Sashe 94
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shawara ya kamata a canja a sakawa Asad layar nan ya haukace kowa ya huta dan lokaci yana tafiya komai sake canjawa yake, matar Asad indai ta haihu komai ya riga da ya lalace dole mu san abinda za'ayi kafin hakan ta faru dan mu ne a ruwa." Waziri ya girgiza kai cikin gamsuwa yace, "Hakan za'ayi, abinda kika ce gaskiya ne a cikin kwanakin nan Asad zai sauka daga mulkin nan, k'arshen wahalar mu tazo lokacin nasara zai fara ina jin hakan a jikina wallahi."
Ta girgiza kai tace, "Ina jin hakan a jikina nima." Kai ya girgiza shima kafin su rabu kowa ya kama gaban sa zuciyar kowa cike da kwarin guiwar samun nasaraa karo na babu adadi.
[17/12, 10:42 pm] Nafisat Alwasa: *Arewabooks@nanahaleema11*
*075*
A kwance yake a mik'e yana jan numfashi dak'yar hannun sa dafe da kansa yana juya kai da alama ciwon da kan yake yi masa ba d'an kad'an bane. Numfashin sa dak'yar yake sauka sabida ciwo ya rame lokaci d'aya yayi bak'i kansa ya taru da gashi haka fuskar sa kamar bashi ba.
A zaune Mama take a gefen sa rik'e da hannun sa jikin ta yayi sanyi sosai ta kalli Hydar da yake tsaye shima tace, "Yaushe ne tafiyar taku ne? Kullum jikin sa sake gaba yake yi ya koma kamar bashi ba." Hydar yace, "an jima jirgin mu zai tashi zuwa India, amma ni Mama jikin Asad sai nake ganin kamar bana asibiti bane ba." Mama hawaye take ta dafe kanta tace, "Ban san me zance ba Hydar, mahaifin ku yace ciwon sa bana asibiti bane amma yak'i mayar da hankali a nema masa magani, dan Allah laifina sai ya shafi Asad? Duk soyayyar da yake yiwa Asad ace yana kwance a haka Abban ku baiyi komai ba kamar ma bai damu ba. Na shiga uku ni Rabi'a komai sake lalace min yake yi" ta fad'a tana sake dafe kanta da hannayen ta duka biyu.
Hydar yace, "Za'a tafi India tunda kina so aje can sai muje in sha Allah zai samu lafiya." Hydar ya kalli Asad da yake kwance sai yaga kamar magana yake yi ya sunkuya da kunnen sa yana sauraron abinda Asad d'in yake cewa yaji yana fad'in, "Aliyu, Mama Aliyu."
Hudar ya dago yace, "Mama Aliyu yake kira fa." Mama tace, "Wai ina yake tafiya ne? D'an uwan sa yana kwance babu lafiya amma shi yana can yawon duniya da y'an matan sa." Hydar yace, "Kiyi hak'uri Mama. Ina Jidda matar sa?." Mama ta dafe kanta bata bashi amsa ba dan bata san me zata ce ba.
Kamar wacce ta tuna wani abu sai ta mik'e tace, "Kafin ku tafi India akwai wajan wani malami da nake so naje na karb'o masa magani, maganin sa yayi tasiri sosai a kwanakin baya ka jira ni" ta fad'a tana fita ta sauka ta nufi b'angaren ta. Bata jira Suhaima ba ta nemi driver ya d'auke ta bai wuce ko ina da ita ba kai tsaye gidan su Rauda ta nufa.
Dawowar Rauda kenan daga Bauchi tana zaune kamar ko yaushe jikinta a sanyaye ta rame sosai sai hasken ciki da tayi dan a lokacin cikin ta yayi wata d'aya harda kwanaki. Kasancewar bata laulayi baza ka fahimci ma ciki ne da ita ba sai ka sani. Umma na zaune kusa da ita gidan babu kowa duk an watse daga su sai su kamar ba shine akayi taro ba.
Sallama sukaji anyi an shigo falon Umma ta kalli wacce ta shigo tare da amsawa, Rauda bata juya ba tana zaune hannun ta rik'e da ruwa wanda tasha ta rage ta rik'e a hannu bata kalli wacce ta shigo ba. Mama da take tsaye Umma ta kalle ta tace, "Bismillah ki zauna mana." Jikin Mama a sanyaye ta zauna ta kalli Umma tace, "barka da gida." Umma tace, "Yauwa sannu da zuwa" Umma ta fad'a da mamaki ganin yadda tayi magana kamar ba ita ba harda murmushi.
