Sashe 28
Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A...aaa.. Abbiey, Abbiey"
Furucin ya yi fitar gurbi daga cikin bakinta, ba tare data san waye a wajan ba, azaba ta saka babu sunan wanda ya zo bakinta da tunaninta sai na Abbiey.
Ustaz ya juyo da sauri har hiramin kansa na faÉ—uwa, idanunsa da suke kodayaushe a rufe ya sauka a kan Ridayya, ya zuba mata ido ganin sai murza harshe take.
"Shalele" Ya kira ta, cikin sauri ta buɗe idanunta ta kalli wanda ke tsaye a gabanta, bata hawaye da shi ba, amma tabbas muryarsa ta zauna a tunaninta raɗau. Ta shige ƙifta idanunta a karo na farko cikin murya ta sangarta ta fashe da kuka har lokacin kallonsa take. Ustaz ya durƙosa a gabanta ya kasa magana a tsayin shekaru shida ɗin da suka samu basa tare abubuwa da yawa sun faro har girman Ridayya, da kuma yanayin daya rusketa a yanzu. Tattausan hannunsa ya saka ya cira ta saba, tare da ɗora ta a kafaɗa ɗaya hannun kuma ya ja trolley ɗinsa kai tsaye kuma part ɗin Baba ƙarami ya nufa, shiru komai an yi mutuwa ba kowa, ko sallamar da ya yi cikin kamilalliyar muryarsa babu wanda ya yi balle ya amsa bedroom ɗinsa ya nufa da ita, yana jin yadda take sauke ajjiyar zuciya a bayyane.
Ammi dake zaune tana jinjina girman asarar da Ridayya ta saka ta, ta yi ƙwafa ta ce "Wallahi na tsani yarinyar nan, da dukkan alamu uwarta ma malamai take bi gashi nan komai na neman jirkice mini" Biba ta yi murmushi ta ce "Me ya sa kike tunanin Fatima za ta yi miki asiri?" Ammi ta ce "Me ya sa ba zan yi tunanin hakan ba, tunda tana son mijinta dole ce ta saka suka rabu, gashi da baya ƙaunar ko jin sunanta babu wanda yake magana a kan al'amarin auren yarinyar da kuma neman hakƙin Fatiman, kwatsam yanzu Mansur ya tsiro mini da wata ɗabi'a"
"A moral person doesn't lie, cheat, or steal, Fatima ba zata taɓa miki asiri ba wallahi zuciyarta ai ba irin taki bace, matsayin ƴar'uwa take kallon ki ba kishiya ba, babu laifi don ta so mijinta tunda ai sun gina tsaftatacciyar soyayya tun kafin aure, shiga kika yi wajan ganin kin raba su, ki ka yi musu farraƙu kuma kika raba uba da ƴarsa"
Ammi ta sauke ajjiyar zuciya ta ce "Yanzu Biba mene abin yi?" Biba ta yi murmushi ta ce "Nasan bayan na yi tafiya kin je wajan Malam right? Wanne aiki ya yi miki?"
