Sashe 83
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yamara da kanta ta haɗa mata mai na amfani iya fuska mai ɗauke da aloe vera da honey da ƙwai cikin sati guda jikin Ridayya ya dinga wani glowing duk inda ta zauna kuma sai ta bar alama ko waje ya jiƙe ga wani mafifaffen ƙamshi daya zauna a jininta na musamman. Aka dawo kai kullum sumar sai an wake da karkashi da wasu tarkace ashe duk tsayin gashin ba iya haka yake ba, daman gashi da laushi sai ya zamana ko kalba akai baya zama ware wa yake.
Ridayya duk da gyaran ne a gabanta ba yadda Yamara ke yi mata wani karatun ne bata ganewa idan ta faɗi wata maganar sai Ridayya ta runtse idanunta sannan ta sake fahimtar lallai akwai wani abu da take ji game da Ustaz, ga tsoran kasancewarta bazawara ga babban zunubin data aikata idan ta tuna wannan sai ta share domin har lokacin bata san Ustaz mijinta bane, a ranta take jin abinda yake mata ya shige misali kuma babu kyau ba zata bari hakan ta kasance ba. Ga wani baƙin cikin Mardiyya da take ji idan ya tuna ta sai ta ji gabaɗaya haushin Ustaz ɗin ya kamata.
Satin ta biyu tana zaune kamar sabuwar halitta hannunta riƙe da tsumi tana ta kwaɓe fuska kira ya shigo wayarta ta dinga bin number da kallo tunaninta Ustaz ne tunda har yanzu bai neme ta ba. Ta ɗaga wayar ta kara a kunne muryarta a kasalance ta ce
"Hello"
Ajjiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi ya ce "So is true"
Gabanta ya faÉ—i jin muryar Sadauki a hankali ta ce "Sadauki"
"Why Ridayya? Why why kashe ni kike son yi ko so da gaske kin yi blocked number na?"
"Kamarya"
A raunace ya ce "Kamar yadda na faɗa miki Shanshan sau nawa zan kira number ki baya tafiya, na shiga damuwa da tashin hankali gashi ban san gidanku ba, yin duniya Tajj ya faɗa mini yaƙi wallahi na kusa mutuwa a kan yanzu haka drip ne a hannnuna Shanshan"
Kamar zai yi mata kuka yadda yake marairaice murya can ƙasa "Ayya sannu ya jikin me ya same ka"
"You are the reason behind anything, kin guje wa ganina, na rasa kallonki da muryarki da jikin nan naki mai ƙara sawa na ji babu wata mace a duniya sai ke, Ridayya Allah ne shaida ina tsananin son ki"
"Uhm be patient Sahibi"
"Where are you zan zo na ganki" Ta ce "Kai da baka da lafiya?"
"Zan iya, idan na ganki zan warke daman rashin ki n Shanshan"
"Ka bari ka ji sauƙi mana"
Sadauki ya zare ruwan hannunsa yana miƙewa daga cinyar mother data gama cin kuka sosai ya ce "Uhm just tell me kina ina? I'll be there for you"
"Maiguduri"
Ya zare idanu sai kuma ya ɗan yi baya ya zauna, yana dafe kansa dake matuƙar sara masa ya jima kana ya sauke numfashi ya ce
"Yaushe kika je, when za ki dawo kuma?"
Tana ɗan kallon Anuty Kaltum ta ce "Sati na biyu sai na yi wata a can, idan na dawo zan faɗa maka" tun kafin ta ƙarasa maganar Sadauki yake girgiza kai ya ce "I can't wait any longer Shannn, ba zan iya zaman jira ba ki bani address zan zo na ganki mu tsayar da magana"
"Please mana ka bari ka ji sauƙi" Sadauki ya nace sosai ta ce "Shikenan to ko na faɗa maka ka zo ba zan fito ba"
"Shikenan Allah ya dawo mini dake lafiya, but promise me kina dawo za a tsayar da maganar auren mu already na faÉ—awa Prof da Mother"
"Na yi" Ya sauke numfashi mai ƙarfi yana ƙanƙame wayar ya ce "Thank you Shannn shaaa. Zanna kiran ki ok ki kula"
"Tom"
“I love youâ€
"Thank you" Ya sake cewa "I love you" ta ce "Thank you"
“I LOVE YOU JAANNâ€
Cikin jan aji ta ce "Really appreciate Sahibi"
“Mu'ahh💋"
Ya sakar mata ta cikin wayar tsigar jikinta ya tashi ta yi saurin kashe wayar tana lumshe idanunta tare da ƙanƙame wayar a ƙirjinta, ta jima a haka sai kuma ta ɗauki wayar ta kira number Ustaz da aka saka Abbieyna ana ɗagawa ta fara jin ruwan ashar kwando kwando kuma muryar Umma ce.
