Sashe 16
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hehehe ki je ina? Ai ni dake mai ƙarfi yau shi zai ƙwaci kansa lashakka, ki bar gidan Ridayya matar mijin Zameer ban miki lahani ba? Ai ƙarya kike, Har ka tuna mini, an ce da mahaukaci ba ka duka, har ke ce kike cire kaya a gaban mijina ko? To bari na cire miki nono ɗaya sai naga gobe me za ki nuna" A gigice Khairiyya ta ce "Na shiga uku wallahi kin haukace, banda haka ni da nake ƙanwar miji meye na ɗora zargin naki akai na?" Ridayya ta ware idanu ta ce
"Au, ba rami mene ya kawo rami? Kin ji na Amjat zargi? Haka tara, in ji kishiyar mai mageduwa, ai shi ɗa na kowa ne, ƙanwar miji ai ƙanwa ce, dole na ba ki tarbiyya saboda gudun bakin jama'a"
Khairy ta ce "Don Allah ki barni na fita, na je gidanmu babu wani ciki a jikina" Ridayya ta ce
"Kin san Allah, wallahi ba zan barki ba, kowa ya yi maka kan kara, yi masa na itace" Da gudu Khairy ta juya ta nufi wajan ƙofa ta sunkuya zata buɗe, Ridayya ta sauke mata wuƙar a wuyanta ta ƙara sauke mata a damtsen hannu, Khairy ta gantsare tana kare cikinta don a duniya yanzu ba abinda take so dama da cikinta.
"Jama'a wai ba kowa a gidanne? Zata kashe ni wallahi kashe ni za ta yi matar yayana ta haukace ku kawo mana a gaji" A guje ta buɗe ƙofa ta fita Ridayya ta bita da sauri, daidai nan Zameer na shigowa da Zainaba idanun Ridayya rufe kallon Zameer take tamkar Khairy ce a gabanta. Yana zuwa ya kifa wata wasu lafiyayyun maruka guda biyu sau biyu a jere ta yi taga-taga zata faɗi ta cake waje guda. Khairy itama wuƙar ta ɗakko ta ce "Wallahi ba ki jimi ciwo a banza ba, ƴar ta'adda kawai" Ridayya ta yi murmushi hawaye na fita daga idanunta bakinta na rawa ta ce
"Haka nake so daman, ko dai ki kashe ni ko kuma na kashe ki" Khairy ta ɗaga wuƙar zata kwaɗawa Ridayya a gigice Zainaba ta hankaɗa Zameer tsakiyarsu daidai nan Khairy ta sauke masa wuƙar a mara, ya fasa ihu yana riƙe gabansa saboda wani azaba daya tsarga masa jini ya fara zuba, ya faɗi ƙasa Khairy ta shiga ɗaki ta rufe ta fara haɗa kayanta.
Ganin Zameer kwance a ƙasa cikin jini ya dawo da Ridayya daga hayyacinta, ta rarrafa ta nufi inda yake ta fara jijjiga shi tana kuka tare da furta
"Ka tashi rayuwata, ka yi mini rai kar ka barni a cikin wannan halin da nake ciki" Zainaba ta ce "Ridayya mene ya sameki a fuska? Gobara kukai ta cinye rabin fuskar ko annoba ce ta faÉ—a miki? Zameer kuma ina ruwanki da shi, ai bake kika ji masa ciwon ba ki yi ta kan ki kawai" Wani irin kallo Ridayya ta yi wa Zainaba ta ce
"Ki fita daga rayuwata ki barni haka, mene rayuwarki da gidan aurena da mijina kuma? Kin saka mini ido kin takura ni"
"Ridayya ni kike faɗawa haka saboda kina son maso wani? Makauniyar soyayyar da bata da wata riba wajanki, munafukin mijin naki cima zaune wahalalle maƙaryacin" kuka kawai Ridayya take kafin ta ce "Kima siyar da rayuwa take, soyayya kuma bada rayuwa take, ki saurara mini ki barni ki tsahirta mini...,"
Saukar bulala ta ji ta ko'ina a jikinta, tun yana dukan ta da bulala har ya fara saka ƙafa yana ball da ita tare da taka mata ruwan ciki, daman buta ta ɗauka zata shiga banɗaki ta fasa, azabar bugun mararta da ya yi ta saki kashin wahala a kiɗime take cewa "Na tuba ka yafe mini tausayi ne, don Allah ka da ka kassara mini ɗan cikina" Bai kulata ba, dukanta yake da ko'ina tana ihu da ƙoƙarin guduwa har ta kasa motsi. Zainaba mutanenta na kusa jikinta ya fara rawa da ɓari ta ƙura wa Zameer idanu kafin ta yi ihu ta zube a ƙasa tana surutai.
