Sashe 106
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yaya you are always telling me cewa Aljannata na ƙarƙashin mijina, biyayya kuma ke bada ita, kin ce mini haƙurin shi ne maganin komai a rayuwa, abinda haƙuri bai baka ba, rashin shi ba zai baka ba, yaya na gino akan wannan kalaman naki. Na tuna keda kan ki kike bani wata kissa lokacin Annabi Muhammad S.W.A kin ce; wata mata mahaifinta ne ko mahaifiyarta babu lafiya, amma taƙi zuwa dubiya saboda mijinta baya gari kuma babu al'amarin waya a zamanin, har daga ƙarshe kika ce an aiko mata cewa mahaifin nata ya rasu, ta yi aike wajan Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce mata ta yi haƙuri ta nemi izinin miji, haka ta haƙura ta yi wa mahaifin nata addu'a tana daga gida, a kaiwa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama wahayin cewa wannan matar Ubangiji ya bata Aljanna.... Me ya sa ba za mu yi koyi da mutanen ƙwarai ba, da bana haƙuri ba zan kawo yanzu cikin gidan Prof ba Yaya ki yi haƙuri na nemi izinin shi" A sanyaye Mahmah ta ce
"Okkk"
Ta juya ta kalli Tajj ta ce "Yaushe zasu ƙarasu da gawar?"
"Not too long, don sun jima da tashi bari na faɗawa wanda ya dace" ta jinjina kai ta ɗauki hijabi ta saka ta gyara parlon da za a saka gawar Sadauki. Tajj ya kira Baffa da Baba ƙarami da Junaid duk ya sanar musu, ya kira ƴan'uwansu na kusa da kuma na nesa ya kira abokan mahaifinsa ya saka aka wallafa rasuwar Sadauki a social media da gidajen rediyo. Da kansa ya kira Prof amma bai ɗauka ba ya masa kira sautarin shurin masaƙi but not respond.
Cikin ƙaramin lokaci gidan Murgayi Alhaji Baita ya cika da jama'a ƴan ta'aziyya hatta Mami da Sisters ɗinta suna gidan da kuma Dada, hadda Zainu da little. Daga baya Balisa da Yaya Zuhura suka shigo tare dasu Abdullahi da Khaliperh su Usman har lokacin kuma Hajja Azizat bata ƙarasu ba. Gida ya cika zuwa su BM USTAZ kawai ake jira.
Sama sama ya fara jin news dalilin breaking news da aka fara sanarwa nan take Allah ya yi wa Hamza Sadauki rasuwa ɗa a wajan Professor ɗan takarar ɗan'majalissa ya rasu ne a ƙasar Japan kamar yadda sanarwa ta je musu, za a yi jana'izarsa idan jirgin dake ɗauke da gawarsa ta ƙarasu aka maƙala photon Sadauki da yake tsaye da voyel fari tas ya yi murmushi idanuna na kallon wani direction ɗin daban ba camera ba. A gigice Prof ya yi cilli da wacce ke kusa da shi ya jawo jallabiya ya saka jikinsa sai rawa da ɓari yake yana ƙokarin ɗaukar key ya fita ta riƙe shi ta ce "Malam ina kake ƙoƙarin zuwa ai ha haka mukai alƙawari da kai ba" idanunsa na shigewa ciki ya ce "kina da hankali kowa? Kina jin ana news cewar ɗana gudu ɗaya tal da na mallaka ya rasu maimakon ki mini jaje sai ki kawo mini rubbish?"
"And so what don ɗanka ya rasu? Ba zai taɓa zama ciwon kaina ba" wani irin mari ya sauke mata yana kaiwa bakinta naushi ta fasa ihu ta ce "Wallahi ka yi kaɗan ka dage ni kamar baka san wacece Ladi ƙarin kunama ba, da kuma abinda zan iya yi?" Idanuna rufe ya zare Belt ya shiga lafta mata tana kururuwa itama ta shiga kai masa duka, suka fara dukan juna kamar rayuwa bariki kodayake bambancin kaɗanne ya mata lilis tare da mata jina-jina ya zari wayata da key ya fita. Duk a hanyar ya fara duba miss calls na jama'a babu adadi ya yi mamakin ganin Hajja Azizat ta kira kuma har an ɗaga yaushe to? Bayan ya san yau gabaɗaya bai waya da ita ba? Yaga kiran Tajj dana shugaban jam'iya har kiran yan'uwansa kiran kowa ya share ya kira number Hajja Azizat yana kira ta ɗauka ta ce.