"Kin san wannan yayar Fatimar Kaltum take kowa? Ƴar ta'adda ce wallahi da ƙyar idan bata taɓa yin dabanci ba, gashi mijinta soja ne muƙamin General gare shi, ni da abinda ya shafi hukuma bana son shi, to kuma tana iƙirarin zan gane kure ne"
"Kawai ki faɗa mini wanne aiki malam ya miki, ki riƙe bayaninki" Ammi ta ce "Ok. Na saka ya garƙame mini bakin jama'a da dama, ya kuma ɗauke hankalin kowa daga tunanin samawa Ridayya ƴanci, an rufe bakin Kaltum da mijinta, haka na mahaifiyar Fatima, an rufe bakin Baba ƙarami da matarsa ke dukkan wanda ya shafi Ridayya kuma yake da ikon yin magana a kan lamarin na kai sunansa wajan Malam, na saka an ɗauke hankalin Hajiya da Mai ran ƙarfe daga zuwa Kano, tun ranar basu ƙara zuwa ba, balle kiran waya, ke hatta yarana na rufe bakunan su kuɗi kawai nake kwasa wajan Alhaji Mansur" Murmushi sosai Biba ta yi ta ce
"Wow! That's good dear, amma kin manta malam ya ce Ridayya mai ƙashin arziƙi ce? Ko alherin da Alhji Mansur ke samun albarkacin haihuwarta ne, kuma ya haska mana goben mun gani, ga baiwa da tarin hikima"
Ammi ta miƙe tsaye ta ce "Shi ne abinda ba zai taɓa faruwa ba, idan har ina raye Ridayya ba zata taɓa zama wata a duniyar nan ba, shi ya saka nake bada maganin mayen nan ƙwaƙwalwar ta ƙara sa juyewa, ta yadda ba za ta taɓa fuskantar karatu ba, yadda ban hango future mai kyau a tawa zuri'ar ba, babu abinda zai saka na zuba idanu ƴar kishiya ta zaba wata, zan tabbatar bata samu ilimi ba idan har ina raye"
"Idan haka ne, kar ki sake ki bari Fatima ta dawo cikin gidan nan har abada" Biba ta faÉ—a tana cewa "kawo kunnenki"
Duk suna zaune a babban parlour mai zaman kansa, banda ƙira'ar Sheikh Afif Taj babu abinda ke tashi, ƙamshin Air-freshnerh ke tashi tako'ina.
A hankali ta É—aga kai tana kallon wacce ta fito daga cikin É—akin, cikin nutsuwa ta ajjiye azkar É—in hannunta tana sakin murmushi ta ce
"Autana ta fi ta kowa ya aka yi?" Mami ta ɗan juya idanunta sai kuma ta miƙa wa Dada wayarta idanun Dada ya sauka akan number da aka saka "Zaujina"
"To ki ɗaga mana" Mami ta zauna kusa da Dada ta ce "I won't pick it, six years bai kira ni ba sai yanzu?" Murmushi Dada ta yi ta ce "Ikon Allah, Autana shin sau nawa zan faɗa miki ki wa Alhji Mansur uzuri ne? Ita addu'a bata taɓa faɗuwa a ƙasa dole akwai ranar da za ta yi aikin ta, ki ɗauka yanzu ne ta yi nata aikin ɗauki wayar mijinki Fatima"
"Dada please"
"Just pick up dear" Mami ta ɗauki kiran tare da saka wayar a handsfree ta cikin wayar Baffa ya sauke wani wahalallen numfashi mai nauyi ya ce "Batuluna kin azabtar dani, kiran waya ba ɗagawa kamar na miki laifi?" Mami ta yi saurin kallon Dada, Dada kuma ta yi murmushi tana ci-gaba da duba azkar ɗin ƙasan zuciyarta tana hamdala ga Sarkin sarakuna Ubangijin talikai, Ubangijin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, ta wanzar da ƙudira da buwayarsa a lokacin da suke tsananin buƙatar taimakon shi.
