Sashe 34
Abinda Ke Cikin Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau kam na fi koda yaushe saurin shiryawa dan zuwa gurin aiki saboda zumudi, na shirya tsab na dauki jakata Tukur driver ya dauke ni sai gurin aiki. Babu kowa sai wadanda suka yi aikin kwana, na shiga muka gaisa sannan na wuce office na zauna dan jiran lokacin da zan yi program dina. Bamu hadu da Mas'oud ba sai wajan karfe goma sha d'aya dalilin rashin zuwan sa da wuri. Sai da na jira har karfe d'aya lokacin da ya gama nashi sannan mukai sallah nace ina son yin magana dashi. Yana ta zolaya ta ganin yadda na cika da nishad'i ba kamar kullum ba, ya samar mana gurin zaman muka zauna.
“Ko ranar da aka daura mana igiyoyin aure sai haka madam, irin wannan murna da farin ciki haka, meye sirrin a ban nasha nima.”
Na yi dariya tare da rufe ido da hannayena, na bude ina wasa da zoben yatsa na nace.
“Albishirin ka?”
“Goro Oum Waleedah.”
“Fari ko baki?”
“Ahhh! Sai ma an jani tukunna? Toh na zabi uhmmmm... Uhmmmm... Zabar min dai da kanki.”
Ya yi maganar cike da shagwaba, ban san lokacin da na saki dariya ba ina cewa.
“Gaskiya kai zaka zaba, ai ni zan gaya ma albishir d'in.”
“Toh shi kenan na zabi fari tartar.”
“Yauwa jarumi na kasan me?”
“Sai kin gaya min da bakin ki sweetheart.”
“Kawu daddy ya gano cewa muna soyayya, jiya da kanshi ya kira ni yace ya yaba da hankalin ka ya amince za'a yi auran mu nan ba da jimawa ba.”
Mas'oud ya bude baki tare da zaro ido cike da tsantsar mamaki, ya kasa ma magana saboda yadda abin ya zo masa daga sama.
“Wai kina nufin kice min min daddy da kanshi ya gano cewa soyayya muke yi?”
Na gyada kai ba tare da na yi masa magana ba sai dariya nake yi. Kasan cewar a cikin office din su muke, kuma babu kowa a ciki sai kawai ya taso tare da yin juyi yana rawa ina dariya. Kusa dani na ji ya matso tamkar zai hade jikina da nashi nayi saurin rintsa ido saboda na riga na saddakar da faruwar hakan, sai naji yace.
“Ina ma ace ina da wannan damar, dana nuna miki irin tsantsar farin cikin da na shiga ta hanyar baki lafiyayyan runguma. But ya zama bashi, Allah ya kai mu lokacin da zamu zama abu d'aya zan biya ki harda na yau.”
Sai ya d'an matsa daga kusa da ni ya zauna akan kujerar da ya taso, sannan ne na samu damar bude idanu na.
“Kin fiye jin tsoro Oum Waleed, ya kamata kuma na rage miki yawan shi.”
“Ai ni wani lokacin wallahi tsoranka nake ji, dubi yanzu fa kana kokarin taba ni.”
“Ban taba ba ai Oum waleedah, but soon zan yi miki abin da yafi tabawa ma.”
Na share shi dan idan na biye masa tsab zai sanya ni cikin wani yanayin da ban shirya zuwan sa ba. Muka ci gaba da hira saboda zakewa harda yadda bikin zai kasance muke ta tattaunawa hankali kwance. Tun daga wannan lokacin muka sake d'in kewa ni da Mas'oud saboda ganin zamu mallaki juna. Daga ni har shi bamu taba kawowa cewar kawu daddy ba junan mu ya mallakawa ba, saboda bai fito fili ya bayyana mana cewa ga yadda yake nufi ba. Haka muka ci gaba da rayuwa lokaci yana ta tahowa, Mas'oud yana ta hada kudin da zai turo gidan mu dan nema masa aure na kamar yadda ake yi.
*FADAR BASANNABAS*
Tunda yai mafarkin nan yake jin jikin sa yana rawa, Tunani ne dankare a kirjin sa. Amma ya kasa samun nutsuwar yadda zai warware shi. Dafe kansa yai ya rintse idanun sa. Yana zaune a fada amma bai bada damar aiwa kowa iso ba. Jakadiya sai zarya take tana sanar masa isowar mutane. Dakyar ya bari tabawa waziri dama ya shigo,
“Allah yaja zamanin sarki adali. Allah ya Kara Maka lapia da nisan kwana mai amfani ranka ya dade!”