"Thank God, ina kiranka ka yi mini izinin zuwa gidan yaya ta mini kiran gaggawa ban san meke faruwa ba" Wani irin tausayin matarsa ya kama shi, innocent mace ya cutar haka? Har ɗanta ya rasu amma ta kasa fita ji ya yi hawaye ya cika idanunsa wani irin sonta ya ninku a zuciyarsa da ƙyar ya ce "Jeki yanzu Azizat, Allah ya yi miki Albarka"
Tana shirin fita notification na shigowa wayarta dake gidan nasu akwai Wi-fi bata tsaya duba pictures ɗin da aka turo mata ba da sabuwar number a WhatsApps ta shiga mota, da kanta take driving tunani fal zuciyarta hannunta kuma sai rawa yake. zuwanta da yin parking ɗin motarta ya yi daidai da shigowar motar Ambulance ta tsaya tana kallon ikon, akan idanunta aka fito da gawa rufe da farin yadi a kan wani gado, can taga Dr Riyad ta gane shi sarai babu jimawa wani magidancin mutum ya fito fari tas dashi farinsa ya shige misali ko'ina na fatarsa lub yake da gargasa fuskarsa rufe da mask ya saka baƙin glasses a idanunsa, da kansa ya ja gawar Sadauki zuwa cikin gidan Mother ta bi bayansa da kallo ta kasa tunain komai da ƙyar ta ja ƙafarta zuwa cikin gidan, tana shiga parlo ya ruɗe da koke koken jama'a ta dinga bin kowa da idanu sai kawai ta shiga cikin bedroom ɗin Mahmah ta kwanta Mahmah da Tajj suka biyo bayanta nasiha sosai sukai mata can ta ce "Me ya faru ne?"
"Allah ya amshi Sadauki, Ubangiji ya amsa ran Sadauki ya rasu"
Mother ta rasa gane waye Sadauki wacce kalar mutuwa kuma "Sadauki? Wanne Sadauki?"
"Hamza Sadauki É—anki Azizat"
"Kamar bani da É—a mai suna Sadauki Yaya, wanne Sadauki yaya take nufi Deen?"
Tajj ya ce "Ki yi haƙuri don Allah Anty Sadauki dai ɗanki ɗaya tal ke da Prof"
Ta jinjina kai a hankali ta yi baya ta ce "Allah ya jiƙan shi ya yi masa rahama" daga haka bata kuma cewa komai ba, ta juya baya tare da kwanciya saman gadon babu hawaye ko tashin hankali a tattare da ita amma zuciyarta cak take kwakwalwarta nata processing tuna waye Sadauki? Mene haɗin ta da shi nata sadauki dai baya ƙasar gabaɗaya ai.
Haka al'amarin Ubangiji yake komai da lokacin shi, haka kuma mai rai dole ya ɗanɗani ɗaci mutuwa. Har akai arba'in ɗin Sadauki babu wanda ya ji kukan Hajiya Azizat ta kaɗaice daga cikin jama'a bata son kowa ya raɓe ta. Sau ɗaya suka ji ta fasa ihu a gigice Tajj ya shiga ɗakin ya ganta tana fisge-fisge ta fita hayyacinta idanunta rufe jikinta na rawa Tajj ya ƙarasa wajanta tuni ta doka wayarta da ƙasa wayar ta fashe ta yi fari baka ganin komai, kokawa suke sosai da Tajj da ƙyar ya rungume ta a jikinsa yana hawaye tare da kiran sunan Allah ya fara mata addu'a yana tofa mata, Mahmah ta yi tsaye ta kasa cewa komai makamin yadda Hajja Azizat bata ƙaunar Prof ya zo kusa da ita take, ko ta'aziyyarsa taƙi amsawa ta tambayi dalili ta ce "Me zata cewa wanda ya kashe kiran yaro?" Tun daga lokacin bata kuma cewa komai ba sai sanda ta yi ihun a hankali ta sauke numfashi jikinta ya saki a jikin Tajj ta riƙe shi da kyau kuma. Gabaɗaya sun rasa meke damunta mai kuma ta gani? Suka kira Malami ya fara mata rubutun don gana amma abu ya ci tura.
Umma ta kalli Mardiyya da duk ta yi wani zuru-zuru sai ciki a gaba ta dire mata kuɗi ta ce "My daughter gashi 200k ne ki ƙaro abinda kike so na fitar suna, tunda haihuwa ta zo gab gamu cikin watan haihuwar edd kawai muke jira" Mardiyya ta kalli kuɗin ta ce "Ok thanks"
Ta ce a yatsune kafin ta ce "Hadda Ustaz a masu zuwa ta'aziyyar Sadauki amma kin kasa dawo da shi gida, bakwa tsoron haƙƙina rabona da shi tun ina amarya tun kafin na samu ciki?"
