Sashe 70
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun ranar Ustaz ya ƙauracewa ganin Ridayya baya zama a gidan sosai ita kuma kullum sai ta fito ko zata ganshi abin ya fara damunta ta yi ta kuka ita kaɗai saboda ya yi aure ya daina son ta? Ashe mata tafi ƴa daman? Wani irin zafin Mardiyya take ji a ranta ita har yanzu ta kasa yarda cewa matarsa ce wannan ai cin amana ne kuma tun ranar data gansu rungume da juna bata sake yarda taga Mardiyya ba, bata da abin faɗa mata. Gefe guda kuma suna waya da Sadauki sosai a wayar Hajiya.
Ustaz ya fara neman appointment da likitan kwakwalwar domin a tabbatar ko tana da Mental Illness. Hakan yasa cikin gaggawa ya fara neman hanyar zuwa asibitin Psychiatry domin samun ganin Neurologist a san mene matsalar.
Rana tsaka ya saka Hajiya ta kira Ridayya bai ce mata komai ba ko gaisuwarta bai amsa ba. Bayan tambayoyin da likitan ya yi mata ya buƙaci yi mata photo na ka da yin gwaje-gwaje na kamar su CT scan (Brain hemorrhage) MRI (Stroke, Brain tumor) da EEG (Epilepsy) bayan duk an yi komai ya ce Ustaz ya dawo shi ɗaya washegari Ridayya dai da idanu da kunne take jin komai, ya shige da ita shopping ta baza idanu tana kallon garin Legos gwanin sha'awa abayas ya siya mata underwears komai size ɗinta perfumes, kalar man da aka rubuta mata a bela dake ya ganshi a ɗakin dake gidansu Tajj ribbons, flat shoes. Har sun gama komai taga wasu saitin kaya na maza masu kyau amma ƙanana ta ce
"Abbiey ka siyi wancan zai maka kyau" ya kalli kayan kafin ya yi magana ta ɗakko ta haɗa da wata hula p.cap da wani baƙin glasses ya fahimci Ridayya ita kyalekyale kawai ta sani bai kulata ba ya biya kuɗin.
Har bayan mota aka kai musu ya nufi gida ko ciki bai shiga ba ya juya ya fita yana buƙatar shan iska da samun nutsuwa.
A can Batsari mahaifin Zameer Giɗaɗo ya nema masa auren Hanne cikin ƙaramin lokaci aka ɗaura aka ware mata ɗaki a cikin gidan ta tare kasancewar Allah ya jarabceta da son shi amma duk ya siri mata auren ma fin ƙarfinta akai kullum cikin dare rufe ƙofa take.
Da ƙyar cikin sa a ya samu ƙofar a buɗe, jiki na rawa ya nufeta ta yi saurin ja baya ta ce "Saurara meye haka kamar wani daƙiƙi zaka yo kai na haka dabba ce ni da zaka faɗo mini?"
"Ke kisan da wanda kike magana dole ta saka zan raɓeki a rashin matata ne"
Hanne ta yi shewa ta ce "Wacce matar bayan wacce ka saka kana da wata mata ne ko jikin karuwar taka kake marari? Ashe zuwa birnin na banza ne"
Ya haɗe fuska gabansa na faɗuwa ya ce "Yaushe na saki matar tawa? Kuma ko ki yarda ki karki yarda dole na amshi hakƙina sadaki na biya, ki yi a hankali kafin na tafa miki rasit"
"Ai na zame maka ciwon ido wallahi zama dani dole mutukaraba takalmin kaza, na zama ƙadangaren bakin tulo, ni ba irin Ridayya bace ina da gata yanzu za a ci ubanka hankali kwance"
"Zagina ki kai fa?"
"Allah ya yi mini tsari da zagin mijin karuwa"
Ya sauke murya ya ce "To na ji, amma mu je mu raya daren aurenmu, haba Hannene Hanneta"
Gabaɗaya laɓɓanta ke fusgarsa yadda suke jajur kuma bakin ƙarami sai ya ji yana sha'awar sumbatar bakin. Hanne ta ce "Ni wanka zan yi ma kuma ina buƙatar cin kaza"
Kaya ta cire gabansa ya faɗi Hannen da yake rainawa ita ce haka? Har wani yawu yake haɗiyewa daman a matse yake kullum sai ya yi mafarkin Ridayya da yadda yake jinta zam idan yana tare da ita sai ya ji kamar ba ita bace baƙa mummunan ba. Kawai baya ganin darajarta tun ranar data bashi kanta kuma daman ba wani sonta yake ba.
