Sashe 14
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwana biyu da faruwar lamarin Ustaz na zaune a parlon gidansa ko wajan aiki ya kasa zuwa, haka kurum ya ji faɗuwar gaba na ruskarsa, fargaba da tsoran da basu da masaniyar komai a kan wanzuwar su a zuciyarsa suka shiga ratsa shi. Ya rufe idanu sai ya buɗe da sauri shi kaɗai amma duk a firgice yake dukda ƙoƙarin riƙe kansa da yake da kyau da gudun hana faruwar tashin ciwonsa. Wayarsa ya ɗauka yaga Baffa ne last wanda ya kira shi sai kuma a lokacin ya lura da saƙon Baffa dalilin notification dake alamta masa zuwan saƙon. Kai tsaye number Baffa ya kira amma baturiyar wayar na zayyana masa wayar a kashe take. Ustaz ya yi shiru yana sauke numfashi can ƙasa zuciyarsa kuma sunan Allah yake kiran a kan ya sassauta masa fargabar dake shirin tarwatsa masa zuciya ya miƙe tsaye a hankali ya ce "Ya Allah, Rabbi inni lima anzalta min khairin faƙir..." Number Baba ƙarami ya kira itama ƴar'uwar ɗayar ce duk a kashe ya koma da baya kamar zai zauna sai kuma ya tsaya saƙon da Baffa ya tura masa ya buɗe, ya ware idanu ƙirjinsa na dukan tara-tara a hankali ya fara bin abinda saƙon ke cewa.
_Muhammad-Bilal zan so wannan maganar na yi ta ga-ni ga-ka babu mamaki zaka fi fahimtar hali da raunin da zuciyata take ciki, faɗar kalmar ban yi wa Ridayya adalci a rayuwa ba wannan kuskure ne, ina tunanin ta zaɓi rabuwa dani ne bisa ga abubuwan da suka faru a baya, Bilal girma muke nasan cewa mutuwa da rayuwa na Allah ne, amma babu tabbacin ganin gobe balle jibi balle kuma sanda zamu dawo daidai da Ridayya, Kullum Baffa take ce mini bata taɓa guduna ba, a wannan karan Ridayya ta zaɓi rayuwa da mijinta a kaina, bata ƙaunar ganina ta ce kar mu sake nemanta, ba zan wa Ridayya baki ba balle hakan ya haddasa ƙara lalacewarta. Muhammad-Bilal, Abbiey kullum Ridayya ke kiranka tun tana ƙarama har ta girma, sai daga baya ta fahimci ba kai ka haifeta ba...,_
Kasa ƙarasa karatun Ustaz ya yi saboda ƙafewar da yawon bakinsa ya yi, ruwa mai sanyi ya ɗauka ya sha kana ya kira number Junaid itama a kashe a fili ya ce "Ya Allah!"
Ya koma tare da ci-gaba da duba saƙon Baffa wanda yake tamkar wasiyya ce ga Ustaz ɗin
_Ka ci-gaba da zama a matsayin Uba kuma jigo a rayuwarta, Bilal don Allah don Allah ka duba girman Allah ka bawa Mamana rayuwa mai kyau idan har mijinta bai kasheta ba, ka bata karatun data rasa a baya ka tabbatar bata sake kuka ba, sai yanzu na fahimci ba Ridayya ta yi kuskure ba, mune mukai muna muka bata lasisin zaɓar wanda ya fi mata muhimmaci a rayuwarta, Bilal, Muhammad-Bilal, Ustaz Ridayya taka ce amace yanzu a wajanka na bar maka ita halak malak har abada, da zarar mun dawo daka Rano duk zan raba auren su wanda bai yi mini wata rana ba, zan bata mijin da yanzu fitila ta haska mini da cewa; shi ne ya fi cancanta da rayuwarta, ba zance umarni nake baka ba, ba kuma zance saƙon zuciya zuwa zuciya bane, ina da yaƙinin cewa wannan ɗin tamkar WASIYYA ce, rashin tabbaci kawai nake da shi, Na barka lafiya yanzu zamu ɗauki hanyar zuwa Rano duba kakarku_
Tunda Ustaz yake a rayuwa bai taɓa shiga halin daya shiga irin yanzu ba, rana mafi dana sani a rayuwarsa shi ne ranar auren Ridayya, sai yanzu da wannan ranar take bin bayanta suka zama tagwaye. Zufa ta dinga yanko masa jiri ya shiga ɗaukarsa. Da sauri ya fara dubawa ko zai samu jirgin da zai kai shi ya isa Ranon? Cikin dare ko gama kimtsa wa bai yi ba ya nufi garin Rano. Mamakinsa bai shige ganin babu wani ahhali ko guda ɗaya ba, sai Hajiya wacce jikin nata yake da sauƙi ta sa shi gaba da tsokana ya fara tsofa babu aure.