"Kamarya kenan kafin ki samu ciki kuma? Ko dai bayan kin samu ciki?" Cikin inda-inda Mardiyya ta ce "A'a ina nufin kafin nasan da cikin a wajena" murmushi Umma ta yi ta ce "To albishirin ki wannan kuÉ—in shi ne ya turo da su ya ce a ba ki kuma yana nan kan hanya soon" cikin farinciki Diyya ta ce
"Da gaske ko dai ƙarya kike mini Umma?" Da wani mamaki Umma ta ce "Ƙarya kuma Mardiyya?"
"Opps sorry na ruɗe ne, bedside kin jima ai kina ce mini yana hanya, amma dai kafin na haihuwa zai dawo" Umma ta jinjina kai cikin ya yi laushi ta ce "In sha Allah" daga haka ta juya cikin sauri Mardiyya ta kira ƙawarta ta sanar mata komai ta cikin waya ta ce "Saura ki ƙara jakanta irin na baya, tunda brain ɗinki a tushe yake kamar na kifi bayan maganinsu sha'awa ki saka masa wanda zai zama kamar na maye, sai ki yi bidiyo shi zai zama hujja ni kuma zan bayar a yi editing na bidiyon a cire cikin jikinki shi kuma a ɗan rage masa ƙiba, don na lura ya ƙara tumbi da kyau da haske wallahi irin yana cikin kwanciyar hankalin nan" Diyya ta haɗe fuska ta ce "Ban gane ba, mijina ne fa kuma kike yabon ƙyan shi"
"Dilla to mene? Ai kyakkyawa ne"
"Kambu saurara akan shi zan iya rabuwa dake tuni wallahi aikin banza daman haka ku ƴan'matan da kukai kwantai a gida kuke, guzuma" ta ce "Ni kikewa gorin aure Mardiyya? To shikenan kya zauna da Ustaz ɗin na gani" tana faɗin hakan ta kashe wayarta. Baba ƙarami ya dinga ladamar aibata Ustaz da ya yi daman a lokacin ya kasa fahimtar meke faruwa da shi har ya yarda, ya samu nutsuwa ya kuma tambaye shi ya jikin Ridayya da yanayinta ya sanar masa tana lafiya.
Baba ƙarami ya ce "Babban mutum ya kama ka dawo gida haka nan domin asan kana tare da matarka" Ustaz ya sauke ajjiyar zuciya yana janye idanunsa da lumshe su hannunsa ɗaya yana shafa sumar Ridayya dake bacci akan cinyarsa hankali kwance ta zama wata ƙatuwa da ita jikinta ya buɗe sosai kamar an hura ta, ta fresh da ita laɓɓanta jajur dasu ya kasa cewa Baba ƙarami komai.
"Okkk"
Ta juya ta kalli Tajj ta ce "Yaushe zasu ƙarasu da gawar?"
"Not too long, don sun jima da tashi bari na faɗawa wanda ya dace" ta jinjina kai ta ɗauki hijabi ta saka ta gyara parlon da za a saka gawar Sadauki. Tajj ya kira Baffa da Baba ƙarami da Junaid duk ya sanar musu, ya kira ƴan'uwansu na kusa da kuma na nesa ya kira abokan mahaifinsa ya saka aka wallafa rasuwar Sadauki a social media da gidajen rediyo. Da kansa ya kira Prof amma bai ɗauka ba ya masa kira sautarin shurin masaƙi but not respond.
Cikin ƙaramin lokaci gidan Murgayi Alhaji Baita ya cika da jama'a ƴan ta'aziyya hatta Mami da Sisters ɗinta suna gidan da kuma Dada, hadda Zainu da little. Daga baya Balisa da Yaya Zuhura suka shigo tare dasu Abdullahi da Khaliperh su Usman har lokacin kuma Hajja Azizat bata ƙarasu ba. Gida ya cika zuwa su BM USTAZ kawai ake jira.
