← Book details Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 118

Sashe 17

Munafukin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A zaune ta sameta ya ce "Ba dai kin cinye abincin ba?" Ta ce "Wanne abinci?" Ya ce "Wanda kika dafa" ta yi shiru ya sake magana shiru, ji ya yi kamar ya zabga mata mari amma ya daure
"Fushinki a zama ce mai raɗaɗi a gare ki wife, zan jure shurin kowa banda naki" Nan ma ta yi shiru. Cike da makirci ya fashe da kuka yana riƙe hannunta ya ce
"Saboda Allah ya jarabce ni da son ki, kike wulaƙanta ni Ridayya? Laifi ne don na so ki? Mene laifin zuciyata kar ki hukunta ni ta haka, nikam kar ki mini wannan azabar zan zutu da yawa" Kuka yake sosai ya ce
"I love You Ridha, wallahi ina son ki, ki yafe mini abinda na yi miki jiya"

"Me ka yi mini?"
Ya ce "ƙona ki da dutse, wallahi lemo aka bani na sha ashe akwai ƙwaya a ciki ita ta buge ni, har na ci zarafin matata ƴar aljanna, ba zan taɓa yafewa wanda ya sa na yi shaye-shaye ba" Ta yi murmushi mai ciwo ta ce "Ba komai" Ya rirriƙe hannunta ya ce "Hankalina ya tashi gudun kar ki yi kisan kai a kashe mini ke ya sa na dake ki, bawai saboda kin jiwa Khairy ciwo ba" Ya sauke murya ƙasa yana tausasa kalami ya ce "Wanne irin miji ne ni? Ridayya ban cancanta da rayuwarki ba ina zaluntarki, ki bari na sawwaƙe miki" Ya faɗa yana bugar cikinta.

"A'a, ka rufa mini asiri bani da kowa yanzu sai kai" Ta faɗa tana girgiza masa kai, ya ɓoye dariyarsa ya ce "Me ya sa kike zargin Khairy dani? Saboda ban taɓa faɗa miki Khairy nada aure ba? Laifina ne ƙanwata Khairy nada aure saɓani suka samu da mijinta shi ne ta nufi gida, a gida aka hanata zama ana ganin laifinta ne, ganin hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar ya saka na dawo da ita gidana kafin Allah ya daidaita labarin auren"

"Kuma ciki bai bayyana ba sai yanzu?" Da sauri ya ce "Kwanciya ya yi, ai kwantawa cikin ya yi amma gobe zan je na same shi zata koma ɗakinta shikenan?" Ta jinjina kai kawai ya ce "A'a ki ce kin yafe mini" Ta ce "Ya shige ba komai ka bata haƙuri" Ya yi sai kuma ya ce "To ɗakko mana abincin muci mai sona" Ta ware idanu ta ce "Bani da abinci,nima bata ishe ni ba" Wata uwar ashariya ya narka Ridayya a zuciyarsa ya fice. Yana fita Khairy ta shigo ta ce "Yanzu kin fahimta ko?"

"Ki yi haƙuri ban ɗauka haka ba, Allah ya daidaita tsakaninku" Khairy ta ce "Wannan turaren naki da maganin matan za ki sammin please" Ridayya ta nuna mata lafiyayyiyar humra ce da kwalacca, tun kafin ta buɗe suka cika ɗakin da ƙamshi ita kanta Khairy ta san humra ɗin ta musamman ce ba a ko'ina ake samun irinta ba, tafiyayyiya ce, sai ka wanke kaya sau nawa ƙamshinta bai fita ba. Ta duba maganin matan duka ta kwashe ta yi waje Ridayya sam bata damu ba hankalinta ya kwanta bata da matsala da Khairy bata damu da sanin me za ta yi da kayan matan bai tunda ba a gidan miji take ba.