Hanne ya juya ta sake juyawa tana ƙara rura wutar dake tashi a jikin Zameer idanunsa a rine ya ce "Bari na je na kawo miki kazar, amma ki bari ko ɗan bakinki na sumbata"
Ta zare Idanu ta ce "Hoɗijam! Ni na haɗa baki da kai Allah ya sauwaƙa maza ka kawo kazar dai na baka hakƙinka" a gurguje ya je ya kawo kazar bayan ta cinye tas ta ce "Ya leɓo mata ruwa a tulo ya ɗan fi san yi" Kafin ya dawo ta rufe ƙofa ta sha ruwa abinta kaza ta kwanta ta bi lafiyar katifa sai bacci. A daren Zameer kasa bacci ya yi kamar ya haukace ciwon ciki dana mara banda gizau babu abinda jikin Ridayya ke masa, yasan kuma duk inda take tana hanyar dawowa gare shi. A suba ya haɗa takardu da nufin zuwa Kano siyar da ko filaye uku ne daga cikin filayen Ridayya tunda yanzu shi ne yake da iko da su. Bayan ya shirya ya baza shaddar daya zo da su ya haɗa komai ya duba inda ya ajjiye kuɗin mota suka je nemi inda ka ajjiye ba kuɗi babu alamar su sama sukai ƙasa sukai sai Allah gashi bayan su bashi da ko taro.
Gabaɗaya parlourn ya cika da mutane kowa na familyn yana nan banda mutane huɗu, Ustaz, Ridayya, Hajiya, Mai ran ƙarfe. Cikin fara'a da farin ciki Baffa ya ce
"Allahamdulillah komai ya yi farko yana da ƙarshe, na so ba yanzu zamu bayyana ba amma na kasa jurewa ina buƙatar ganin yarana gabaɗaya su biyun, farin cikin haɗuwar su waje guda ya saka na sa a ka yi mini saukar Alkur'ani akan Ubangiji ya kawo mana ƙarshen komai ya daidaita tsakaninmu har na rabawa kowa alawa da goro to bana komai bane sai na farinciki. Kuma gabaɗayanmu zamu haɗu muje Lagos zuwan bazata"
Junaid ya ce "Baffa ai bamu san ina suke a Lagos ba" Alhji Mansur ya ce "Tajuddeen ya sani"
GabaÉ—aya suka kalli Tajj dake shigowa da mamaki Yaya Balkisu ta ce "Tajj ya san komai?"
"Babu abinda ya sani, infact bai san Ridayya ba bai kuma san muna raye ba, daga baya na buƙaci ganinsa da neman taimakonsa. Ni na bashi picture ɗin Ridayya a nan yake ce mini ya taɓa ganinta sau ɗaya mota ta kusa bugeta, har ya bata kuɗi taƙi amsa daman ita ce Ridayya ɗin? Shima ta tsaya masa a rai haka kurum yana son taimaka mata tun daga ranar ya tsananta bincike a kan Ridayya har zuwa sanda ya je Katsina ya bigeta nine farkon wanda ya faɗawa, kuma na shaida masa kar ya nuna ya santa ko yana da alaƙa da wani nata, duk kuɗin daya kashe mata ni na bayar har wayar daya siya mata domin ina buƙatar na fara ɗaukar ɗawainiyyarta tun yaushe, kuma na hana shi faɗawa Ustaz, nine da kaina na saka ya dinga ɗora photon ɗanta mai sunan Babban mutum a status, kuma ta hanyar ɗora photon muka jawo tunaninsa zuwa Kano akai-akai har mutuwar aurenta na sani, ban san dai abinda ya kaita Katsina ba shi ma Tajj bai sani ba, kuma shi ne ya faɗa mini Ustaz ya ɗauketa sun tafi Lagos to in sha Allah a gobe muma zamu ɗauki hanya gabaɗaya kuma ta jirgi domin ina fargabar shiga mota tafiya irin wannan akwai ban tsoro iyali guda"
Barrister ya ce "Wannan haka ne kuma na yabawa ƙoƙarin Tajuddeen sosai samun aminin ƙwarai kamarsa yana da wahalar gaske mun samu taimakon ƴansanda na rashin binciken mutuwar taku"
"Yanzu a kan ganin Ridayya zaka kashe maƙudan kuɗaɗe na jirgi har wajan mutum goma sha?" Baffa ya kalli Ammi ya ce "Wai Maryam lafiyarki lou ya ci a ce kinfi kowa murna da dawowar Ridayya tunda kunfi kusanci da ita a kan mahaifyarta, kuma ko nawa na kashe a kan Ridayya ban faɗi na yi mata abinda ba lallai ta yafe mini ba, kuma Ubangiji ya hure mini donna kyautatawa iyalina ba laifi bane"
"Haka ne murna ce ta mini yawa Allah ya ƙara arziƙi da wadata, na ce ka haɗa da Burhan shima zai yi farin ciki idan yaga Ridayya". "Babu komai a je da shi ɗin"
Tajj ne ya kira Ustaz ya ce gobe kar ya fita zai zo da mutane masu muhimmanci.