"Haihuwar tsiya mai raba ɗa da uwarsa Allah ya fiki kuma ke da shi har abada sai dai ki hange inuwarsa in sha Allah, bazawarar kawai baƙa gayyar muni ai kin yi kaɗan ɗana ya dinga wahala a kan ki mai baƙin jini wacce ta rasa mijin aure mijin nata ya kure ta....,"
Da sauri ta kashe wayar Anuty Kaltum kuma ta ji komai Ridayya ta fashe da kuka ta ce "Na shiga uku wallahi GiÉ—aÉ—o ba kura ta ya yi ba, ni ce na ce ya sake ni bana son zama dashi, don Allah Umma kar ki raba ni da Abbiey zan jure komai banda haka ni ban masa asiri ba ban san yaya ake yi ba"
Kuka take kamar ranta zai fita babu abinda ta tsana irin a ce ta rasa miji bata so, ta tsani gorin aure ko da sigar wasa ne sai ta yi mai isarta Anuty Kaltum ta bata ruwa ta sha kana ta ce "Mene damuwar don an rabaki da Ustaz?"
Da mamaki Ridayya ke kallon Anuty Kaltum "Yi ta kallona ba yanzu kuke waya da wani ba har yake miki kiss kina tunanin idan kika aure shi zai jure ganinki da Ustaz ne? Duk da muharraminki ke amma ai akwai aure tsakaninki da shi, idan bakya son rasa Ustaz so be with him, a yanzu ne yake buƙatarki bari na faɗa miki abinda baki sani ba Ridayya. Ai kin tuna sanda ya faɗi a Lagos ko?"
Bata amsa ba kallon Anuty Kaltum take kawai ta ɗora da "To tsautsayi ya saka Ustaz ya faɗa saman dutse ina nufin mararsa ta sauka akan dutse har aka yi masa aiki a mararsa, abinda ba ki sani ba ake ɓoye miki Ustaz ba zai taɓa haihuwa ba, kuma ba zai iya tarayya da mace ba a duniya saboda ya nakasa kinga kenan babu yadda za a yi ya samu macen da zata zauna da shi tsakani da Allah sai dan kuɗinsa, tunda da shi za fankon ashana duka ɗaya suke. Idan ke baki amshe shi ba waye zai amshe shi? Ki yi amfani da damarki kafin ta ƙwace miki, kina ji kina gani ganinsa zai yi miki wahala kina yawan ƙaryata abinda zuciyarka ke ƙoƙarin bayyanawa amma ba za ki iya ba, domin soyayya gaskiya ce yanzu ya rage naki ki rungumi Ustaz da ƙaddararsa ki taya shi share hawayen idanunta kamar yadda ya yi miki sanda kike neman mataimaki, soyayya bata ɓangare ɗaya bace kuma ƙarfe ɗaya baya amo!"
Tashi ta yi ta bar mata wajan cike da takaicin Ridayya da uwar Ustaz Umma kenan. Ridayya ta dinga juya maganganun Anuty Kaltum a kanta.
***
Tun bayan tafiyar Ridayya Umma ta saka Ustaz a gaba da masifa a kan ya saki Ridayya tun kafin ta dawo idan kuma har ta isa fa kenan. Ta ƙwace wayoyinsa gabaɗaya kamar yaro komai ta ce biyayya yake mata amma yana cikin azaba ya san ko yanzu ya faɗi ya mutu Umma ce sila a wannan lokacin ba Ridayya ba. Mardiyya aka samu abin yi Umma ta ƙara tabbatar mata Ustaz lafiya yake ta yi ƙoƙari su fahimci juna kafin mayyar ta dawo ta suɗe masa kurwa ko kunyar Baffa da Mami bata ji.
Ustaz ya samu meeting da Madugu kai tsaye Magudu da secretary na Jam'iyya suka faɗawa Ustaz ƙudirinsu na son tsayar da shi ɗan takara a matsayin gwamna a ƙarƙashin jam'iyyarsu. A nan take ya nuna he is not interested siyasa ba ita ce a gabansa secretary ya fara lallaɓa shi meeting ɗin ya ƙare babu daɗi amma Madugu ya kafa na ci.
