← Book details Abinda Ke Cikin Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 108

Sashe 33

Abinda Ke Cikin Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Guda uku 3 Kuma 450,

Guda biyu 2 Kuma 400,

Guda daya akan 300.

Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

*+234 903 234 5899*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

*09033181070*

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥.   [3/30, 9:40 PM] Maman Maryam: www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac.

_*ASSALAMU ALAIKUM SISTERS..!_*

_*INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN: _*
_*HERBALS APHRODISIAC MA’ANA NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?_*

_*TO KU MATSO, DOMIN NESA TAZO KUSA.._*

_*ZEE HERBALS APHRODISIAC_*
_*ZEE HERBALS APHRODISIAC_*
_*ZEE HERBALS APHRODISIAC_*

_*MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA KI CIKI DA WAJE_*

_*MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI LUWAI TAMKAR TA JARIRAI_*

_*AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI._*

_*KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI_*

_*AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)_*

_*KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA... SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC_*

_*MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA_*

_INSTAGRAM LINK DIN MU:_

www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac

_WHATSAPP LINK DIN MU:_
https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz

_NAMBAR TARHON MU_
08169380189

_*DA A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYAN MU A KO’INA A FADIN NAJERIYA._*

_*BE YOUR OWN BOSS, BUILD YOUR OWN EMPIRE, BE THE WHOLE WORLD OF HIS MAJESTY( YOUR HUBBY) BE THE ONLY CENTER OF ATTRACTION WITH ZEE HERBALS APHRODISIAC. OUR PRODUCTS LASTS LONGER AND VERY EFFECTIVE. NO SIDE EFFECTS. AVAILABLE N WHOLESALE/ RETAILS.. DELIVERY IS NATIONWIDE. 100% TESTED AND TRUSTED_*

*1___9*

_Zakuga canjin sunan masarauta daga BARNABAS... zuwa BASANNABAS. Ko ince tun d’and’ano ma na canza. Na manta ban sanar ba.. My baddd! So dai komai yana bukatar sanarwa. Bayan nayi bincike nagano BARNABAS. Wani suna ne ko ince abu ne daya danganci ma’abota littafi. Sunan yazo acikin bible ma sunce: The Gospel of Barnabas is a book depicting the life of Jesus😅so BARNABAS din Joseph dinsu ne acikin bible.. To avoid consequences 😂💔salin alin se muka koma da BASANNABAS. Duk kuwa da kirkirarren labari ne gara a canza din🤤 case closed ko? .. To acigaba da gashi🤗😉_

*MASARAUTAR BASANNABAS*

*Yadda* taga yana ta waige waige kamar yana neman wani abu a kusurwoyin dakin yasa itama ta tsorata tare da rike shi. Nan take taji ya yi wancakali da ita yana kuka mai firgitarwa, hannayensa dafe a kai yana ihu. Tabbas akwai abin da yake damun sarki Salman wanda ta kasa fahimta, da tana tunanin ko maganin da tasa masa a cikin pillow ne, wanda su Gimbiya Najwa suka bata suka umarce ta da ta sanya masa, ko shine yasa shi yin wannan abun cikin talatainin dare? Babu mai ba ta wannan amsa, har sai taji abin da ya sanya shi yin wannan abun.

Gimbiya Shaheeda ta riko gaban sleeping dress d'in ta da botiran suke a bude, ta sake matsowa kusa da shi a tsorace dan gaba daya ya canza sai faman cije baki yake yi da hakoransa. Leka idanunsa tayi taga yana zubar da hawaye, abin da ta dade bata gani ba a tare da shi. Sai ta marairaice tana share masa kwallar saman kirjinsa, murya a sanyaye ta fara masa magana.

“Na tsorata da ganin ka cikin wannan yanayin, nasan mafarki kayi, kuma da alama bashi da dadi duba da yadda kake zubar da hawaye. Shin me ka gani a cikin mafarkin naka?”

Ya yi shiru ba tare da ya kalleta ba, ga wani irin azababban sanyi da yaji yana huda duk wata kofar gashi dake jikin shi. Zare hannunsa ya yi daga rikon da ta yi masa, ya janyo jarkar ruwa tare da budewa ya kafa kai yana sha. Tun da ya fara sha bai sauke ba sai da ya kusa shanyewa taji ya ja wani dogon numfashi tare da saukewa yana lumshe ido.

“Ko mafarkin Ammie ka yi?”

Sai tambayar ta ta tayi matukar daure masa kai, ya dago tare da kallon ta da jajayen idanunsa. Take yaji wani faduwar gaba, sai ya sunkuyar da fuska yana girgiza mata kai.

“Idan mafarkin ta kake yi ya kamata ka dena, domin Ammie sam bata kaunarka. Ka manta sanda za'a nada ka matsayin sarkin Basannabas ita tazo ta dinga gayawa mutane cewar kai juya ne baka haihuwa kar a baka? Ka manta?”

Salman ya yi shiru kafin daga bisani ya daga kai alamar haka aka yi. Shaheeda ta yi murmushi sannan ta sake matsawa jikin shi ta shige tana faman shafa shi, cikin tsantsar makirci tace masa.