Ustaz ya shaidawa Hajiya zuwa Tajj don bai ɗauki baƙin wasu serious ba, bashi da appointment da kowa a ranar ma yake ƙoƙarin zuwan jin sakamakon gwajin da akaiwa Ridayya.
Yana zaune saman kujerar parlourn ɓangarensa system ce a gabansa yana ɗan operating ɗinta Mardiyya ta shigo sai baza ƙamshi take ya sha atamfa Valisco da ɗauri ta yi sallama bata da tabbacin ya amsa domin bata ji ba, amma ta san ba zai wofintar da sallamar ba. Ta ƙarasa ta zauna tana cewa
"Barka da yamma ka shigo ashe?" Ya jinjina kai bai kalleta ba. "Na kawo maka abincin nan? Tuwon Alkama ne idan ba zaka ka ci ba to ka faÉ—i abinda za a dafa maka"
"No" Kawai ya ce mata a hankali itama idanunsa har yanzu a kan system
Wani irin Mardiyya take ji ta ce "To shayi fa? Ko fura naga kana so"
"Injiwa?"
Sosai ta ji daɗin maganar tasa har ƙasan zuciyarta ta ce "Ai nasan duk abinda kake so a wajan ƴarka Ridayya na ji tun kafin ma ta yi aure kullum sai ta bani labarinka da abinda kake so na abinci da kayan sawa, ka san har cewa ta yi shigarka bai taɓa burgeta ba, kullum kana saka jallabiyya da hirami kana carbi Ustazai basu san komai a soyayya ba, gabaɗaya baku san mene soyayya ba shi ya sa ba zata iya auren Ustaz kamarka ba"
Ya ɗago kai ya kalleta sai ya ɗauke ganinsa zata sake manana ya nuna mata hanyar waje "Idan ina buƙatar abincin zan sanar"
Sai ta ji ba daɗi ta ce "Don Allah ko baka so na ka yi ƙoƙarin kallona a matsayin matarka Ridayya kake so kuma kaga yanzu ai ita bazawara ce, ka ji tausayina da gaske ni ina sonka"
Ustaz ya fara neman appointment da likitan kwakwalwar domin a tabbatar ko tana da Mental Illness. Hakan yasa cikin gaggawa ya fara neman hanyar zuwa asibitin Psychiatry domin samun ganin Neurologist a san mene matsalar.
Rana tsaka ya saka Hajiya ta kira Ridayya bai ce mata komai ba ko gaisuwarta bai amsa ba. Bayan tambayoyin da likitan ya yi mata ya buƙaci yi mata photo na ka da yin gwaje-gwaje na kamar su CT scan (Brain hemorrhage) MRI (Stroke, Brain tumor) da EEG (Epilepsy) bayan duk an yi komai ya ce Ustaz ya dawo shi ɗaya washegari Ridayya dai da idanu da kunne take jin komai, ya shige da ita shopping ta baza idanu tana kallon garin Legos gwanin sha'awa abayas ya siya mata underwears komai size ɗinta perfumes, kalar man da aka rubuta mata a bela dake ya ganshi a ɗakin dake gidansu Tajj ribbons, flat shoes. Har sun gama komai taga wasu saitin kaya na maza masu kyau amma ƙanana ta ce
"Abbiey ka siyi wancan zai maka kyau" ya kalli kayan kafin ya yi magana ta ɗakko ta haɗa da wata hula p.cap da wani baƙin glasses ya fahimci Ridayya ita kyalekyale kawai ta sani bai kulata ba ya biya kuɗin.
Har bayan mota aka kai musu ya nufi gida ko ciki bai shiga ba ya juya ya fita yana buƙatar shan iska da samun nutsuwa.
A can Batsari mahaifin Zameer Giɗaɗo ya nema masa auren Hanne cikin ƙaramin lokaci aka ɗaura aka ware mata ɗaki a cikin gidan ta tare kasancewar Allah ya jarabceta da son shi amma duk ya siri mata auren ma fin ƙarfinta akai kullum cikin dare rufe ƙofa take.