Cikin dare Ridayya ta kasa bacci hannunta ya kumbura, fuskarta sai jini take. Kamar an cillo Zameer haka ya faÉ—o ta kalle shi ya ce
"Ina buƙatar ki"
"Bani da lafiya, marata ciwo take hannuna haka ga fuskata" Rai ɓace ya ce "Nina ɗora miki ciwon? Sanda na biya sadakinki kin faɗa mini ba ki da lafiya ne? Bayan ba uwar tsiyar da kika iya sai dai ki kwanta kamar ruwa? Allah ya ƙara mini haƙuri, ga babu gyara ɗan ƙamshin nan na zamani ɗan farin da mata suke"

"Dame zan yi kwalliyar? Duk abinda na mallaka wana bawa ina cewa kai ne? Ya kake so na yi wai me ya sa duk ka sauya?" Ya ce "Bai dame ni ba, hakƙina na zo amsa" Mamaki ya cika ta ganin yana rufe fuska da face mars, daman tunda suke irin sumbatar nan ta Zameer bai taɓa yi mata ba, tamkar yana ƙyanƙyamin bakinta "Idan har da yarda ta ce to I'm not in the mood"
Ƙafa ya saka ya maketa ta faɗi ƙasa kamar mahaukaciya babu tausayi yana ya haike mata babu kulawa ba soyayya, ya yi forcing nata ne tunda bada yardar ta ba, haka ya shaƙe mata wuya tana kakari gabaɗaya bai san me yake ba kamar zai kasheta...
Kuka ta dinga yi ta kasa motsi saboda wahala wuyanta duk shacin yatsunsa saboda shaƙa. Washegari bayan Zameer ya fice Khairy ta shirya ta fice wajan samarinta. Mai gyara Zainaba ta kira ya duba hannun Ridayya ashe karyata Zameer ya yi tana kuka sosai da muryarta mai sanyin nan kamar shagwaɓa, saboda bata da hargowa sam. Bayan an gama Ridayya ta kwaɓe fuska ta kasa kallon Zainaba, murmushi kawai Zainaba ta yi ta ce "Alkawari na zo ki cika mini, ki bani labarin rayuwarki kafin aure" Ridayya ta lumshe idanunta ba dan ta so ba ta soma bawa Zainaba labarinta kamar haka.....

*Ga duk mai buƙatar humra da kwalacca lafiyayyun sa mai gida magana ka hanzarta neman wannan number 08164069385 suna aikawa ko'ina, akwai ta masu ƙarfi akwai ta masu ƙaramin ƙarfi, ba za ku taɓa ladamar siya ba muna maraba da masu siyan ɗaiɗai ko sari🥰🥰🤙🏼🤙🏼*

*✿ MUNAFUKIN MIJI ✿*
Ridayya's story

Page 10
BRIGHT PENS🤙🏼 free batch

Please ku yi following nawa a facebook🫶🏼👇🏼
https://www.facebook.com/naeemerh.suleiman?mibextid=ZbWKwL

*PAID ADVERT*
https://chat.whatsapp.com/LvflCjMI3U5IfUHobHzudk
*HAUSA AFFILIATE MARKETING (HAM COURSE)* Yadda zaka samu kuɗi a ƙalla 50k- 100k a wata online da wayarka ta hannu (Smartphone) Matan aure, Ma'aikata, Ɗalibai, Ƴan mata e.t.c 07063194432

*Ta ina zan fara ne? Ta haɗuwar Ridayya da Zameer a jami'a ko kuma ta amintarta da ƙawarta Mardiyya? Ko dai na fara ta riƙon da Ustaz Bilal ya yi mata, girman ƙaddarar nada faɗi, al'ajabinta na da girma, dafin ƙaddarar kan iya harbar kowa, babu kuma wanda akai wa shamafiki da zubar hawaye. lissafin ƙaddarar zai fi tafiya daidai, idan muka fara da tubalin ginin, ya sanya zan fara da sanda Ridayya Bilal Mansur Rano ta zo duniya!*

Gabaɗaya suna tsaye sun yi carku-carku yanayin sauyin fuskokin kowa zai labartawa mai kallon su akwai lauje cikin naɗi, abu biyu ya sanya zuƙatansu cikin halin da suke, dukda bai cancanci ace akwai damuwar da kan iya hana fara'ar fuskarsu bayyana ba, duba da tagomashin abin alherin daya samu zuri'ar Mai ran ƙarfe a safiyar yau ta juma'a. A kuma unguwar Darmanawa dake Jihar Kanon Nigeria.