Sama sama ya fara jin news dalilin breaking news da aka fara sanarwa nan take Allah ya yi wa Hamza Sadauki rasuwa ɗa a wajan Professor ɗan takarar ɗan'majalissa ya rasu ne a ƙasar Japan kamar yadda sanarwa ta je musu, za a yi jana'izarsa idan jirgin dake ɗauke da gawarsa ta ƙarasu aka maƙala photon Sadauki da yake tsaye da voyel fari tas ya yi murmushi idanuna na kallon wani direction ɗin daban ba camera ba. A gigice Prof ya yi cilli da wacce ke kusa da shi ya jawo jallabiya ya saka jikinsa sai rawa da ɓari yake yana ƙokarin ɗaukar key ya fita ta riƙe shi ta ce "Malam ina kake ƙoƙarin zuwa ai ha haka mukai alƙawari da kai ba" idanunsa na shigewa ciki ya ce "kina da hankali kowa? Kina jin ana news cewar ɗana gudu ɗaya tal da na mallaka ya rasu maimakon ki mini jaje sai ki kawo mini rubbish?"
"And so what don ɗanka ya rasu? Ba zai taɓa zama ciwon kaina ba" wani irin mari ya sauke mata yana kaiwa bakinta naushi ta fasa ihu ta ce "Wallahi ka yi kaɗan ka dage ni kamar baka san wacece Ladi ƙarin kunama ba, da kuma abinda zan iya yi?" Idanuna rufe ya zare Belt ya shiga lafta mata tana kururuwa itama ta shiga kai masa duka, suka fara dukan juna kamar rayuwa bariki kodayake bambancin kaɗanne ya mata lilis tare da mata jina-jina ya zari wayata da key ya fita. Duk a hanyar ya fara duba miss calls na jama'a babu adadi ya yi mamakin ganin Hajja Azizat ta kira kuma har an ɗaga yaushe to? Bayan ya san yau gabaɗaya bai waya da ita ba? Yaga kiran Tajj dana shugaban jam'iya har kiran yan'uwansa kiran kowa ya share ya kira number Hajja Azizat yana kira ta ɗauka ta ce.
"Thank God, ina kiranka ka yi mini izinin zuwa gidan yaya ta mini kiran gaggawa ban san meke faruwa ba" Wani irin tausayin matarsa ya kama shi, innocent mace ya cutar haka? Har ɗanta ya rasu amma ta kasa fita ji ya yi hawaye ya cika idanunsa wani irin sonta ya ninku a zuciyarsa da ƙyar ya ce "Jeki yanzu Azizat, Allah ya yi miki Albarka"
Tana shirin fita notification na shigowa wayarta dake gidan nasu akwai Wi-fi bata tsaya duba pictures ɗin da aka turo mata ba da sabuwar number a WhatsApps ta shiga mota, da kanta take driving tunani fal zuciyarta hannunta kuma sai rawa yake. zuwanta da yin parking ɗin motarta ya yi daidai da shigowar motar Ambulance ta tsaya tana kallon ikon, akan idanunta aka fito da gawa rufe da farin yadi a kan wani gado, can taga Dr Riyad ta gane shi sarai babu jimawa wani magidancin mutum ya fito fari tas dashi farinsa ya shige misali ko'ina na fatarsa lub yake da gargasa fuskarsa rufe da mask ya saka baƙin glasses a idanunsa, da kansa ya ja gawar Sadauki zuwa cikin gidan Mother ta bi bayansa da kallo ta kasa tunain komai da ƙyar ta ja ƙafarta zuwa cikin gidan, tana shiga parlo ya ruɗe da koke koken jama'a ta dinga bin kowa da idanu sai kawai ta shiga cikin bedroom ɗin Mahmah ta kwanta Mahmah da Tajj suka biyo bayanta nasiha sosai sukai mata can ta ce "Me ya faru ne?"
"Allah ya amshi Sadauki, Ubangiji ya amsa ran Sadauki ya rasu"
Mother ta rasa gane waye Sadauki wacce kalar mutuwa kuma "Sadauki? Wanne Sadauki?"
"Hamza Sadauki É—anki Azizat"
"Kamar bani da É—a mai suna Sadauki Yaya, wanne Sadauki yaya take nufi Deen?"
Tajj ya ce "Ki yi haƙuri don Allah Anty Sadauki dai ɗanki ɗaya tal ke da Prof"
Ta jinjina kai a hankali ta yi baya ta ce "Allah ya jiƙan shi ya yi masa rahama" daga haka bata kuma cewa komai ba, ta juya baya tare da kwanciya saman gadon babu hawaye ko tashin hankali a tattare da ita amma zuciyarta cak take kwakwalwarta nata processing tuna waye Sadauki? Mene haɗin ta da shi nata sadauki dai baya ƙasar gabaɗaya ai.