"Kin yi shiru? Wallahi ɗan tafiyar da na yi a kan kwangilar da mukai magana last month ji nake kamar na yi shekara ɗari bakya kusa dani, i feel nothing but empty without you Zahraahna" Mami jin abin take kamar a mafarkin data saba yi na mijinta da tilon ƴarta, dukda babu wanda take nunawa abin yana damunta tasha wahala ƙwarai da gaske har kukan mutuwarta an fasa, amma dake mai dokin rai ce ta miƙe jijjigar da ta samu bata sake ta har yanzu. "Fatima, are okay?" Ta yi shiru can ya ce "Ok fine ki yi mini tuwon shinkafa miyar kuka ki tanadar mini man shanu, ki yi mini wannan kyakkawar shigar taki" Nan ma murmushi Mami ta yi idanunta na cikowa da hawaye a hankali ta ce
"Kamar baka cikin hayyacin ka naga alama, har ya sa ka manta cewa ni ba matarka bace ko?" A rikice ta ji muryarsa yana buga tsawa ya ce "What kamar ya? wanne irin mummunan furuci ne wannan wanda girman dafinsa na iya tarwasa zuciyata na roƙe ki da ki daina" Mami ta ce "Wallahi tallahi ni ba matarka bace, shekaru shida da suka shige ka sake ni ka rabani da jaririyata" Cikin sauri shima ya ce "Na rantse da girman Allah ke matata ce ban sake ki ba" Sai kawai ta kashe wayar tana kifa kanta a cinyar Dada tare da rushewa da wani irin kuka mai cin rai. _So the real love is never gone..?_
Dada ta dinga shafa kan Mami tana ganin yadda Baffa ke kira ba tsahirta wa wani na korar wani har number Dadan ya kira suke suka ƙi ɗagawa.
Ustaz ya dinga bin Ridayya da idanunsa masu laushi ganin yadda take ta murmushi a bawon wankan daya saka ta a ciki, ya ɗaure mata ƙugu da towel ƙarami ya jiƙe ta shakaf da ruwa, hakan ya yi ma Ridayya daɗi tana wasa irin wannan yadda ta nuna tamkar ba a yi mata wanka. She's so happy.
"Shalele, fita dai" Ta yi murmushi mayan dimples ɗinta suka loma duka lokaci ɗaya, ta fiddo masa da manyan idanunta masu zara-zaran gashin Idanu, baƙin fuskar nan kamar a saka ruwa da audiga a laso tamkar ya yi magana, yanayin farin idonta ke ƙara fidda baƙar fatarta ta a fili, a zahiri babu wani abu mai jan hankali a fuskar Ridayya duba da yadda bakinta ke tamkar a karkace ga yawu na fita ta gefe. "Abbiey"
Ta ce tana ƙifta masa ido, ya mata ƙuri a hankali kuma ya kai yatsa yana taɓa dimples ɗinta both sides.
"Ƴar gidan Abbiey" Ya furta a kasalance hana rufe ido, shekarun Ustaz 25 yayinda Ridayya take shekara 6 a duniya.
Tafiya karatunsa ya sauya sosai da gaske daman yana da girman jiki, wannan dalilin ya sa yake ganin idan aka faɗi shekarunsa jama'a za su raina shi, yanzu komai nasa ya sauya girma, nagarta, nutsuwa miskilanci da rashin son magana, baya damuwa da komai kamar yadda baya ɗaukan raini daga wajan wanda ba zai lamunta ba. Ya ajjiye ƙasumba mai kyau wacce ta yi daidai da tsayayyen gemun da Ridayya ke yawan jaa masa tana murmushi. Yana cireta daga cikin ruwan ta haɗe fuska ita ba haka ta su ba, ya shafe ta da Rob, ya ɗauki kaya masu nauyi yasa mata, da zai cire towel ɗin jikinta sai daya rufe ido yana faɗin "Haza haramun" bayan ya kammala shiryata cif ya kalleta ya kalli sumar kanta, bai ma iya tazar ba sai kawai ya ƙuƙƙulle ya saka mata hula. Ruwan zam-zam da rubutu ya ɗauka ya yi addu'a ya bata kana ya bata ruwan bagaruwa da zaiton yana jin tana da ajjiyar zuciya.
Bacci ne ya ɗauketa ya shirya shima cikin jallabiyya mai taushi ya naɗe kansa da hirami kana ya kunna karatun Alkur'ani mai girma ya rufo ɗakin. A parlour ya samu Umma da Baba ƙarami ta ce "Ikon Allah saukar yanzu hala?"