"Hajiya su Baffa?" Ta ɗan yi sak sai kuma ta ce "Mun yi waya da su, tun kwanaki biyu baya ya ce sun taho amma har yanzu shiru" Mai ran ƙarfe ya ce "Babu mamaki ɗaga tafiyar sukai domin umarni na bayar a tattaro mini kowa a zo da shi, har da wannan yarinyar mai kama da baƙar tukunya rabo na da ita tun tana shan nono babu wanda nake kwaɗayin gani sai ita" Ustaz ya ce "Baku sake waya ba?" Ta ce "A'a, mene damuwar wai suna nan tafe In sha Allah" Ustaz ya girgiza kai sai kuma ya miƙe ya fice, number maƙocinsu ya kira ka ce ai kwanansu biyu da yini da tafiya, tashin hankali ya ƙara shigar Ustaz duk inda zai bincika labarin hatsari wanda baya fatan ace haka ɗinne ya yi amma ba wani labarai da suke yawo ba hatsari daga Kano zuwa Rano, Asibiti zuwa asibiti ya dinga dubawa har mutuware amma shiru.
Watan uku da yunƙurin zuwan Ridayya gida wanda Zameer ya yi munafurci ta fasa kenan. Tana zaune banda mugwayen mafarkai babu abinda take yi. Kwaɗon kwaki ne a gabanta wanda ta baɗa masa gishiri ta kasa ci, Zameer ya ɗaga labule daga waje yana ƙare mata kallo ya ce "Ga kayan wanki na nan" Kai kawai ta jinjina ya ƙanƙantar da idanunsa cike da masifa ya ce
"Ba'a yi mini magana da kai, nikam ba a yi mini ban so" A hankali muryarta bata fita sosai ta ce "To, kuɗin Omo da ruwa" Ya ɓata fuska ya ce "Nan fa ɗaya, ki ranta mini ruwa kuma ki shiga gidan matar can ki ja a rijiya" Da jemammun idanunta kawai take kallonsa magana ma bata ƙaunar yi ko kaɗan "Kana gani bani da lafiya ka tausaya mini mana, Khairiyya ta ja ruwan" Ya zaro idanu waje sosai ta ce "Tamɗijam! Lallai kin samu matsala ki duba fatarki ki duba da baby Khairy ɗaya ce? Farar fata ai bata san wahala ba, kuma ke aure kike bautar aure za ki fa Ridayya ladanki yana wajan Allah"
Ya girgiza kai yana riƙe ƙugu ya ce "Kambu to na saka Khairy jan ruwan guga ai Ubangiji ba zai yafe mini ba, saboda na ci zarafin kyakkawar halitta, ko aure ta yi mijinta ya ce ta ɗakko wallahi ubansa zan ci" Yar da yake magana haka take binsa da kallo zuciyarta fal mamakin abu biyu, baby Khairy, ko aure ta yi zai ci uban miji cike da damuwa ta ce
"Aure baya nufin bautar da mace Rayuwata, biyayyar gidan miji ai ba bauta ba ce" Ya É—aga kafaÉ—unsa ya ce "A to!" Ya zuciya sai fita ta ce
"Ashe Khairy baby ce kuma yanzu?" Ya tsaya turus gabansa na faÉ—uwa ya ce "E, haka babanmu ke ce mata baby saboda mugun kyan da take da shi, she's so romantic"
Duk da ilimin Ridayya bai yi zurfi ba ta fahimci me yake nufi ya ce "Ki aro iron ki goge mini"
Ya fita domin burinsa bai huce ya ciwo maƙudan kuɗaɗen da aka zuba a caca ba. Zanin wata atamfarta ruwan huda ta yafa ta ɗauki bokici ta shiga gidan Zainaba. Zainaba na zaune tana kaɗa miyar abincin dare ta ce "Wai ikon Allah yau kuma" murmushi Ridayya ta yi dugun bakinta ya washe haƙora suka fito kamar ƴar shekaru 50 don tsofa.