“To ka dena damuwa da duk wanda be damu da san ganin abinda Allah ne ya mallaka maka shi. Ni zan kasan ce da kai a duk yanayin da kake ciki, zafi rana da damuna ba zan taba rabuwa da kai ba.”

Cikin matukar farin ciki Salman ya jinjina kai, sai kuma ya matsa ya kwanta akan pillow still tana jikin shi sai lailaya shi take kamar ta samu jariri sabuwar haihuwa. Daga haka ya manta da wannan mafarkin da ya yi da mahaifiyar shi, bacci ya kuma daukar shi. Gimbiya Shaheeda ta mike zaune lokacin da ta tabbatar da cewa ya yi bacci da gaske. Sakkowa ta yi daga kan gadon ta ciro wani farin zare daga cikin gashin kanta tana kare masa gani kafin ta yi murmushi wanda ita kadai ce tasan matsayin shi.

Boyewa tayi sannan ta shiga toilet ta tsarkake jikinta ta fito ta shirya ta kwanta tana jin farin ciki. Basu farka ba sai wajan karfe shida, ya bude ido da kyar sai yaga Shaheeda a kusa da shi, ya fara duba jikin shi. Gabaki d'aya bai san sunyi wani abu ba sai yanzu da yaga yanayin shi, ya duba agogo yaga lokacin sallah har ya wuce. Da sauri ya tashi ya tashe ta sai tace masa ai tayi wanka tun dare. Yaji haushi kuwa sai dai ko a fuska kasa nunawa ya yi, kawai ya wuce bathroom shima ranshi a bace.

*KHADIJA (Dije).....*

Tun da na idar da sallah nake jiran kiran kawu daddy da yace zai ganni da anjima amma naji shiru, sai na fito daga daki naje parlor na koma kitchen amman shiru yana daki be fito ba. Hakura na yi na koma daki na zauna ina duba wani littafi. Kamar jira ake na zauna sai ga kiran shi ya shigo waya ta, na daga yace na sakko na same shi a parlorn kasa. Jiki na rawa na dauki hijab nasa na fito dan na kagu naji abin da zai sanar da ni, wanda sam na kasa kawo ko meye a cikin zuciyata. Yana zaune rike da waya yana dannawa nayi masa sallama ya dago ya kalle ni, kafin na zauna ya ce yace na rufe kofar naje na rufe sannan na dawo na samu gefen kujera nesa dashi na zauna. Ya yi gyara murya tare da aje wayar a gefen sa ya dan matso daga gefen kujerar yace.

“Alhamdulillahi Khadija a kullum na kalli yadda rayuwar ki ta dawo na kanji dadi da farin ciki. Gashi cikin ikon Allah ya sake daga daraja da mutuncinki ta hanyar da bamu tunani ba, yanzu bani da wani buri irin naga na mika ki zuwa dakin mijin ki, wannan shine buri na na biyu akan ki Khadija. Ina fatan zaki ci gaba da kulawa da kanki kamar yadda kike yi a koda yaushe. Na ga yanzu Allah ya baki miji wanda nake saka ran insha Allahu shine fitila na gaba da zai ci gaba da haskakawa a cikin duniyar ki. Ni dai ya yi min, tarbiyarsa, dabi'unsa da kuma kalamarsa duk ba bu wanda ban duba ba. Kema nasan zai yi miki, naga yaro ne matashi mai jini a jika, Allah ya daukaka shi a cikin tarin ni'imomin da yake da su.”

Kai na a kasa farin ciki ya mamaye ni, ashe kawu daddy kallon takun mu kawai yake yi nida Mas'oud bamu sani ba? Lallai babba-babba ne inji bahaushe da yace yaro ko ya hau rimi ba zai iya hango komai ba. Wayyo Allah dadi sai na hango gashi har an daura mana aure an kai ni gidan Mas'oud birnin zuciya ta muna ta shan soyayyar mu.

“Nan da dan wani lokaci za'a daura auran ku insha Allahu. Duk da cewa bani ne wanda zai bada auran ki ba, amman na dauki alkawarin zuwa can dangin mahaifinki da kai na nayi musu bayani yadda zasu fahimta. Allah ya yi miki albarka Khadija tashi kije daki ki kwanta nasan gobe akwai aiki.”

Ciki da jin kunya na tashi na ruga da gudu, farin ciki da nishad'i na suka dadu ba. Kan gado na fada ina tsalle tamkar wata yar shekara uku, na kagu Mas'oud ya kirani dan na kyankyasa masa wannan zazzafan labarin wanda nasan idan yaji ko bacci ba zai iya yi ba saboda murna. Wani ikon Allah sai be kira ba sai sako da ya turo min na text message cewar suna tare da Abban su ba zai samu damar kira ba mu hadu gobe a gurin aiki. Banji komai ba saboda ina cike da murna na je kitchen na zuba abinci naci sannan na dawo na kwanta cike da zakuwar ganin gobe.

*WASHE GARI*
Chapter 33 · 0% Book details