Ya jinjina mata kai yana zama saman kujera kana ya lumshe idanunsa hannunsa ɗaya yana murza goshinsa da gumi ke yanko masa da ƙyar ya iya cewa "Umma, Abba sabahur khair"
Furucin ya yi fitar gurbi daga cikin bakinta, ba tare data san waye a wajan ba, azaba ta saka babu sunan wanda ya zo bakinta da tunaninta sai na Abbiey.
Ustaz ya juyo da sauri har hiramin kansa na faÉ—uwa, idanunsa da suke kodayaushe a rufe ya sauka a kan Ridayya, ya zuba mata ido ganin sai murza harshe take.
"Shalele" Ya kira ta, cikin sauri ta buɗe idanunta ta kalli wanda ke tsaye a gabanta, bata hawaye da shi ba, amma tabbas muryarsa ta zauna a tunaninta raɗau. Ta shige ƙifta idanunta a karo na farko cikin murya ta sangarta ta fashe da kuka har lokacin kallonsa take. Ustaz ya durƙosa a gabanta ya kasa magana a tsayin shekaru shida ɗin da suka samu basa tare abubuwa da yawa sun faro har girman Ridayya, da kuma yanayin daya rusketa a yanzu. Tattausan hannunsa ya saka ya cira ta saba, tare da ɗora ta a kafaɗa ɗaya hannun kuma ya ja trolley ɗinsa kai tsaye kuma part ɗin Baba ƙarami ya nufa, shiru komai an yi mutuwa ba kowa, ko sallamar da ya yi cikin kamilalliyar muryarsa babu wanda ya yi balle ya amsa bedroom ɗinsa ya nufa da ita, yana jin yadda take sauke ajjiyar zuciya a bayyane.
Ammi dake zaune tana jinjina girman asarar da Ridayya ta saka ta, ta yi ƙwafa ta ce "Wallahi na tsani yarinyar nan, da dukkan alamu uwarta ma malamai take bi gashi nan komai na neman jirkice mini" Biba ta yi murmushi ta ce "Me ya sa kike tunanin Fatima za ta yi miki asiri?" Ammi ta ce "Me ya sa ba zan yi tunanin hakan ba, tunda tana son mijinta dole ce ta saka suka rabu, gashi da baya ƙaunar ko jin sunanta babu wanda yake magana a kan al'amarin auren yarinyar da kuma neman hakƙin Fatiman, kwatsam yanzu Mansur ya tsiro mini da wata ɗabi'a"
"A moral person doesn't lie, cheat, or steal, Fatima ba zata taɓa miki asiri ba wallahi zuciyarta ai ba irin taki bace, matsayin ƴar'uwa take kallon ki ba kishiya ba, babu laifi don ta so mijinta tunda ai sun gina tsaftatacciyar soyayya tun kafin aure, shiga kika yi wajan ganin kin raba su, ki ka yi musu farraƙu kuma kika raba uba da ƴarsa"
Ammi ta sauke ajjiyar zuciya ta ce "Yanzu Biba mene abin yi?" Biba ta yi murmushi ta ce "Nasan bayan na yi tafiya kin je wajan Malam right? Wanne aiki ya yi miki?"