"Mara ba lallai yanzu muke maganarki ni da Baban hajjo, yana jira ki bani labari na je na bashi har da mafarki na yi jiya" Ridayya ba ta yi magana ba. Can ta ce "Ruwan zan ɗiba" Zainaba ta ƙura mata ido sai bata ce komai ta ce "Zan saka Almajiri ya kawo miki, zauna kici abinci" Ta girgiza kai "Allhamdulillah na ƙoshi" Zainaba ta miƙe ta zuba mata tuwon samo har da bushsshen kifi ta shimfiɗa tabarma ta ce "Yau banga abinda zai saka ki fita kibar gidan nan ba" Dole Ridayya ta zauna ta fara cin tuwon hannu baka hannu ƙwarya ta kawo mata kwaɗon zugala domin jinin jikinta ya dawo harda yanka mata dafaffen ƙwai kafin ta gama ci Almajiri ya fara kaiwa Ridayya ruwan.
"Ciki ne dake Ridayya"
Ridayya ta zaro Idanu waje ta ce "Ciki kuma?" Murmushi kawai Zainaba ta yi ta ce "Wallahi ciki gare ki na jima da fahimta, kamar yar da na fahimci Khairy ma ta haɗiyi wake" Ridayya bata gane irin wannan maganganun ta ce "Haɗiyar wake kuma? Kamar yaya" Zainaba ta ce "Za ki gani ai shi ɗan duma ne watarana zai fallasa kan shi, ƙwai zai fashe warinsa ya adabin uban kowa musamman mamallakinsa" Ridayya ta yi shiru "Ki bani labarin tunda kin shigo mini yau"
"Wannan labari" Zainaba ta ce "Shi fa, wallahi na ƙagu" Ridayya ta lumshe idanunta hawayen dake ciki ya sakko a nutse ta ce "Ta ina zan fara? Labarin Ridayya mai girma ne, girman da ko wacce ɗiya mace musamman budurwa da matar aure jinsa zai yi mata amfani" Ta yi jim "Rayuwata a wajan Amma zan faɗa miki? Ko zamana da Abbiey zan labarta miki? Ko kuma juya mini baya da mahaifina ya yi ne zai zama farkon labarin ko haɗuwata da Zameer?" Zainaba ta kawo kujera ta zauna ta yi taƙumi ta ce "Fara mini ta farko yadda zan fahimta" murmushi kawai Ridayya ta ce "Taya zan ba ki labarin abinda bana duniya ya faru sai dai abinda aka bani labari zan iya" Zainaba ta ce "Yawwa ai farkon zai fi citta ƙila shi ne soyayyar Baffa da Mami ko?"
_Muhammad-Bilal zan so wannan maganar na yi ta ga-ni ga-ka babu mamaki zaka fi fahimtar hali da raunin da zuciyata take ciki, faɗar kalmar ban yi wa Ridayya adalci a rayuwa ba wannan kuskure ne, ina tunanin ta zaɓi rabuwa dani ne bisa ga abubuwan da suka faru a baya, Bilal girma muke nasan cewa mutuwa da rayuwa na Allah ne, amma babu tabbacin ganin gobe balle jibi balle kuma sanda zamu dawo daidai da Ridayya, Kullum Baffa take ce mini bata taɓa guduna ba, a wannan karan Ridayya ta zaɓi rayuwa da mijinta a kaina, bata ƙaunar ganina ta ce kar mu sake nemanta, ba zan wa Ridayya baki ba balle hakan ya haddasa ƙara lalacewarta. Muhammad-Bilal, Abbiey kullum Ridayya ke kiranka tun tana ƙarama har ta girma, sai daga baya ta fahimci ba kai ka haifeta ba...,_
Kasa ƙarasa karatun Ustaz ya yi saboda ƙafewar da yawon bakinsa ya yi, ruwa mai sanyi ya ɗauka ya sha kana ya kira number Junaid itama a kashe a fili ya ce "Ya Allah!"