Hannu sarki Salmaan ya daga masa yana dafe da habar sa,
“Allah ya tausasa ran sarki! Allah yakara maka dattako baban kowa. Shin akwai abunda ke damun Sarkin mu ne? Sanar min ko menene shi shugaba na.”
Sarki Salmaan ya d’anyi murmushin jin dadi. A duk duniya waziri na cikin sahun mutanen farko da yake so. Saboda a kullum sai ya tambayi abinda ke damun sa yana kuma k’ok’arin ganin ya yaye masa matsalolin sa,
“Waziri... Nayi mafarki irin na kwanaki. Menene gaskiyar al’amari?”
“Allah ya karawa sarki lapia. Tabbas shakka babu zamu iya fassara hakan da cewar sharri ne na mafarki. Amma kuma idan aka auna abun a mizanin hankali za’a gano akwai kullalliya ko makircin bil adama..”
“Menene mafita to...?”
“Kamar dai yadda na nemo maka hayakin nan da ka yiyyi kwanaki? Yanzun ma zan koma wajen Malam din na karbo maka wani..”
Kada kai SAS yayi kafin su cigaba da magana data shafi fada. Mikewa sarki yayi. Dogaran sa suka rufe shi ya wuce sashen sa jin yadda yake wani irin jiri mai gigita kwakwalwa, ga ciwon kai da yake kuma barazanar faduwa. Waziri ne ya cigaba da zaman fadar, inda ya zauna dasu Galadima, ciroma, wambai da sauran su. Ya sanar da su rashin lafiyar sarki Salman tare da umartar wani babban hadimin sa da cewar yana son ya kuma karbo masa wannan hayakin a wajan malam kamar yadda ya taba karbowa kwanaki.
Galadima ya kalli ciroma suka saki wani murmushi ta cikin rawanin su, da alama wata damar ce zasu samu wajan kuma yiwa sarki Salman wani makircin. Nan dai suka nuna jimami da alhinin rashin lafiyar, amman a zukatan su ba haka abin yake ba, wata muguwar manufa ce a rasu. Ciroma da kanshi yaje ya karbo wasu kayan tsibbun wanda yake dauke da tsana mai karfi tsakanin sarki Salman da mahaifiyarsa, ganin ya fara mafarki da ita sun tabbatar zasu iya shiryawa, wanda shirin zai iya wargaza musu duk wani shiri da suka yiwa masarautar. Shi kuma tunda ya shiga daki ya kwanta yake wani irin bacci mai nauyi da ko wane irin ihu ba zai iya farkar da shi ba.
____Cikin wasu furanni masu launin shudi da rawaya yake hangenta, sanye da kaya na alfarma sai faman murmushi take yi. Shi kuma yana daga gefe zaune da jarida yana dubawa sai idanunsa suka sauka akan ta, ya dinga kallon ta yana son kuma ya gano wa take yiwa wannan fara'ar mai tsadar gaske. Ya mike cike da kasaita yana isa gurin da take sai yaga shi take yiwa dariyar, ya kuma kallon ta tare da kamo hannunta sai kawai ta shige jikinsa tana kankamewa, murya a raunane yaji tana cewa.
“Nagode ya kai annurin da yake haskaka min zuciya ta, tun dazu nake nan ina jiran zuwanka.”
Shafar bayanta kawai ya yi ba tare da ya yi magana ba. Shan kamshin nan nasa yana sake sanya ta cikin begen sa, ta dago fuskarta tana kallon tashi tace.
“I love you my hubby.”
Sai ga Shaheedah tazo gurin, gabansa ya yi mugun bugawa, amman sai yaji Dijen ta rike shi tana cewa.
“Kadena jin shakkarta saboda ita ba komai bace face azzaluma, ba ta son ka shi yasa take cin zalinka. Allah ya fita babu abin da ta isa ta yi maka ina tare da kai my hubby.”