Kallon Rauda tayi har lokacin bata san wanda ta shigo ba ta kalli Umma sai taji mugun nauyi ya danne mata k'irji ta sunkuyar da kanta k'asa a karo na farko da tayi hakan ga wank kafin ta d'ago ta sake kallon Umma tace, "Bata da lafiya ne?" Ta fad'a tana nuna mata Rauda. Umma tayi mata wani irin kallo kafin ta tab'e baki tace, "Eh bata jin dad'i." Mama tace, "Allah ya k'ara lafiya."
"Amin" Umma ta amsa a tak'aice tayi shiru bata sake magana ba dan so take taji da me tazo kuma. Mama ta had'd'iye yawu dak'yar tace, "Alfar......" Sai ta kasa furta alfarma tayi shiru dan kalmar bata zauna a bakinta ba dan ba fadar ta take yi ba ta sake bud'e baki dak'yar, "Nazo neman alfarmar sake ganin Malam a karo na uku." Umma ta numfasa tace, "To ai ba'a gidan nan yake ba ko kin manta ne?." Mama ta girgiza kai tace, "Ban manta ba, iso nake so ayi min kamar wancan lokacin, ina son ganin sa da gaggawa ne."
Umma tace, "Ai tunda kun gana wancan lokacin in kikayi masa bayani zai gane ki zai baki lokacin da zaki same shi." Mama a tausahe tace, "emergency nake son ganin sa, wanda zaiyi amfani da maganin India zai wuce anjima kad'an." Umma ta girgiza kai ta sauke numfashi tace, "To ga gidan namu shiru babu kowa balle a raka ki, sai dai in a neme shi a waya in ya bada dama sai kije ki ganshi." Mama ta girgiza kai tace, "Na gode."
Umma ta d'auki wayar ta a gabanta ta kira Baba malam a waya ta katse bai d'auka ba ta sake kira a nan ya d'auka bayan sun gaisa ta sanar dashi dalilin kiran ya bata amsa sukayi sallama ta kashe ta kalli Mama tace, "Yace ganin sa yau bazai yu ba gaskiya, sai dai ki bari zuwa gobe in Allah ya nuna mana." Mama kamar zata zubar da hawaye ta kalli Umma muryar ta har rawa take yi tace, "Ina so na ganshi a yau d'in matsalar da take tare dani a yanzu har tafi ta baya." Umma tace, "To ga abinda yace ban san me zan miki bayan wannan ba."
Mama tace, "a nema min alfarma a wajan sa dan Allah. Maganin sa yayi min tasiri matuk'a a kwanakin baya yanzu matsalar da Asad yake ciki har tafi wancan, dan Allah ki sake masa magana" Mama ta fad'a kamar da alama ta manta da talaka kamar Umma take magana jin yadda take karyar da murya baza ka d'auka ita bace ba, kana jin maganar ta kasan tabbas akwai damuwa sosai a tare da ita.
Ambatar Asad da Mama tayi sai gaban Umma ya yanke ya fad'i amma sai ta jure bata nuna ba tace, "To ya kike so nayi miki? Nayi iya abinda zan iya tunda yace haka babu damar ganin naki ne a yau." Mama ta sauke numfashi jikin ta duk yayi sanyi ta kasa furta komai domin bata san me zata ce ba, duka burin ta akan maganin sane gashi bazata samu ba.
K'arar wayar Umma ya saka Umma ta kalli wayar ganin mai kiran sai ta d'auka ta saka a kunne tayi magana kafin ta kashe ta kalli Mama tace, "Yace kije nan da mintina ashirin, kika wuce haka baza ki same shi ba." Nan take fuskar Mama ta washe farin ciki ya bayyana tace, "Yanzu kuwa zanje. Na gode sosai" ta mik'e tsaye ta kalli Rauda nan take sai gaban ta ya fad'i sosai amma bata nuna hakan ba tace, "Allah ya baki lafiya."