Ya koma tare da ci-gaba da duba saƙon Baffa wanda yake tamkar wasiyya ce ga Ustaz ɗin
_Ka ci-gaba da zama a matsayin Uba kuma jigo a rayuwarta, Bilal don Allah don Allah ka duba girman Allah ka bawa Mamana rayuwa mai kyau idan har mijinta bai kasheta ba, ka bata karatun data rasa a baya ka tabbatar bata sake kuka ba, sai yanzu na fahimci ba Ridayya ta yi kuskure ba, mune mukai muna muka bata lasisin zaɓar wanda ya fi mata muhimmaci a rayuwarta, Bilal, Muhammad-Bilal, Ustaz Ridayya taka ce amace yanzu a wajanka na bar maka ita halak malak har abada, da zarar mun dawo daka Rano duk zan raba auren su wanda bai yi mini wata rana ba, zan bata mijin da yanzu fitila ta haska mini da cewa; shi ne ya fi cancanta da rayuwarta, ba zance umarni nake baka ba, ba kuma zance saƙon zuciya zuwa zuciya bane, ina da yaƙinin cewa wannan ɗin tamkar WASIYYA ce, rashin tabbaci kawai nake da shi, Na barka lafiya yanzu zamu ɗauki hanyar zuwa Rano duba kakarku_
Tunda Ustaz yake a rayuwa bai taɓa shiga halin daya shiga irin yanzu ba, rana mafi dana sani a rayuwarsa shi ne ranar auren Ridayya, sai yanzu da wannan ranar take bin bayanta suka zama tagwaye. Zufa ta dinga yanko masa jiri ya shiga ɗaukarsa. Da sauri ya fara dubawa ko zai samu jirgin da zai kai shi ya isa Ranon? Cikin dare ko gama kimtsa wa bai yi ba ya nufi garin Rano. Mamakinsa bai shige ganin babu wani ahhali ko guda ɗaya ba, sai Hajiya wacce jikin nata yake da sauƙi ta sa shi gaba da tsokana ya fara tsofa babu aure.
"Hajiya su Baffa?" Ta ɗan yi sak sai kuma ta ce "Mun yi waya da su, tun kwanaki biyu baya ya ce sun taho amma har yanzu shiru" Mai ran ƙarfe ya ce "Babu mamaki ɗaga tafiyar sukai domin umarni na bayar a tattaro mini kowa a zo da shi, har da wannan yarinyar mai kama da baƙar tukunya rabo na da ita tun tana shan nono babu wanda nake kwaɗayin gani sai ita" Ustaz ya ce "Baku sake waya ba?" Ta ce "A'a, mene damuwar wai suna nan tafe In sha Allah" Ustaz ya girgiza kai sai kuma ya miƙe ya fice, number maƙocinsu ya kira ka ce ai kwanansu biyu da yini da tafiya, tashin hankali ya ƙara shigar Ustaz duk inda zai bincika labarin hatsari wanda baya fatan ace haka ɗinne ya yi amma ba wani labarai da suke yawo ba hatsari daga Kano zuwa Rano, Asibiti zuwa asibiti ya dinga dubawa har mutuware amma shiru.