"Tsinanne maciyaci, mugu macuci ba za mu barka ba, ka zalunci yarinyar jama'a ka ajiyye karuwa a cikin gidanka ƙarya yake ba ƙanwarsa ba ce zaman cin amana suke bashi da kowa a garin nan" Da sauri Zameer ya ce
"Munafukar banza na ci uwar aljanun" Domin ya ɗauka aljanun ƙarya ta yi. Baban hajjo Usman ya yi sallama Zameer ya ce "Yawwa! Babu matarka babu tawa duk abinda na yi mata zunubinta ya ja mata, ba zata raba mini aure na kasa gane kan matata ba" Usman ya ce
"Ai kowa ya yi na gari kansa, daɗin abin ba a duniya za mu tabbata ba" Yana faɗin haka ya kinkimi matarsa sukai waje, Zameer ya shige banɗaki sosai gabansa da mararsa ke masa ciwo har ɗingi shi yake. Yana fitowa ya shiga ɗaki ganin Khairy ya yi tana haɗa kayanta da sauri ya ajjiye wayar hannunsa ya nufi inda take, ta yi saurin kauce wa ta ce "Kar ka taɓa ni, kar ka fara" Zameer ya sauke numfashi yana yin ƙasa da murya.
"Haba dear, ki sassauta hukuncin nan" Khairy ta ce "Wato ni ba ƴa bace saboda ina zaman bariki da kai ko? Wallahi idan kaga ba haƙura ka bi mini hakƙina"
Riƙota ya yi gabaɗaya ya haɗe ta da jikinsa yana sauke mata numfashi a wuya idanunsa a saman kyakkawar fuskarta, a nutse daidai kunnenta ya ce "Za ki iya barina ashe?" Ya faɗa yana fesa mata iska a kunne. Jikinta ya saki sai kawai ta fashe da kuka ta ce
"Ka sauya mini matsayi, ka mayar dani matarka, zan yi istibira'i mu yi aure mu huta da wannan rayuwar na san cewa zaman kishi nake da tsinanniyar matarka mai zubin aljanu"
Hannu ya sa ya matse bakinta a hankali ya ce
"Kar ki mini tsiwa, ke kika bari har tasan da cikin amma nasan me zan yi" daga nan rufe ƙofa sukai abinsu tare da barin Ridayya yashe a ƙasa.
Usman ya ce "Kema Allah ya ƙara ya daɗa, kafirin iyayinki ne ya ja miki wahala" Zainaba na kuka ta ce "Baban hajjo ba zaka gane ba, jin Ridayya nake kamar ƴar'uwata wallahi tausayinta nake ji sosai" Bai ce mata komai ba don baƙin ciki yana jin da shi mai kuɗi ne babu abinda zai hana shi maka Zameer a kotu ko kuma ya kaiwa hisba ƙara. "In sha Allah Zameer sai ya wulaƙanta ba zai taɓa ganin daidai ba, ba kuma zan bar shiga gidan nasa ba"
"Azzalumi ba fa dole sai ya wulaƙanta ba, muddin zai tuba wajan Ubangiji" a fusace ta ce "Banda munafiki irin Zameer wanda shaiɗan ya yi wa fitsari aka".
Sanyin yamma ne ya dawo da Ridayya daga suman da ta yi, ta motsa kaɗan tare da yin ƙara saboda wani nauyi da hannunta ya yi mata, da ƙyar ta miƙe zaune sai a lokacin ta farga da kashin da ta yi, ta runtse idanunta zuciyarta na zafi da raɗaɗi na rashin mafita da abin yi. Ba zata iya tashi ba don haka ta dinga jan jiki zuwa banɗaki ta wanke jikinta tas, kana ta daddafa ta fito tare da haɗa kai da qwiwa ta shiga sauke ajjiyar zuciya wani irin matsanancin tsoran Zameer ya kamata, haka kurum ta shiga razana ita kaɗai, ga ciki a jikinta, ga duka ga wata kafurar yunwa dake mata barazanar raba mata hanji. Tunaninta ya tsaya kwakwalwarta ta gaza yin aikin komai da sarrafa wasu kalaman na Zameer. Bata da burin daya shige zuwa gidansu wajan Mami. A hankali ta miƙe ta saci jiki ta fice daga cikin gidan.