Alhji Mansur da Alhji Tahir suka tsayar da biki wata uku masu zuwa ya yi daidai da kammala ginin Ustaz na gidansa Mami ta shiga shirye-shirye ita da su Yaya A'isha. Ammi ana ta ɓangaren tana ta haɗa plan B ɗinta ita da Burhan ba wanda ya san me take yi. _Only God knows!_ Ga Anuty Zuhura mijinta ya sake halin ta yi ya ji ta dawo gida.
Ustaz ne durƙushe gaban Umma hannunta riƙe da farar takarda da biro ta ce "Muhammmmd"
Ya ɗago kai ya kalleta ya kasa magana ta ce "Well is allowed ai kana ji, idan ni ce uwarka na yi cikinka na kuma na raini cikin tsayin wata tara, na yi nishin naƙudarka na shayar da kai nono na shekara biyu ciff wata ashirin da huɗu to ka gaggauta rubatawa Ridayya sakinta a wannan takardar idan ba haka ba wallahi wallahi sai na ɗaga maka nono kuma na yi maka Allah.....,"
Jikinsa na rawa ya amshi paper É—in gumi na yanko masa all over himself idanunsa ya jirkice ya ce "A'a kar ki mini Allah ya isa zan yi yadda kike so"
Rubutu ta fara a takardar yana gani dishi-dishi ya gama ya ninke sosai ya miƙewa Umma duk abinda yake faruwa Baba ƙarami yana kallo shigowarsa kenan cikin gidan. Umma ta yi murmushi ta rangaɗa buɗa ta ce "Allahamdulillah yadda yarinyar nan ta baka wahala albarkacin Annabi sai ta wahala a kan ka, ai daman na san ba za ka ƙi yi mini biyayya ba yanzu ka rungumi matarka baka da mace sama da Mardiyya"
Ustaz tunda ya miƙe tsaye jiri ya fara ɗaukar shi idanunsa baya buɗewa, yana jin idan har ya samu zarafin fita to ƙasar zai bari gabaɗaya kuma sarai ya san inda Ridayya take domin Zainura ta faɗa masa, ya ji a ransa ba zai ƙara kwana a gidan ba, ba zai ƙara kwana ɗaya a kano ba kuma ba zai sake yin sati guda a Nigeria ba. Zuciyarsa na bugawa da ƙarfi yana riƙe jikinsa a haka ya nufi hanyar waje Umma ta ce "Maza jeka sha iskar ƴan'ci ka dawo wajan matarka Allah ya yi maka albarka ba dai biyayya ba"
Ridayya duk da gyaran ne a gabanta ba yadda Yamara ke yi mata wani karatun ne bata ganewa idan ta faɗi wata maganar sai Ridayya ta runtse idanunta sannan ta sake fahimtar lallai akwai wani abu da take ji game da Ustaz, ga tsoran kasancewarta bazawara ga babban zunubin data aikata idan ta tuna wannan sai ta share domin har lokacin bata san Ustaz mijinta bane, a ranta take jin abinda yake mata ya shige misali kuma babu kyau ba zata bari hakan ta kasance ba. Ga wani baƙin cikin Mardiyya da take ji idan ya tuna ta sai ta ji gabaɗaya haushin Ustaz ɗin ya kamata.
Satin ta biyu tana zaune kamar sabuwar halitta hannunta riƙe da tsumi tana ta kwaɓe fuska kira ya shigo wayarta ta dinga bin number da kallo tunaninta Ustaz ne tunda har yanzu bai neme ta ba. Ta ɗaga wayar ta kara a kunne muryarta a kasalance ta ce
"Hello"
Ajjiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi ya ce "So is true"
Gabanta ya faÉ—i jin muryar Sadauki a hankali ta ce "Sadauki"
"Why Ridayya? Why why kashe ni kike son yi ko so da gaske kin yi blocked number na?"
"Kamarya"
A raunace ya ce "Kamar yadda na faɗa miki Shanshan sau nawa zan kira number ki baya tafiya, na shiga damuwa da tashin hankali gashi ban san gidanku ba, yin duniya Tajj ya faɗa mini yaƙi wallahi na kusa mutuwa a kan yanzu haka drip ne a hannnuna Shanshan"
Kamar zai yi mata kuka yadda yake marairaice murya can ƙasa "Ayya sannu ya jikin me ya same ka"
"You are the reason behind anything, kin guje wa ganina, na rasa kallonki da muryarki da jikin nan naki mai ƙara sawa na ji babu wata mace a duniya sai ke, Ridayya Allah ne shaida ina tsananin son ki"
"Uhm be patient Sahibi"
"Where are you zan zo na ganki" Ta ce "Kai da baka da lafiya?"