Haka al'amarin Ubangiji yake komai da lokacin shi, haka kuma mai rai dole ya ɗanɗani ɗaci mutuwa. Har akai arba'in ɗin Sadauki babu wanda ya ji kukan Hajiya Azizat ta kaɗaice daga cikin jama'a bata son kowa ya raɓe ta. Sau ɗaya suka ji ta fasa ihu a gigice Tajj ya shiga ɗakin ya ganta tana fisge-fisge ta fita hayyacinta idanunta rufe jikinta na rawa Tajj ya ƙarasa wajanta tuni ta doka wayarta da ƙasa wayar ta fashe ta yi fari baka ganin komai, kokawa suke sosai da Tajj da ƙyar ya rungume ta a jikinsa yana hawaye tare da kiran sunan Allah ya fara mata addu'a yana tofa mata, Mahmah ta yi tsaye ta kasa cewa komai makamin yadda Hajja Azizat bata ƙaunar Prof ya zo kusa da ita take, ko ta'aziyyarsa taƙi amsawa ta tambayi dalili ta ce "Me zata cewa wanda ya kashe kiran yaro?" Tun daga lokacin bata kuma cewa komai ba sai sanda ta yi ihun a hankali ta sauke numfashi jikinta ya saki a jikin Tajj ta riƙe shi da kyau kuma. Gabaɗaya sun rasa meke damunta mai kuma ta gani? Suka kira Malami ya fara mata rubutun don gana amma abu ya ci tura.
Umma ta kalli Mardiyya da duk ta yi wani zuru-zuru sai ciki a gaba ta dire mata kuɗi ta ce "My daughter gashi 200k ne ki ƙaro abinda kike so na fitar suna, tunda haihuwa ta zo gab gamu cikin watan haihuwar edd kawai muke jira" Mardiyya ta kalli kuɗin ta ce "Ok thanks"
Ta ce a yatsune kafin ta ce "Hadda Ustaz a masu zuwa ta'aziyyar Sadauki amma kin kasa dawo da shi gida, bakwa tsoron haƙƙina rabona da shi tun ina amarya tun kafin na samu ciki?"
"Kamarya kenan kafin ki samu ciki kuma? Ko dai bayan kin samu ciki?" Cikin inda-inda Mardiyya ta ce "A'a ina nufin kafin nasan da cikin a wajena" murmushi Umma ta yi ta ce "To albishirin ki wannan kuÉ—in shi ne ya turo da su ya ce a ba ki kuma yana nan kan hanya soon" cikin farinciki Diyya ta ce
"Da gaske ko dai ƙarya kike mini Umma?" Da wani mamaki Umma ta ce "Ƙarya kuma Mardiyya?"
"Opps sorry na ruɗe ne, bedside kin jima ai kina ce mini yana hanya, amma dai kafin na haihuwa zai dawo" Umma ta jinjina kai cikin ya yi laushi ta ce "In sha Allah" daga haka ta juya cikin sauri Mardiyya ta kira ƙawarta ta sanar mata komai ta cikin waya ta ce "Saura ki ƙara jakanta irin na baya, tunda brain ɗinki a tushe yake kamar na kifi bayan maganinsu sha'awa ki saka masa wanda zai zama kamar na maye, sai ki yi bidiyo shi zai zama hujja ni kuma zan bayar a yi editing na bidiyon a cire cikin jikinki shi kuma a ɗan rage masa ƙiba, don na lura ya ƙara tumbi da kyau da haske wallahi irin yana cikin kwanciyar hankalin nan" Diyya ta haɗe fuska ta ce "Ban gane ba, mijina ne fa kuma kike yabon ƙyan shi"
"Dilla to mene? Ai kyakkyawa ne"
"Kambu saurara akan shi zan iya rabuwa dake tuni wallahi aikin banza daman haka ku ƴan'matan da kukai kwantai a gida kuke, guzuma" ta ce "Ni kikewa gorin aure Mardiyya? To shikenan kya zauna da Ustaz ɗin na gani" tana faɗin hakan ta kashe wayarta. Baba ƙarami ya dinga ladamar aibata Ustaz da ya yi daman a lokacin ya kasa fahimtar meke faruwa da shi har ya yarda, ya samu nutsuwa ya kuma tambaye shi ya jikin Ridayya da yanayinta ya sanar masa tana lafiya.
Baba ƙarami ya ce "Babban mutum ya kama ka dawo gida haka nan domin asan kana tare da matarka" Ustaz ya sauke ajjiyar zuciya yana janye idanunsa da lumshe su hannunsa ɗaya yana shafa sumar Ridayya dake bacci akan cinyarsa hankali kwance ta zama wata ƙatuwa da ita jikinta ya buɗe sosai kamar an hura ta, ta fresh da ita laɓɓanta jajur dasu ya kasa cewa Baba ƙarami komai.