Duk inda ta gilma kallonta ake ana nunata, domin kawo yanzu a wannan sabon zamanin da muke ciki ba kowa zai kai Ridayya gidan miji ba, amma a yarda ake kallon nata da yawa sun ɗauka wata dattijuwar ce. Turus ta yi lokacin da taga gate ɗin gidansu a garƙame, gabanta na faɗuwa wani yaro ta gani, ta ya fito shi da hannu da gudu ya runtuma yana "Wayyo mahaukaciya" Ridayya ta dinga kallon kanta can wata yarinya ta fito daga gidan dake kusa dana su Ridayya, ta ce
"Don Allah masu gidan nan fa?" Yarinya ta kalli Ridayya tana ja da baya ta ce "Sun tafi Rano, sun daÉ—e da tafiya na ji ana siyar da gidan za a yi"
"Siyar da gida? Rano?"
Ridayya ta maimaita a fili, yarinyar tuni ta juya, zama ta dinga yi a wajan abin mamaki duk wanda suka zo shigewa sai su ajjiye mata kuɗi a gabanta, wani irin hawayen baƙin ciki ya ziraro mata a ƙofar gidansu ake bata sadaƙa? Ganin tana samun kuɗi taƙi tafiya har aka kira magriba, ta rarrafa ta miƙe a hanya ta siyi taliya guda ɗaya, da kayan miya da magi da mai. Tana zuwa ta fassakara itace tare da dafa jallof ɗin taliya ta saka daddawa. Zameer da Khairy suna ɗaki suka jiyo ƙamshin abinci nan da nan kwaɗayin masu ciki ya addabi Khairy ta ce "Baby matarka ke girki?"
"Ina ta ga kuÉ—in?" Saboda basu san ta fita ba ta ce "Ka duba please wallahi hankalina duk ya tashi" Ya yi murmushi yana cireta a jikinsa ya ce
"Idan ma ita ce dole zata bani ba zata iya cin abinci banci ba, idan ta bani zan kawo miki" Yana fita ya samu Ridayya na juye taliyar a faranti daman rabi ta dafa, ya tsaya tare da sassauta murya ya ce "Ridayya mai sona girki kike?" Shiru ta yi masa don magana yanzu sai dole ga zugin fuska gana hannu da ƙyar take motsa shi.
"Fushi kike dani? Bari na yi sallah na dawo mu yi magana ki jira ji" A hankali ta ce "To" Yana fita ta saka hannu a faranti ta fara cin taliyar ta cinye tas, saboda baƙar yunwa ta suɗe farantin kana ta yi alwala tare da yin Sallah, hannu ta ɗaga ta rasa wacce kalar addu'a za ta yi sai kawai ta yi shiru.
"Au, ba rami mene ya kawo rami? Kin ji na Amjat zargi? Haka tara, in ji kishiyar mai mageduwa, ai shi ɗa na kowa ne, ƙanwar miji ai ƙanwa ce, dole na ba ki tarbiyya saboda gudun bakin jama'a"
Khairy ta ce "Don Allah ki barni na fita, na je gidanmu babu wani ciki a jikina" Ridayya ta ce
"Kin san Allah, wallahi ba zan barki ba, kowa ya yi maka kan kara, yi masa na itace" Da gudu Khairy ta juya ta nufi wajan ƙofa ta sunkuya zata buɗe, Ridayya ta sauke mata wuƙar a wuyanta ta ƙara sauke mata a damtsen hannu, Khairy ta gantsare tana kare cikinta don a duniya yanzu ba abinda take so dama da cikinta.
"Jama'a wai ba kowa a gidanne? Zata kashe ni wallahi kashe ni za ta yi matar yayana ta haukace ku kawo mana a gaji" A guje ta buɗe ƙofa ta fita Ridayya ta bita da sauri, daidai nan Zameer na shigowa da Zainaba idanun Ridayya rufe kallon Zameer take tamkar Khairy ce a gabanta. Yana zuwa ya kifa wata wasu lafiyayyun maruka guda biyu sau biyu a jere ta yi taga-taga zata faɗi ta cake waje guda. Khairy itama wuƙar ta ɗakko ta ce "Wallahi ba ki jimi ciwo a banza ba, ƴar ta'adda kawai" Ridayya ta yi murmushi hawaye na fita daga idanunta bakinta na rawa ta ce
"Haka nake so daman, ko dai ki kashe ni ko kuma na kashe ki" Khairy ta ɗaga wuƙar zata kwaɗawa Ridayya a gigice Zainaba ta hankaɗa Zameer tsakiyarsu daidai nan Khairy ta sauke masa wuƙar a mara, ya fasa ihu yana riƙe gabansa saboda wani azaba daya tsarga masa jini ya fara zuba, ya faɗi ƙasa Khairy ta shiga ɗaki ta rufe ta fara haɗa kayanta.