"Zan iya, idan na ganki zan warke daman rashin ki n Shanshan"
"Ka bari ka ji sauƙi mana"
Sadauki ya zare ruwan hannunsa yana miƙewa daga cinyar mother data gama cin kuka sosai ya ce "Uhm just tell me kina ina? I'll be there for you"
"Maiguduri"
Ya zare idanu sai kuma ya ɗan yi baya ya zauna, yana dafe kansa dake matuƙar sara masa ya jima kana ya sauke numfashi ya ce
"Yaushe kika je, when za ki dawo kuma?"
Tana ɗan kallon Anuty Kaltum ta ce "Sati na biyu sai na yi wata a can, idan na dawo zan faɗa maka" tun kafin ta ƙarasa maganar Sadauki yake girgiza kai ya ce "I can't wait any longer Shannn, ba zan iya zaman jira ba ki bani address zan zo na ganki mu tsayar da magana"
"Please mana ka bari ka ji sauƙi" Sadauki ya nace sosai ta ce "Shikenan to ko na faɗa maka ka zo ba zan fito ba"
"Shikenan Allah ya dawo mini dake lafiya, but promise me kina dawo za a tsayar da maganar auren mu already na faÉ—awa Prof da Mother"
"Na yi" Ya sauke numfashi mai ƙarfi yana ƙanƙame wayar ya ce "Thank you Shannn shaaa. Zanna kiran ki ok ki kula"
"Tom"
“I love youâ€
"Thank you" Ya sake cewa "I love you" ta ce "Thank you"
“I LOVE YOU JAANNâ€
Cikin jan aji ta ce "Really appreciate Sahibi"
“Mu'ahh💋"
Ya sakar mata ta cikin wayar tsigar jikinta ya tashi ta yi saurin kashe wayar tana lumshe idanunta tare da ƙanƙame wayar a ƙirjinta, ta jima a haka sai kuma ta ɗauki wayar ta kira number Ustaz da aka saka Abbieyna ana ɗagawa ta fara jin ruwan ashar kwando kwando kuma muryar Umma ce.
"Haihuwar tsiya mai raba ɗa da uwarsa Allah ya fiki kuma ke da shi har abada sai dai ki hange inuwarsa in sha Allah, bazawarar kawai baƙa gayyar muni ai kin yi kaɗan ɗana ya dinga wahala a kan ki mai baƙin jini wacce ta rasa mijin aure mijin nata ya kure ta....,"
Da sauri ta kashe wayar Anuty Kaltum kuma ta ji komai Ridayya ta fashe da kuka ta ce "Na shiga uku wallahi GiÉ—aÉ—o ba kura ta ya yi ba, ni ce na ce ya sake ni bana son zama dashi, don Allah Umma kar ki raba ni da Abbiey zan jure komai banda haka ni ban masa asiri ba ban san yaya ake yi ba"
Kuka take kamar ranta zai fita babu abinda ta tsana irin a ce ta rasa miji bata so, ta tsani gorin aure ko da sigar wasa ne sai ta yi mai isarta Anuty Kaltum ta bata ruwa ta sha kana ta ce "Mene damuwar don an rabaki da Ustaz?"
Da mamaki Ridayya ke kallon Anuty Kaltum "Yi ta kallona ba yanzu kuke waya da wani ba har yake miki kiss kina tunanin idan kika aure shi zai jure ganinki da Ustaz ne? Duk da muharraminki ke amma ai akwai aure tsakaninki da shi, idan bakya son rasa Ustaz so be with him, a yanzu ne yake buƙatarki bari na faɗa miki abinda baki sani ba Ridayya. Ai kin tuna sanda ya faɗi a Lagos ko?"