Har lokacin bata kalle ta ba Mama ta fita zuciyar ta cikin farin ciki amma wani b'angaren na zuciyar ta mamakin kanta take yau itace ya nemi alfarma wajan k'ananun mutane kamar su Umma har tana had'a su da Allah. Tana fita Umma ta kalli Rauda tace, "Ke Rauda sai naji tace Asad ne babu lafiya, kenan wanda yake tare dake waye?." Nan take gaban Rauda ya buga ta d'ago ta kalli Umma itama ita take kallo ido cikin ido ta had'd'iye yawu tana kallon Umma.
Umma tace, "Naji tace shine babu lafiya da alama jikin yayi zafi kuma ciwon duk yadda akayi bana asibiti bane ba duba da yadda ta tashi hankalin ta har take had'ani da Allah, kenan bayan ya daina zuwa wajan ki ya fara rashin lafiya ko kuma daman ba shi bane yake tare dake? Nifa jikina ya bani k'anin sane a tare dake bashi ba Rauda" Umma ta fad'a cikin tashin hankali tana kallon Rauda.
Dumm gaban Rauda ya buga ta zaro idanu waje ta kasa magana ta rasa me zata ce tana kallon Umma itama cikin tsananin tsoro, Umma tace, "Bara baban ki yazo yana dakyau a bincika dakyau zuwan babar sa gidan nan ya saka ni a rud'ani, tunanina yana bani bashi ne a tare dake ba Aliyu ne." Rauda tayi shiru tana sauke numfashi hankalin ta har yafi na Umma tashi bata da kuzarin da zata nuna ne.
Umma ta kuma cewa, "in kuma Asad din ne kenan bashi da lafiya? Babar sa bata san har yanzu da auren sa a tare dake ba kenan kome?. Tabd'ijam gaskiya akwai sauran rina a kaba." Ita dai Rauda shiru tayi amma yadda gaban ta yake fad'uwa Allah kad'ai yasan abinda take ji a zuciyar ta.
Tashi tayi ta shiga d'aki kafin ta zauna wayar ta ta fara ihu ta kalli wayar taga Anty Ramla a kai sai ta samu kanta da yin murmushi har cikin zuciyarta ta samu waje ta zauna ta d'auki wayar ta saka a kunne, daga can b'angaren tace, "Amarsu ta ango, amarya kin sha khamshi." Y'ar dariya Rauda tayi kad'an kafin tace, "Ina kwana Anty."
"Kin tashi lafiya Amarya? Ya kwanan amarci?." Rauda bata amsa ba sai tace, "Ina Dr fatan yana lafiya?."
"Lafiya lau Rauda. Munyi miki laifi bamu shigo Nigeria bikin ki ba ko?. Wallahi Dr ne aiki ya masa yawa a asibiti ni kuma exams muke shiyasa baki ganmu ba amma dan Allah kiyi hak'uri, ki bawa Umma hak'uri zamu zo takanas dan ke."
Ta girgiza kai tace, "Ina jin hakan a jikina nima." Kai ya girgiza shima kafin su rabu kowa ya kama gaban sa zuciyar kowa cike da kwarin guiwar samun nasaraa karo na babu adadi.
[17/12, 10:42 pm] Nafisat Alwasa: *Arewabooks@nanahaleema11*
*075*
A kwance yake a mik'e yana jan numfashi dak'yar hannun sa dafe da kansa yana juya kai da alama ciwon da kan yake yi masa ba d'an kad'an bane. Numfashin sa dak'yar yake sauka sabida ciwo ya rame lokaci d'aya yayi bak'i kansa ya taru da gashi haka fuskar sa kamar bashi ba.
A zaune Mama take a gefen sa rik'e da hannun sa jikin ta yayi sanyi sosai ta kalli Hydar da yake tsaye shima tace, "Yaushe ne tafiyar taku ne? Kullum jikin sa sake gaba yake yi ya koma kamar bashi ba." Hydar yace, "an jima jirgin mu zai tashi zuwa India, amma ni Mama jikin Asad sai nake ganin kamar bana asibiti bane ba." Mama hawaye take ta dafe kanta tace, "Ban san me zance ba Hydar, mahaifin ku yace ciwon sa bana asibiti bane amma yak'i mayar da hankali a nema masa magani, dan Allah laifina sai ya shafi Asad? Duk soyayyar da yake yiwa Asad ace yana kwance a haka Abban ku baiyi komai ba kamar ma bai damu ba. Na shiga uku ni Rabi'a komai sake lalace min yake yi" ta fad'a tana sake dafe kanta da hannayen ta duka biyu.