Ya samu kansa da tsayawa a gurin na ta duk da tsoran da yake tattare da shi na Shaheedah. Daga gefe ta tsaya itama tama miko masa hannu wai yaje, sai ya kalli Dije ya kuma kallon Shaheedah yana tunani yadda zai yi. Zuwan wani saurayi gurin yana kuka shine yasa Shaheedah barin gurin, Dije kuma ta kama shi suka tafi daki. Sai ya kuma jin nutsuwa yana yiwa Allah godiya da ya bashi Khadija matsayin mata abar alfahari. Sam be yi zaton a bacci yake ganin hakan ba sai sa ya farka ya ganshi a tsakiyar gadon sa yana juye-juye a kai. Tabbas yaji a jikinsa Khadija itace zabin zuciyar shi, dole ne ya ci gaba da farautar neman auran ta koda kuwa yin auran zai janyo abubuwa da dama a cikin masarautar. Sai da ya yi wanka ya shirya sannan ya nemo amintaccen bafadensa wato Al-hassan, suka kebe yace masa yana son a ci gaba da shirye-shiryen auran sa kamar yadda suka fara. Ya amsa sannan ya sake komawa wajan Alhaji Isma'il wanda ya tabbatar da cewar zai je dangin mahaifin Khadija ya sanar dasu, idan yaso yana dawowa sai ya sanar da a shirya daurin auran.
Haka kuwa aka yi Alhaji Isma'il be sanar da su Mami zai je ba, sai shiryawa ya yi da shatara ta arzikinsa ya je ya sanar dasu komai, suma dai be gaya musu wanda zata aura ba, ya ce musu dai ya amince da tarbiyar yaron dan gidan mutunci ne iyayensa masu daraja ne. Suka amince tare da bashi ragamar aurar da Khadija, a cewar su ai shine uwa da uba na ta dan haka babu wani abu da zasu ce sai fatan Alkairi a cikin auran. Bayan ya dawo ne yake sanar da Mami cewa yaje can sun gama komai sannan ya kira yan uwansa suma ya gaya musu sunce idan lokacin yazo yasu bar komai su zo ayi dasu. Bata damu ba dan bata yi zatan wani mai daraja za'a aurawa Khadijan ba.
Tunda aka fara wannan abun Dije da Mas'oud basu yi zaton ba junan su zasu aura ba, basu zaci hangen da kawu daddy ya yi ba akan su yake ba, sai da abin yazo gab har ana sauran sati daya biki sannan ne yace da Dije zai kuma yin magana da ita idan ya gama komai. Kasan cewar da yamma ne ta gaya mata kuma Jumma'a ce yana ganawa da mutane yan kasuwa, shi yasa ta bari zuwa gobe idan Allah ya kaimu.
°°°°°°°°°°° °°°°°°°°°°°°°° °°°°°°°°°°°°
*WASHE-GARI*
“Ko ranar da aka daura mana igiyoyin aure sai haka madam, irin wannan murna da farin ciki haka, meye sirrin a ban nasha nima.”
Na yi dariya tare da rufe ido da hannayena, na bude ina wasa da zoben yatsa na nace.
“Albishirin ka?”
“Goro Oum Waleedah.”
“Fari ko baki?”
“Ahhh! Sai ma an jani tukunna? Toh na zabi uhmmmm... Uhmmmm... Zabar min dai da kanki.”
Ya yi maganar cike da shagwaba, ban san lokacin da na saki dariya ba ina cewa.
“Gaskiya kai zaka zaba, ai ni zan gaya ma albishir d'in.”
“Toh shi kenan na zabi fari tartar.”
“Yauwa jarumi na kasan me?”
“Sai kin gaya min da bakin ki sweetheart.”
“Kawu daddy ya gano cewa muna soyayya, jiya da kanshi ya kira ni yace ya yaba da hankalin ka ya amince za'a yi auran mu nan ba da jimawa ba.”
Mas'oud ya bude baki tare da zaro ido cike da tsantsar mamaki, ya kasa ma magana saboda yadda abin ya zo masa daga sama.
“Wai kina nufin kice min min daddy da kanshi ya gano cewa soyayya muke yi?”
Na gyada kai ba tare da na yi masa magana ba sai dariya nake yi. Kasan cewar a cikin office din su muke, kuma babu kowa a ciki sai kawai ya taso tare da yin juyi yana rawa ina dariya. Kusa dani na ji ya matso tamkar zai hade jikina da nashi nayi saurin rintsa ido saboda na riga na saddakar da faruwar hakan, sai naji yace.