Bata amsa ba kallon Anuty Kaltum take kawai ta ɗora da "To tsautsayi ya saka Ustaz ya faɗa saman dutse ina nufin mararsa ta sauka akan dutse har aka yi masa aiki a mararsa, abinda ba ki sani ba ake ɓoye miki Ustaz ba zai taɓa haihuwa ba, kuma ba zai iya tarayya da mace ba a duniya saboda ya nakasa kinga kenan babu yadda za a yi ya samu macen da zata zauna da shi tsakani da Allah sai dan kuɗinsa, tunda da shi za fankon ashana duka ɗaya suke. Idan ke baki amshe shi ba waye zai amshe shi? Ki yi amfani da damarki kafin ta ƙwace miki, kina ji kina gani ganinsa zai yi miki wahala kina yawan ƙaryata abinda zuciyarka ke ƙoƙarin bayyanawa amma ba za ki iya ba, domin soyayya gaskiya ce yanzu ya rage naki ki rungumi Ustaz da ƙaddararsa ki taya shi share hawayen idanunta kamar yadda ya yi miki sanda kike neman mataimaki, soyayya bata ɓangare ɗaya bace kuma ƙarfe ɗaya baya amo!"
Tashi ta yi ta bar mata wajan cike da takaicin Ridayya da uwar Ustaz Umma kenan. Ridayya ta dinga juya maganganun Anuty Kaltum a kanta.
***
Tun bayan tafiyar Ridayya Umma ta saka Ustaz a gaba da masifa a kan ya saki Ridayya tun kafin ta dawo idan kuma har ta isa fa kenan. Ta ƙwace wayoyinsa gabaɗaya kamar yaro komai ta ce biyayya yake mata amma yana cikin azaba ya san ko yanzu ya faɗi ya mutu Umma ce sila a wannan lokacin ba Ridayya ba. Mardiyya aka samu abin yi Umma ta ƙara tabbatar mata Ustaz lafiya yake ta yi ƙoƙari su fahimci juna kafin mayyar ta dawo ta suɗe masa kurwa ko kunyar Baffa da Mami bata ji.
Ustaz ya samu meeting da Madugu kai tsaye Magudu da secretary na Jam'iyya suka faɗawa Ustaz ƙudirinsu na son tsayar da shi ɗan takara a matsayin gwamna a ƙarƙashin jam'iyyarsu. A nan take ya nuna he is not interested siyasa ba ita ce a gabansa secretary ya fara lallaɓa shi meeting ɗin ya ƙare babu daɗi amma Madugu ya kafa na ci.
Alhji Mansur da Alhji Tahir suka tsayar da biki wata uku masu zuwa ya yi daidai da kammala ginin Ustaz na gidansa Mami ta shiga shirye-shirye ita da su Yaya A'isha. Ammi ana ta ɓangaren tana ta haɗa plan B ɗinta ita da Burhan ba wanda ya san me take yi. _Only God knows!_ Ga Anuty Zuhura mijinta ya sake halin ta yi ya ji ta dawo gida.
Ustaz ne durƙushe gaban Umma hannunta riƙe da farar takarda da biro ta ce "Muhammmmd"
Ya ɗago kai ya kalleta ya kasa magana ta ce "Well is allowed ai kana ji, idan ni ce uwarka na yi cikinka na kuma na raini cikin tsayin wata tara, na yi nishin naƙudarka na shayar da kai nono na shekara biyu ciff wata ashirin da huɗu to ka gaggauta rubatawa Ridayya sakinta a wannan takardar idan ba haka ba wallahi wallahi sai na ɗaga maka nono kuma na yi maka Allah.....,"
Jikinsa na rawa ya amshi paper É—in gumi na yanko masa all over himself idanunsa ya jirkice ya ce "A'a kar ki mini Allah ya isa zan yi yadda kike so"
Rubutu ta fara a takardar yana gani dishi-dishi ya gama ya ninke sosai ya miƙewa Umma duk abinda yake faruwa Baba ƙarami yana kallo shigowarsa kenan cikin gidan. Umma ta yi murmushi ta rangaɗa buɗa ta ce "Allahamdulillah yadda yarinyar nan ta baka wahala albarkacin Annabi sai ta wahala a kan ka, ai daman na san ba za ka ƙi yi mini biyayya ba yanzu ka rungumi matarka baka da mace sama da Mardiyya"
Ustaz tunda ya miƙe tsaye jiri ya fara ɗaukar shi idanunsa baya buɗewa, yana jin idan har ya samu zarafin fita to ƙasar zai bari gabaɗaya kuma sarai ya san inda Ridayya take domin Zainura ta faɗa masa, ya ji a ransa ba zai ƙara kwana a gidan ba, ba zai ƙara kwana ɗaya a kano ba kuma ba zai sake yin sati guda a Nigeria ba. Zuciyarsa na bugawa da ƙarfi yana riƙe jikinsa a haka ya nufi hanyar waje Umma ta ce "Maza jeka sha iskar ƴan'ci ka dawo wajan matarka Allah ya yi maka albarka ba dai biyayya ba"