"Kin san wannan yayar Fatimar Kaltum take kowa? Ƴar ta'adda ce wallahi da ƙyar idan bata taɓa yin dabanci ba, gashi mijinta soja ne muƙamin General gare shi, ni da abinda ya shafi hukuma bana son shi, to kuma tana iƙirarin zan gane kure ne"
"Kawai ki faɗa mini wanne aiki malam ya miki, ki riƙe bayaninki" Ammi ta ce "Ok. Na saka ya garƙame mini bakin jama'a da dama, ya kuma ɗauke hankalin kowa daga tunanin samawa Ridayya ƴanci, an rufe bakin Kaltum da mijinta, haka na mahaifiyar Fatima, an rufe bakin Baba ƙarami da matarsa ke dukkan wanda ya shafi Ridayya kuma yake da ikon yin magana a kan lamarin na kai sunansa wajan Malam, na saka an ɗauke hankalin Hajiya da Mai ran ƙarfe daga zuwa Kano, tun ranar basu ƙara zuwa ba, balle kiran waya, ke hatta yarana na rufe bakunan su kuɗi kawai nake kwasa wajan Alhaji Mansur" Murmushi sosai Biba ta yi ta ce
"Wow! That's good dear, amma kin manta malam ya ce Ridayya mai ƙashin arziƙi ce? Ko alherin da Alhji Mansur ke samun albarkacin haihuwarta ne, kuma ya haska mana goben mun gani, ga baiwa da tarin hikima"
Ammi ta miƙe tsaye ta ce "Shi ne abinda ba zai taɓa faruwa ba, idan har ina raye Ridayya ba zata taɓa zama wata a duniyar nan ba, shi ya saka nake bada maganin mayen nan ƙwaƙwalwar ta ƙara sa juyewa, ta yadda ba za ta taɓa fuskantar karatu ba, yadda ban hango future mai kyau a tawa zuri'ar ba, babu abinda zai saka na zuba idanu ƴar kishiya ta zaba wata, zan tabbatar bata samu ilimi ba idan har ina raye"
"Idan haka ne, kar ki sake ki bari Fatima ta dawo cikin gidan nan har abada" Biba ta faÉ—a tana cewa "kawo kunnenki"
Duk suna zaune a babban parlour mai zaman kansa, banda ƙira'ar Sheikh Afif Taj babu abinda ke tashi, ƙamshin Air-freshnerh ke tashi tako'ina.
A hankali ta É—aga kai tana kallon wacce ta fito daga cikin É—akin, cikin nutsuwa ta ajjiye azkar É—in hannunta tana sakin murmushi ta ce
"Autana ta fi ta kowa ya aka yi?" Mami ta ɗan juya idanunta sai kuma ta miƙa wa Dada wayarta idanun Dada ya sauka akan number da aka saka "Zaujina"
"To ki ɗaga mana" Mami ta zauna kusa da Dada ta ce "I won't pick it, six years bai kira ni ba sai yanzu?" Murmushi Dada ta yi ta ce "Ikon Allah, Autana shin sau nawa zan faɗa miki ki wa Alhji Mansur uzuri ne? Ita addu'a bata taɓa faɗuwa a ƙasa dole akwai ranar da za ta yi aikin ta, ki ɗauka yanzu ne ta yi nata aikin ɗauki wayar mijinki Fatima"
"Dada please"
"Just pick up dear" Mami ta ɗauki kiran tare da saka wayar a handsfree ta cikin wayar Baffa ya sauke wani wahalallen numfashi mai nauyi ya ce "Batuluna kin azabtar dani, kiran waya ba ɗagawa kamar na miki laifi?" Mami ta yi saurin kallon Dada, Dada kuma ta yi murmushi tana ci-gaba da duba azkar ɗin ƙasan zuciyarta tana hamdala ga Sarkin sarakuna Ubangijin talikai, Ubangijin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, ta wanzar da ƙudira da buwayarsa a lokacin da suke tsananin buƙatar taimakon shi.