“Ina ma ace ina da wannan damar, dana nuna miki irin tsantsar farin cikin da na shiga ta hanyar baki lafiyayyan runguma. But ya zama bashi, Allah ya kai mu lokacin da zamu zama abu d'aya zan biya ki harda na yau.”
Sai ya d'an matsa daga kusa da ni ya zauna akan kujerar da ya taso, sannan ne na samu damar bude idanu na.
“Kin fiye jin tsoro Oum Waleed, ya kamata kuma na rage miki yawan shi.”
“Ai ni wani lokacin wallahi tsoranka nake ji, dubi yanzu fa kana kokarin taba ni.”
“Ban taba ba ai Oum waleedah, but soon zan yi miki abin da yafi tabawa ma.”
Na share shi dan idan na biye masa tsab zai sanya ni cikin wani yanayin da ban shirya zuwan sa ba. Muka ci gaba da hira saboda zakewa harda yadda bikin zai kasance muke ta tattaunawa hankali kwance. Tun daga wannan lokacin muka sake d'in kewa ni da Mas'oud saboda ganin zamu mallaki juna. Daga ni har shi bamu taba kawowa cewar kawu daddy ba junan mu ya mallakawa ba, saboda bai fito fili ya bayyana mana cewa ga yadda yake nufi ba. Haka muka ci gaba da rayuwa lokaci yana ta tahowa, Mas'oud yana ta hada kudin da zai turo gidan mu dan nema masa aure na kamar yadda ake yi.
*FADAR BASANNABAS*
Tunda yai mafarkin nan yake jin jikin sa yana rawa, Tunani ne dankare a kirjin sa. Amma ya kasa samun nutsuwar yadda zai warware shi. Dafe kansa yai ya rintse idanun sa. Yana zaune a fada amma bai bada damar aiwa kowa iso ba. Jakadiya sai zarya take tana sanar masa isowar mutane. Dakyar ya bari tabawa waziri dama ya shigo,
“Allah yaja zamanin sarki adali. Allah ya Kara Maka lapia da nisan kwana mai amfani ranka ya dade!”
Hannu sarki Salmaan ya daga masa yana dafe da habar sa,
“Allah ya tausasa ran sarki! Allah yakara maka dattako baban kowa. Shin akwai abunda ke damun Sarkin mu ne? Sanar min ko menene shi shugaba na.”
Sarki Salmaan ya d’anyi murmushin jin dadi. A duk duniya waziri na cikin sahun mutanen farko da yake so. Saboda a kullum sai ya tambayi abinda ke damun sa yana kuma k’ok’arin ganin ya yaye masa matsalolin sa,
“Waziri... Nayi mafarki irin na kwanaki. Menene gaskiyar al’amari?”
“Allah ya karawa sarki lapia. Tabbas shakka babu zamu iya fassara hakan da cewar sharri ne na mafarki. Amma kuma idan aka auna abun a mizanin hankali za’a gano akwai kullalliya ko makircin bil adama..”
“Menene mafita to...?”
“Kamar dai yadda na nemo maka hayakin nan da ka yiyyi kwanaki? Yanzun ma zan koma wajen Malam din na karbo maka wani..”
Kada kai SAS yayi kafin su cigaba da magana data shafi fada. Mikewa sarki yayi. Dogaran sa suka rufe shi ya wuce sashen sa jin yadda yake wani irin jiri mai gigita kwakwalwa, ga ciwon kai da yake kuma barazanar faduwa. Waziri ne ya cigaba da zaman fadar, inda ya zauna dasu Galadima, ciroma, wambai da sauran su. Ya sanar da su rashin lafiyar sarki Salman tare da umartar wani babban hadimin sa da cewar yana son ya kuma karbo masa wannan hayakin a wajan malam kamar yadda ya taba karbowa kwanaki.
Galadima ya kalli ciroma suka saki wani murmushi ta cikin rawanin su, da alama wata damar ce zasu samu wajan kuma yiwa sarki Salman wani makircin. Nan dai suka nuna jimami da alhinin rashin lafiyar, amman a zukatan su ba haka abin yake ba, wata muguwar manufa ce a rasu. Ciroma da kanshi yaje ya karbo wasu kayan tsibbun wanda yake dauke da tsana mai karfi tsakanin sarki Salman da mahaifiyarsa, ganin ya fara mafarki da ita sun tabbatar zasu iya shiryawa, wanda shirin zai iya wargaza musu duk wani shiri da suka yiwa masarautar. Shi kuma tunda ya shiga daki ya kwanta yake wani irin bacci mai nauyi da ko wane irin ihu ba zai iya farkar da shi ba.