Ciwo ɗaya idan ya samu mutum ɗaya a familyn, to kamar ya shafi kowanne daga cikin ahhalin ne kasancewar su, marasa yawa da girma, kowa a hargitse yake idan ka ɗauke Alhaji Mansur Rano, wanda ko zuwa cikin asibitin bai yi balle a san halin da yake ciki. Shekaru aru-aru bai taɓa nuna rashin kulawa akan jininsa ba sai yau, ranar da kowa ya girgiza ya kuma ji a jikinsa tare da shakkar Alhaji Mansur Rano, jinkimarsa da ainahin ɓoyayyiyar siffarsa ta bayyana, wacce ta nuna asalin halinsa wanda inuwarsa ta lulluɓe tare da yi wa jama'a katanga da ita. Reception ɗin asibitin a cike yake idan ka ɗauke wanda baya garin ma. Dr ya fito da sauri yana goge zufar data yanko masa, cikin sauri kuma Hajiya ta miƙe tare da tarar shi tun kafin ya ƙarasu.
"Likita ya ake ciki? Yarinyar nan har yanzu, ba amo ba labari wacce kalar naƙuda ce wannan?" Dr ya yi jim sai kuma ya ce "Sai haƙuri Hajiya..,"
Jikin Hajiya ne ya fara rawa nan da nan ta nemi rikicewa zuciyarta na bugawa ta ce "Ka...ka.. kamarya sai haƙuri? Kada ka kuskura ka ce mini Fatima ta rasu, kar ka ce mini na rasa surukata da abinda ke cikinta?" Ƙoƙarin yi mata bayani yake amma bashi da zarafi da ƙarfin qiwwar yin haka, shi kansa bashi da tabbaci wacce ake magana tana raye ko ta mutu ne. Amma ce ta share hawayen dake gudana a idanunta ta miƙe da ƙyar ta nufi inda Hajiya ta cakume Likitan tana surutai.

"Hajiya ki sake shi please, ki bari mu ji me ya zo da shi, allow him to talk" ta rarrashi Hajiya kana ta dubi likita ta ce "Dr meke faruwa? Ya jikin Fatima?" A karo na wajan uku ya ƙara girgiza kai ya ce "Tsakani da Allah tun yaushe ne ta fara naƙuda?" Amma ta yi jim ta ce "Bana ce ba gaskiya, Fatima ai zurfin ciki gare ta, kodayaushe cewa take lafiya lou take meke faruwa?"

"Follow me Maaa"
Amma ta ce "A'a batun na biyo ka bane, bani da kuzarin hakan ma kawai ka faÉ—a mini halin da Æ´ar'uwata ke ciki" Dr ya yi jim sai kuma ya ce
"Har yanzu bata sauka ba tun jiya da kuka kawota, maganar da ake mun fidda rai da ita, wasiyya take bayar wa kuma tana buƙatar ganin mijinta, don Allah ku kira shi tana cikin wani hali" Amma ta yi baya tana shirin zubewa Zuhura ta yi saurin tare ta ta ce
"Subuhanallahi, take it easy Amma In sha Allah babu abinda zai faru sai abinda Ubangiji ya ƙadarta" Da dugu Amma ta nufi Emergency room hankalinta baya jikinta, kai tsaye ta hankaɗe likitocin da suke wajan tare da faɗawa cikin ɗakin. Abinda idanunta suka gani ya yi matuƙar gigita ta, ta nufi gadon tana cewa

"Ba mu yi haka dake ba Fatima, kar mu fara ba ki taɓa ce mana mutuwa za ki ba, mata nawa suke aure su ɗauki ciki, su yi rainonsa kuma su haife lafiya su shayar da abinda suka haifa? Ba za ki mutu ba, da gaske ba za ki mutu ba Fatima" Amma kuka take sosai domin bata taɓa ganin naƙuda irin ta Mami ba, jijjiga take idanunta ya zazzaro waje harshenta ya zazzago sai fisga take kamar mai aljanu, likitoci ne suka fitar da Amma ta nufi reception hankali tashe, Junaid ya tari Ammi da cewa.
"Ammi ya kike kuka haka? Kar ki ce mana wani abu ya samu Mami don Allah" Ammi ta dake ta share ta ce "Junaidu kira mini Baffanku kada Æ´ar mutane ta rasu na shiga uku"
Chapter 17 · 0% Book details