"Kin yi shiru? Wallahi ɗan tafiyar da na yi a kan kwangilar da mukai magana last month ji nake kamar na yi shekara ɗari bakya kusa dani, i feel nothing but empty without you Zahraahna" Mami jin abin take kamar a mafarkin data saba yi na mijinta da tilon ƴarta, dukda babu wanda take nunawa abin yana damunta tasha wahala ƙwarai da gaske har kukan mutuwarta an fasa, amma dake mai dokin rai ce ta miƙe jijjigar da ta samu bata sake ta har yanzu. "Fatima, are okay?" Ta yi shiru can ya ce "Ok fine ki yi mini tuwon shinkafa miyar kuka ki tanadar mini man shanu, ki yi mini wannan kyakkawar shigar taki" Nan ma murmushi Mami ta yi idanunta na cikowa da hawaye a hankali ta ce
"Kamar baka cikin hayyacin ka naga alama, har ya sa ka manta cewa ni ba matarka bace ko?" A rikice ta ji muryarsa yana buga tsawa ya ce "What kamar ya? wanne irin mummunan furuci ne wannan wanda girman dafinsa na iya tarwasa zuciyata na roƙe ki da ki daina" Mami ta ce "Wallahi tallahi ni ba matarka bace, shekaru shida da suka shige ka sake ni ka rabani da jaririyata" Cikin sauri shima ya ce "Na rantse da girman Allah ke matata ce ban sake ki ba" Sai kawai ta kashe wayar tana kifa kanta a cinyar Dada tare da rushewa da wani irin kuka mai cin rai. _So the real love is never gone..?_
Dada ta dinga shafa kan Mami tana ganin yadda Baffa ke kira ba tsahirta wa wani na korar wani har number Dadan ya kira suke suka ƙi ɗagawa.
Ustaz ya dinga bin Ridayya da idanunsa masu laushi ganin yadda take ta murmushi a bawon wankan daya saka ta a ciki, ya ɗaure mata ƙugu da towel ƙarami ya jiƙe ta shakaf da ruwa, hakan ya yi ma Ridayya daɗi tana wasa irin wannan yadda ta nuna tamkar ba a yi mata wanka. She's so happy.
"Shalele, fita dai" Ta yi murmushi mayan dimples ɗinta suka loma duka lokaci ɗaya, ta fiddo masa da manyan idanunta masu zara-zaran gashin Idanu, baƙin fuskar nan kamar a saka ruwa da audiga a laso tamkar ya yi magana, yanayin farin idonta ke ƙara fidda baƙar fatarta ta a fili, a zahiri babu wani abu mai jan hankali a fuskar Ridayya duba da yadda bakinta ke tamkar a karkace ga yawu na fita ta gefe. "Abbiey"
Ta ce tana ƙifta masa ido, ya mata ƙuri a hankali kuma ya kai yatsa yana taɓa dimples ɗinta both sides.
"Ƴar gidan Abbiey" Ya furta a kasalance hana rufe ido, shekarun Ustaz 25 yayinda Ridayya take shekara 6 a duniya.
Tafiya karatunsa ya sauya sosai da gaske daman yana da girman jiki, wannan dalilin ya sa yake ganin idan aka faɗi shekarunsa jama'a za su raina shi, yanzu komai nasa ya sauya girma, nagarta, nutsuwa miskilanci da rashin son magana, baya damuwa da komai kamar yadda baya ɗaukan raini daga wajan wanda ba zai lamunta ba. Ya ajjiye ƙasumba mai kyau wacce ta yi daidai da tsayayyen gemun da Ridayya ke yawan jaa masa tana murmushi. Yana cireta daga cikin ruwan ta haɗe fuska ita ba haka ta su ba, ya shafe ta da Rob, ya ɗauki kaya masu nauyi yasa mata, da zai cire towel ɗin jikinta sai daya rufe ido yana faɗin "Haza haramun" bayan ya kammala shiryata cif ya kalleta ya kalli sumar kanta, bai ma iya tazar ba sai kawai ya ƙuƙƙulle ya saka mata hula. Ruwan zam-zam da rubutu ya ɗauka ya yi addu'a ya bata kana ya bata ruwan bagaruwa da zaiton yana jin tana da ajjiyar zuciya.
Bacci ne ya ɗauketa ya shirya shima cikin jallabiyya mai taushi ya naɗe kansa da hirami kana ya kunna karatun Alkur'ani mai girma ya rufo ɗakin. A parlour ya samu Umma da Baba ƙarami ta ce "Ikon Allah saukar yanzu hala?"
Ya jinjina mata kai yana zama saman kujera kana ya lumshe idanunsa hannunsa ɗaya yana murza goshinsa da gumi ke yanko masa da ƙyar ya iya cewa "Umma, Abba sabahur khair"