ta ya biyo ta kai na.”
“Aure..”
Mami tafada tana dafe da kirjin ta, Ni kuwa sauri nayi Na fita na jawo musu kofar. Ina fita na haye sama ina mai bude sabon shafin wani kukan. Mami ta muskuta kusa da Kawu daddy,
“Alhaji bangane me kunnuwa na suke jiye min ba, aure? Aure fa kace? Waye zai auri wa?”
“Hajjaju da hausa fa nake miki magana. Nace neman auren ta akazo waje na.”
“Au ashe da saninta ma shine take kukan munafurci kuma?”
“A’a Hajia wanda takeso daban. Wanda kuma yai tambaya daban.”
“Toh fa! Alhaji Kai wa ka bata kenan..?”
“Wanda ya fara magana mana.”
“Shi din wanene shi! Wai ka na nufin bada masaniyar ta ka bayar da auren nata ba? “
“Eh ban isa bane? Ni ba mahaifin ta bane.?”
Yatsina fuska Hajia Abeeda tayi tana sosa idon ta,
“Toh shi wannan Waye manemin kenan? Dan wanene?”
“Wallahi wani bawan Allah ne kawai nutsatstse ya kwanta min arai kuma.”
“Ya'yan abokan ka Wai..?”
“Ko d’aya wallahi.. wani ne daban. Marainiya ce gwara na aurar da ita hankali na yafi kwanciya.”
“Dankari Makari.. Ai shikenan! Toh su Shukra Alhaji ka nemo musu mana acikin yaran abokanan ka. Ko Yayan commissioners dinnan da kukayi makarnta.”
“Ai nagaya miki inde sai dan wane da wane zaki bari su aura ni babu ruwana na tsame hannu na, Muyi ta zama ana k’irga mana shekaru tare.”
“Wai dan anbiyo takan ka ance anason Dije? Tab Alhaji ai wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa, Dai dai ruwa dai dai tsaki. Su ana ganin kai ne mahaifin su babu kasakantaccen da zai biyo takan ka yace yana neman auren su.. “
Dr. Ismael yayi daria yana kurbar ruwan hannun sa, Yasan halin matar sa sarai, Shi yasa bazai taba gaya mata gidan da dije Zata shiga ba sai an daura aure ko kuma an kawo kayan aure abu ya kusan tabbata. Yasan kuma Zata titsiye Dijen da tambaya shiysa bai sanarwa Dijen bama, Duk ya tattara ya rufe su a fai-fai. Mami ta jima tana neman bugar cikin Dr. ismael don jin waye? amma tsabar zurfin ciki irin nasa duk nacinta haka ta hakura bataji Waye manemin na dije ba. Data dame shi ma sai ya rufe fuskar sa da jarida wai kansa ciwo yake. Tashi Tai ta fice ta kyale shi.
“Mami ya akai kuma..?”
“Kukan me take Mami.?”
Shukra da Hameeda suka tasata a gaba da tambaya ganinta fito daga wajen Dr. Ismael
“Hmm! Makira algunguma aure Zata yi fa..”
“Aure! Wa Zata aura Mami..?”
Hameeda ta tambaya tana raba idanuwa.
“Ba dai Mas’oud ba?”Shukrah ma ta tambayi Mami tana dafe kirji.