Ganin Zameer kwance a ƙasa cikin jini ya dawo da Ridayya daga hayyacinta, ta rarrafa ta nufi inda yake ta fara jijjiga shi tana kuka tare da furta
"Ka tashi rayuwata, ka yi mini rai kar ka barni a cikin wannan halin da nake ciki" Zainaba ta ce "Ridayya mene ya sameki a fuska? Gobara kukai ta cinye rabin fuskar ko annoba ce ta faÉ—a miki? Zameer kuma ina ruwanki da shi, ai bake kika ji masa ciwon ba ki yi ta kan ki kawai" Wani irin kallo Ridayya ta yi wa Zainaba ta ce
"Ki fita daga rayuwata ki barni haka, mene rayuwarki da gidan aurena da mijina kuma? Kin saka mini ido kin takura ni"
"Ridayya ni kike faɗawa haka saboda kina son maso wani? Makauniyar soyayyar da bata da wata riba wajanki, munafukin mijin naki cima zaune wahalalle maƙaryacin" kuka kawai Ridayya take kafin ta ce "Kima siyar da rayuwa take, soyayya kuma bada rayuwa take, ki saurara mini ki barni ki tsahirta mini...,"
Saukar bulala ta ji ta ko'ina a jikinta, tun yana dukan ta da bulala har ya fara saka ƙafa yana ball da ita tare da taka mata ruwan ciki, daman buta ta ɗauka zata shiga banɗaki ta fasa, azabar bugun mararta da ya yi ta saki kashin wahala a kiɗime take cewa "Na tuba ka yafe mini tausayi ne, don Allah ka da ka kassara mini ɗan cikina" Bai kulata ba, dukanta yake da ko'ina tana ihu da ƙoƙarin guduwa har ta kasa motsi. Zainaba mutanenta na kusa jikinta ya fara rawa da ɓari ta ƙura wa Zameer idanu kafin ta yi ihu ta zube a ƙasa tana surutai.
"Tsinanne maciyaci, mugu macuci ba za mu barka ba, ka zalunci yarinyar jama'a ka ajiyye karuwa a cikin gidanka ƙarya yake ba ƙanwarsa ba ce zaman cin amana suke bashi da kowa a garin nan" Da sauri Zameer ya ce
"Munafukar banza na ci uwar aljanun" Domin ya ɗauka aljanun ƙarya ta yi. Baban hajjo Usman ya yi sallama Zameer ya ce "Yawwa! Babu matarka babu tawa duk abinda na yi mata zunubinta ya ja mata, ba zata raba mini aure na kasa gane kan matata ba" Usman ya ce
"Ai kowa ya yi na gari kansa, daɗin abin ba a duniya za mu tabbata ba" Yana faɗin haka ya kinkimi matarsa sukai waje, Zameer ya shige banɗaki sosai gabansa da mararsa ke masa ciwo har ɗingi shi yake. Yana fitowa ya shiga ɗaki ganin Khairy ya yi tana haɗa kayanta da sauri ya ajjiye wayar hannunsa ya nufi inda take, ta yi saurin kauce wa ta ce "Kar ka taɓa ni, kar ka fara" Zameer ya sauke numfashi yana yin ƙasa da murya.
"Haba dear, ki sassauta hukuncin nan" Khairy ta ce "Wato ni ba ƴa bace saboda ina zaman bariki da kai ko? Wallahi idan kaga ba haƙura ka bi mini hakƙina"
Riƙota ya yi gabaɗaya ya haɗe ta da jikinsa yana sauke mata numfashi a wuya idanunsa a saman kyakkawar fuskarta, a nutse daidai kunnenta ya ce "Za ki iya barina ashe?" Ya faɗa yana fesa mata iska a kunne. Jikinta ya saki sai kawai ta fashe da kuka ta ce
"Ka sauya mini matsayi, ka mayar dani matarka, zan yi istibira'i mu yi aure mu huta da wannan rayuwar na san cewa zaman kishi nake da tsinanniyar matarka mai zubin aljanu"
Hannu ya sa ya matse bakinta a hankali ya ce
"Kar ki mini tsiwa, ke kika bari har tasan da cikin amma nasan me zan yi" daga nan rufe ƙofa sukai abinsu tare da barin Ridayya yashe a ƙasa.