Da ƙyar cikin sa a ya samu ƙofar a buɗe, jiki na rawa ya nufeta ta yi saurin ja baya ta ce "Saurara meye haka kamar wani daƙiƙi zaka yo kai na haka dabba ce ni da zaka faɗo mini?"
"Ke kisan da wanda kike magana dole ta saka zan raɓeki a rashin matata ne"
Hanne ta yi shewa ta ce "Wacce matar bayan wacce ka saka kana da wata mata ne ko jikin karuwar taka kake marari? Ashe zuwa birnin na banza ne"
Ya haɗe fuska gabansa na faɗuwa ya ce "Yaushe na saki matar tawa? Kuma ko ki yarda ki karki yarda dole na amshi hakƙina sadaki na biya, ki yi a hankali kafin na tafa miki rasit"
"Ai na zame maka ciwon ido wallahi zama dani dole mutukaraba takalmin kaza, na zama ƙadangaren bakin tulo, ni ba irin Ridayya bace ina da gata yanzu za a ci ubanka hankali kwance"
"Zagina ki kai fa?"
"Allah ya yi mini tsari da zagin mijin karuwa"
Ya sauke murya ya ce "To na ji, amma mu je mu raya daren aurenmu, haba Hannene Hanneta"
Gabaɗaya laɓɓanta ke fusgarsa yadda suke jajur kuma bakin ƙarami sai ya ji yana sha'awar sumbatar bakin. Hanne ta ce "Ni wanka zan yi ma kuma ina buƙatar cin kaza"
Kaya ta cire gabansa ya faɗi Hannen da yake rainawa ita ce haka? Har wani yawu yake haɗiyewa daman a matse yake kullum sai ya yi mafarkin Ridayya da yadda yake jinta zam idan yana tare da ita sai ya ji kamar ba ita bace baƙa mummunan ba. Kawai baya ganin darajarta tun ranar data bashi kanta kuma daman ba wani sonta yake ba.
Hanne ya juya ta sake juyawa tana ƙara rura wutar dake tashi a jikin Zameer idanunsa a rine ya ce "Bari na je na kawo miki kazar, amma ki bari ko ɗan bakinki na sumbata"
Ta zare Idanu ta ce "Hoɗijam! Ni na haɗa baki da kai Allah ya sauwaƙa maza ka kawo kazar dai na baka hakƙinka" a gurguje ya je ya kawo kazar bayan ta cinye tas ta ce "Ya leɓo mata ruwa a tulo ya ɗan fi san yi" Kafin ya dawo ta rufe ƙofa ta sha ruwa abinta kaza ta kwanta ta bi lafiyar katifa sai bacci. A daren Zameer kasa bacci ya yi kamar ya haukace ciwon ciki dana mara banda gizau babu abinda jikin Ridayya ke masa, yasan kuma duk inda take tana hanyar dawowa gare shi. A suba ya haɗa takardu da nufin zuwa Kano siyar da ko filaye uku ne daga cikin filayen Ridayya tunda yanzu shi ne yake da iko da su. Bayan ya shirya ya baza shaddar daya zo da su ya haɗa komai ya duba inda ya ajjiye kuɗin mota suka je nemi inda ka ajjiye ba kuɗi babu alamar su sama sukai ƙasa sukai sai Allah gashi bayan su bashi da ko taro.
Gabaɗaya parlourn ya cika da mutane kowa na familyn yana nan banda mutane huɗu, Ustaz, Ridayya, Hajiya, Mai ran ƙarfe. Cikin fara'a da farin ciki Baffa ya ce
"Allahamdulillah komai ya yi farko yana da ƙarshe, na so ba yanzu zamu bayyana ba amma na kasa jurewa ina buƙatar ganin yarana gabaɗaya su biyun, farin cikin haɗuwar su waje guda ya saka na sa a ka yi mini saukar Alkur'ani akan Ubangiji ya kawo mana ƙarshen komai ya daidaita tsakaninmu har na rabawa kowa alawa da goro to bana komai bane sai na farinciki. Kuma gabaɗayanmu zamu haɗu muje Lagos zuwan bazata"
Junaid ya ce "Baffa ai bamu san ina suke a Lagos ba" Alhji Mansur ya ce "Tajuddeen ya sani"
GabaÉ—aya suka kalli Tajj dake shigowa da mamaki Yaya Balkisu ta ce "Tajj ya san komai?"