Watan uku da yunƙurin zuwan Ridayya gida wanda Zameer ya yi munafurci ta fasa kenan. Tana zaune banda mugwayen mafarkai babu abinda take yi. Kwaɗon kwaki ne a gabanta wanda ta baɗa masa gishiri ta kasa ci, Zameer ya ɗaga labule daga waje yana ƙare mata kallo ya ce "Ga kayan wanki na nan" Kai kawai ta jinjina ya ƙanƙantar da idanunsa cike da masifa ya ce
"Ba'a yi mini magana da kai, nikam ba a yi mini ban so" A hankali muryarta bata fita sosai ta ce "To, kuɗin Omo da ruwa" Ya ɓata fuska ya ce "Nan fa ɗaya, ki ranta mini ruwa kuma ki shiga gidan matar can ki ja a rijiya" Da jemammun idanunta kawai take kallonsa magana ma bata ƙaunar yi ko kaɗan "Kana gani bani da lafiya ka tausaya mini mana, Khairiyya ta ja ruwan" Ya zaro idanu waje sosai ta ce "Tamɗijam! Lallai kin samu matsala ki duba fatarki ki duba da baby Khairy ɗaya ce? Farar fata ai bata san wahala ba, kuma ke aure kike bautar aure za ki fa Ridayya ladanki yana wajan Allah"
Ya girgiza kai yana riƙe ƙugu ya ce "Kambu to na saka Khairy jan ruwan guga ai Ubangiji ba zai yafe mini ba, saboda na ci zarafin kyakkawar halitta, ko aure ta yi mijinta ya ce ta ɗakko wallahi ubansa zan ci" Yar da yake magana haka take binsa da kallo zuciyarta fal mamakin abu biyu, baby Khairy, ko aure ta yi zai ci uban miji cike da damuwa ta ce
"Aure baya nufin bautar da mace Rayuwata, biyayyar gidan miji ai ba bauta ba ce" Ya É—aga kafaÉ—unsa ya ce "A to!" Ya zuciya sai fita ta ce
"Ashe Khairy baby ce kuma yanzu?" Ya tsaya turus gabansa na faÉ—uwa ya ce "E, haka babanmu ke ce mata baby saboda mugun kyan da take da shi, she's so romantic"
Duk da ilimin Ridayya bai yi zurfi ba ta fahimci me yake nufi ya ce "Ki aro iron ki goge mini"
Ya fita domin burinsa bai huce ya ciwo maƙudan kuɗaɗen da aka zuba a caca ba. Zanin wata atamfarta ruwan huda ta yafa ta ɗauki bokici ta shiga gidan Zainaba. Zainaba na zaune tana kaɗa miyar abincin dare ta ce "Wai ikon Allah yau kuma" murmushi Ridayya ta yi dugun bakinta ya washe haƙora suka fito kamar ƴar shekaru 50 don tsofa.
"Mara ba lallai yanzu muke maganarki ni da Baban hajjo, yana jira ki bani labari na je na bashi har da mafarki na yi jiya" Ridayya ba ta yi magana ba. Can ta ce "Ruwan zan ɗiba" Zainaba ta ƙura mata ido sai bata ce komai ta ce "Zan saka Almajiri ya kawo miki, zauna kici abinci" Ta girgiza kai "Allhamdulillah na ƙoshi" Zainaba ta miƙe ta zuba mata tuwon samo har da bushsshen kifi ta shimfiɗa tabarma ta ce "Yau banga abinda zai saka ki fita kibar gidan nan ba" Dole Ridayya ta zauna ta fara cin tuwon hannu baka hannu ƙwarya ta kawo mata kwaɗon zugala domin jinin jikinta ya dawo harda yanka mata dafaffen ƙwai kafin ta gama ci Almajiri ya fara kaiwa Ridayya ruwan.
"Ciki ne dake Ridayya"
Ridayya ta zaro Idanu waje ta ce "Ciki kuma?" Murmushi kawai Zainaba ta yi ta ce "Wallahi ciki gare ki na jima da fahimta, kamar yar da na fahimci Khairy ma ta haɗiyi wake" Ridayya bata gane irin wannan maganganun ta ce "Haɗiyar wake kuma? Kamar yaya" Zainaba ta ce "Za ki gani ai shi ɗan duma ne watarana zai fallasa kan shi, ƙwai zai fashe warinsa ya adabin uban kowa musamman mamallakinsa" Ridayya ta yi shiru "Ki bani labarin tunda kin shigo mini yau"
"Wannan labari" Zainaba ta ce "Shi fa, wallahi na ƙagu" Ridayya ta lumshe idanunta hawayen dake ciki ya sakko a nutse ta ce "Ta ina zan fara? Labarin Ridayya mai girma ne, girman da ko wacce ɗiya mace musamman budurwa da matar aure jinsa zai yi mata amfani" Ta yi jim "Rayuwata a wajan Amma zan faɗa miki? Ko zamana da Abbiey zan labarta miki? Ko kuma juya mini baya da mahaifina ya yi ne zai zama farkon labarin ko haɗuwata da Zameer?" Zainaba ta kawo kujera ta zauna ta yi taƙumi ta ce "Fara mini ta farko yadda zan fahimta" murmushi kawai Ridayya ta ce "Taya zan ba ki labarin abinda bana duniya ya faru sai dai abinda aka bani labari zan iya" Zainaba ta ce "Yawwa ai farkon zai fi citta ƙila shi ne soyayyar Baffa da Mami ko?"