____Cikin wasu furanni masu launin shudi da rawaya yake hangenta, sanye da kaya na alfarma sai faman murmushi take yi. Shi kuma yana daga gefe zaune da jarida yana dubawa sai idanunsa suka sauka akan ta, ya dinga kallon ta yana son kuma ya gano wa take yiwa wannan fara'ar mai tsadar gaske. Ya mike cike da kasaita yana isa gurin da take sai yaga shi take yiwa dariyar, ya kuma kallon ta tare da kamo hannunta sai kawai ta shige jikinsa tana kankamewa, murya a raunane yaji tana cewa.
“Nagode ya kai annurin da yake haskaka min zuciya ta, tun dazu nake nan ina jiran zuwanka.”
Shafar bayanta kawai ya yi ba tare da ya yi magana ba. Shan kamshin nan nasa yana sake sanya ta cikin begen sa, ta dago fuskarta tana kallon tashi tace.
“I love you my hubby.”
Sai ga Shaheedah tazo gurin, gabansa ya yi mugun bugawa, amman sai yaji Dijen ta rike shi tana cewa.
“Kadena jin shakkarta saboda ita ba komai bace face azzaluma, ba ta son ka shi yasa take cin zalinka. Allah ya fita babu abin da ta isa ta yi maka ina tare da kai my hubby.”
Ya samu kansa da tsayawa a gurin na ta duk da tsoran da yake tattare da shi na Shaheedah. Daga gefe ta tsaya itama tama miko masa hannu wai yaje, sai ya kalli Dije ya kuma kallon Shaheedah yana tunani yadda zai yi. Zuwan wani saurayi gurin yana kuka shine yasa Shaheedah barin gurin, Dije kuma ta kama shi suka tafi daki. Sai ya kuma jin nutsuwa yana yiwa Allah godiya da ya bashi Khadija matsayin mata abar alfahari. Sam be yi zaton a bacci yake ganin hakan ba sai sa ya farka ya ganshi a tsakiyar gadon sa yana juye-juye a kai. Tabbas yaji a jikinsa Khadija itace zabin zuciyar shi, dole ne ya ci gaba da farautar neman auran ta koda kuwa yin auran zai janyo abubuwa da dama a cikin masarautar. Sai da ya yi wanka ya shirya sannan ya nemo amintaccen bafadensa wato Al-hassan, suka kebe yace masa yana son a ci gaba da shirye-shiryen auran sa kamar yadda suka fara. Ya amsa sannan ya sake komawa wajan Alhaji Isma'il wanda ya tabbatar da cewar zai je dangin mahaifin Khadija ya sanar dasu, idan yaso yana dawowa sai ya sanar da a shirya daurin auran.
Haka kuwa aka yi Alhaji Isma'il be sanar da su Mami zai je ba, sai shiryawa ya yi da shatara ta arzikinsa ya je ya sanar dasu komai, suma dai be gaya musu wanda zata aura ba, ya ce musu dai ya amince da tarbiyar yaron dan gidan mutunci ne iyayensa masu daraja ne. Suka amince tare da bashi ragamar aurar da Khadija, a cewar su ai shine uwa da uba na ta dan haka babu wani abu da zasu ce sai fatan Alkairi a cikin auran. Bayan ya dawo ne yake sanar da Mami cewa yaje can sun gama komai sannan ya kira yan uwansa suma ya gaya musu sunce idan lokacin yazo yasu bar komai su zo ayi dasu. Bata damu ba dan bata yi zatan wani mai daraja za'a aurawa Khadijan ba.
Tunda aka fara wannan abun Dije da Mas'oud basu yi zaton ba junan su zasu aura ba, basu zaci hangen da kawu daddy ya yi ba akan su yake ba, sai da abin yazo gab har ana sauran sati daya biki sannan ne yace da Dije zai kuma yin magana da ita idan ya gama komai. Kasan cewar da yamma ne ta gaya mata kuma Jumma'a ce yana ganawa da mutane yan kasuwa, shi yasa ta bari zuwa gobe idan Allah ya kaimu.
°°°°°°°°°°° °°°°°°°°°°°°°° °°°°°°°°°°°°
*WASHE-GARI*