"Babu abinda ya sani, infact bai san Ridayya ba bai kuma san muna raye ba, daga baya na buƙaci ganinsa da neman taimakonsa. Ni na bashi picture ɗin Ridayya a nan yake ce mini ya taɓa ganinta sau ɗaya mota ta kusa bugeta, har ya bata kuɗi taƙi amsa daman ita ce Ridayya ɗin? Shima ta tsaya masa a rai haka kurum yana son taimaka mata tun daga ranar ya tsananta bincike a kan Ridayya har zuwa sanda ya je Katsina ya bigeta nine farkon wanda ya faɗawa, kuma na shaida masa kar ya nuna ya santa ko yana da alaƙa da wani nata, duk kuɗin daya kashe mata ni na bayar har wayar daya siya mata domin ina buƙatar na fara ɗaukar ɗawainiyyarta tun yaushe, kuma na hana shi faɗawa Ustaz, nine da kaina na saka ya dinga ɗora photon ɗanta mai sunan Babban mutum a status, kuma ta hanyar ɗora photon muka jawo tunaninsa zuwa Kano akai-akai har mutuwar aurenta na sani, ban san dai abinda ya kaita Katsina ba shi ma Tajj bai sani ba, kuma shi ne ya faɗa mini Ustaz ya ɗauketa sun tafi Lagos to in sha Allah a gobe muma zamu ɗauki hanya gabaɗaya kuma ta jirgi domin ina fargabar shiga mota tafiya irin wannan akwai ban tsoro iyali guda"
Barrister ya ce "Wannan haka ne kuma na yabawa ƙoƙarin Tajuddeen sosai samun aminin ƙwarai kamarsa yana da wahalar gaske mun samu taimakon ƴansanda na rashin binciken mutuwar taku"
"Yanzu a kan ganin Ridayya zaka kashe maƙudan kuɗaɗe na jirgi har wajan mutum goma sha?" Baffa ya kalli Ammi ya ce "Wai Maryam lafiyarki lou ya ci a ce kinfi kowa murna da dawowar Ridayya tunda kunfi kusanci da ita a kan mahaifyarta, kuma ko nawa na kashe a kan Ridayya ban faɗi na yi mata abinda ba lallai ta yafe mini ba, kuma Ubangiji ya hure mini donna kyautatawa iyalina ba laifi bane"
"Haka ne murna ce ta mini yawa Allah ya ƙara arziƙi da wadata, na ce ka haɗa da Burhan shima zai yi farin ciki idan yaga Ridayya". "Babu komai a je da shi ɗin"
Tajj ne ya kira Ustaz ya ce gobe kar ya fita zai zo da mutane masu muhimmanci.
Ustaz ya shaidawa Hajiya zuwa Tajj don bai ɗauki baƙin wasu serious ba, bashi da appointment da kowa a ranar ma yake ƙoƙarin zuwan jin sakamakon gwajin da akaiwa Ridayya.
Yana zaune saman kujerar parlourn ɓangarensa system ce a gabansa yana ɗan operating ɗinta Mardiyya ta shigo sai baza ƙamshi take ya sha atamfa Valisco da ɗauri ta yi sallama bata da tabbacin ya amsa domin bata ji ba, amma ta san ba zai wofintar da sallamar ba. Ta ƙarasa ta zauna tana cewa
"Barka da yamma ka shigo ashe?" Ya jinjina kai bai kalleta ba. "Na kawo maka abincin nan? Tuwon Alkama ne idan ba zaka ka ci ba to ka faÉ—i abinda za a dafa maka"
"No" Kawai ya ce mata a hankali itama idanunsa har yanzu a kan system
Wani irin Mardiyya take ji ta ce "To shayi fa? Ko fura naga kana so"
"Injiwa?"
Sosai ta ji daɗin maganar tasa har ƙasan zuciyarta ta ce "Ai nasan duk abinda kake so a wajan ƴarka Ridayya na ji tun kafin ma ta yi aure kullum sai ta bani labarinka da abinda kake so na abinci da kayan sawa, ka san har cewa ta yi shigarka bai taɓa burgeta ba, kullum kana saka jallabiyya da hirami kana carbi Ustazai basu san komai a soyayya ba, gabaɗaya baku san mene soyayya ba shi ya sa ba zata iya auren Ustaz kamarka ba"
Ya ɗago kai ya kalleta sai ya ɗauke ganinsa zata sake manana ya nuna mata hanyar waje "Idan ina buƙatar abincin zan sanar"
Sai ta ji ba daɗi ta ce "Don Allah ko baka so na ka yi ƙoƙarin kallona a matsayin matarka Ridayya kake so kuma kaga yanzu ai ita bazawara ce, ka ji tausayina da gaske ni ina sonka"