Usman ya ce "Kema Allah ya ƙara ya daɗa, kafirin iyayinki ne ya ja miki wahala" Zainaba na kuka ta ce "Baban hajjo ba zaka gane ba, jin Ridayya nake kamar ƴar'uwata wallahi tausayinta nake ji sosai" Bai ce mata komai ba don baƙin ciki yana jin da shi mai kuɗi ne babu abinda zai hana shi maka Zameer a kotu ko kuma ya kaiwa hisba ƙara. "In sha Allah Zameer sai ya wulaƙanta ba zai taɓa ganin daidai ba, ba kuma zan bar shiga gidan nasa ba"
"Azzalumi ba fa dole sai ya wulaƙanta ba, muddin zai tuba wajan Ubangiji" a fusace ta ce "Banda munafiki irin Zameer wanda shaiɗan ya yi wa fitsari aka".
Sanyin yamma ne ya dawo da Ridayya daga suman da ta yi, ta motsa kaɗan tare da yin ƙara saboda wani nauyi da hannunta ya yi mata, da ƙyar ta miƙe zaune sai a lokacin ta farga da kashin da ta yi, ta runtse idanunta zuciyarta na zafi da raɗaɗi na rashin mafita da abin yi. Ba zata iya tashi ba don haka ta dinga jan jiki zuwa banɗaki ta wanke jikinta tas, kana ta daddafa ta fito tare da haɗa kai da qwiwa ta shiga sauke ajjiyar zuciya wani irin matsanancin tsoran Zameer ya kamata, haka kurum ta shiga razana ita kaɗai, ga ciki a jikinta, ga duka ga wata kafurar yunwa dake mata barazanar raba mata hanji. Tunaninta ya tsaya kwakwalwarta ta gaza yin aikin komai da sarrafa wasu kalaman na Zameer. Bata da burin daya shige zuwa gidansu wajan Mami. A hankali ta miƙe ta saci jiki ta fice daga cikin gidan.
Duk inda ta gilma kallonta ake ana nunata, domin kawo yanzu a wannan sabon zamanin da muke ciki ba kowa zai kai Ridayya gidan miji ba, amma a yarda ake kallon nata da yawa sun ɗauka wata dattijuwar ce. Turus ta yi lokacin da taga gate ɗin gidansu a garƙame, gabanta na faɗuwa wani yaro ta gani, ta ya fito shi da hannu da gudu ya runtuma yana "Wayyo mahaukaciya" Ridayya ta dinga kallon kanta can wata yarinya ta fito daga gidan dake kusa dana su Ridayya, ta ce
"Don Allah masu gidan nan fa?" Yarinya ta kalli Ridayya tana ja da baya ta ce "Sun tafi Rano, sun daÉ—e da tafiya na ji ana siyar da gidan za a yi"
"Siyar da gida? Rano?"
Ridayya ta maimaita a fili, yarinyar tuni ta juya, zama ta dinga yi a wajan abin mamaki duk wanda suka zo shigewa sai su ajjiye mata kuɗi a gabanta, wani irin hawayen baƙin ciki ya ziraro mata a ƙofar gidansu ake bata sadaƙa? Ganin tana samun kuɗi taƙi tafiya har aka kira magriba, ta rarrafa ta miƙe a hanya ta siyi taliya guda ɗaya, da kayan miya da magi da mai. Tana zuwa ta fassakara itace tare da dafa jallof ɗin taliya ta saka daddawa. Zameer da Khairy suna ɗaki suka jiyo ƙamshin abinci nan da nan kwaɗayin masu ciki ya addabi Khairy ta ce "Baby matarka ke girki?"
"Ina ta ga kuÉ—in?" Saboda basu san ta fita ba ta ce "Ka duba please wallahi hankalina duk ya tashi" Ya yi murmushi yana cireta a jikinsa ya ce
"Idan ma ita ce dole zata bani ba zata iya cin abinci banci ba, idan ta bani zan kawo miki" Yana fita ya samu Ridayya na juye taliyar a faranti daman rabi ta dafa, ya tsaya tare da sassauta murya ya ce "Ridayya mai sona girki kike?" Shiru ta yi masa don magana yanzu sai dole ga zugin fuska gana hannu da ƙyar take motsa shi.
"Fushi kike dani? Bari na yi sallah na dawo mu yi magana ki jira ji" A hankali ta ce "To" Yana fita ta saka hannu a faranti ta fara cin taliyar ta cinye tas, saboda baƙar yunwa ta suɗe farantin kana ta yi alwala tare da yin Sallah, hannu ta ɗaga ta rasa wacce kalar addu'a za ta yi sai kawai ta yi shiru.