Hydar yace, "Za'a tafi India tunda kina so aje can sai muje in sha Allah zai samu lafiya." Hydar ya kalli Asad da yake kwance sai yaga kamar magana yake yi ya sunkuya da kunnen sa yana sauraron abinda Asad d'in yake cewa yaji yana fad'in, "Aliyu, Mama Aliyu."
Hudar ya dago yace, "Mama Aliyu yake kira fa." Mama tace, "Wai ina yake tafiya ne? D'an uwan sa yana kwance babu lafiya amma shi yana can yawon duniya da y'an matan sa." Hydar yace, "Kiyi hak'uri Mama. Ina Jidda matar sa?." Mama ta dafe kanta bata bashi amsa ba dan bata san me zata ce ba.
Kamar wacce ta tuna wani abu sai ta mik'e tace, "Kafin ku tafi India akwai wajan wani malami da nake so naje na karb'o masa magani, maganin sa yayi tasiri sosai a kwanakin baya ka jira ni" ta fad'a tana fita ta sauka ta nufi b'angaren ta. Bata jira Suhaima ba ta nemi driver ya d'auke ta bai wuce ko ina da ita ba kai tsaye gidan su Rauda ta nufa.
Dawowar Rauda kenan daga Bauchi tana zaune kamar ko yaushe jikinta a sanyaye ta rame sosai sai hasken ciki da tayi dan a lokacin cikin ta yayi wata d'aya harda kwanaki. Kasancewar bata laulayi baza ka fahimci ma ciki ne da ita ba sai ka sani. Umma na zaune kusa da ita gidan babu kowa duk an watse daga su sai su kamar ba shine akayi taro ba.
Sallama sukaji anyi an shigo falon Umma ta kalli wacce ta shigo tare da amsawa, Rauda bata juya ba tana zaune hannun ta rik'e da ruwa wanda tasha ta rage ta rik'e a hannu bata kalli wacce ta shigo ba. Mama da take tsaye Umma ta kalle ta tace, "Bismillah ki zauna mana." Jikin Mama a sanyaye ta zauna ta kalli Umma tace, "barka da gida." Umma tace, "Yauwa sannu da zuwa" Umma ta fad'a da mamaki ganin yadda tayi magana kamar ba ita ba harda murmushi.
Kallon Rauda tayi har lokacin bata san wanda ta shigo ba ta kalli Umma sai taji mugun nauyi ya danne mata k'irji ta sunkuyar da kanta k'asa a karo na farko da tayi hakan ga wank kafin ta d'ago ta sake kallon Umma tace, "Bata da lafiya ne?" Ta fad'a tana nuna mata Rauda. Umma tayi mata wani irin kallo kafin ta tab'e baki tace, "Eh bata jin dad'i." Mama tace, "Allah ya k'ara lafiya."
"Amin" Umma ta amsa a tak'aice tayi shiru bata sake magana ba dan so take taji da me tazo kuma. Mama ta had'd'iye yawu dak'yar tace, "Alfar......" Sai ta kasa furta alfarma tayi shiru dan kalmar bata zauna a bakinta ba dan ba fadar ta take yi ba ta sake bud'e baki dak'yar, "Nazo neman alfarmar sake ganin Malam a karo na uku." Umma ta numfasa tace, "To ai ba'a gidan nan yake ba ko kin manta ne?." Mama ta girgiza kai tace, "Ban manta ba, iso nake so ayi min kamar wancan lokacin, ina son ganin sa da gaggawa ne."
Umma tace, "Ai tunda kun gana wancan lokacin in kikayi masa bayani zai gane ki zai baki lokacin da zaki same shi." Mama a tausahe tace, "emergency nake son ganin sa, wanda zaiyi amfani da maganin India zai wuce anjima kad'an." Umma ta girgiza kai ta sauke numfashi tace, "To ga gidan namu shiru babu kowa balle a raka ki, sai dai in a neme shi a waya in ya bada dama sai kije ki ganshi." Mama ta girgiza kai tace, "Na gode."
Umma ta d'auki wayar ta a gabanta ta kira Baba malam a waya ta katse bai d'auka ba ta sake kira a nan ya d'auka bayan sun gaisa ta sanar dashi dalilin kiran ya bata amsa sukayi sallama ta kashe ta kalli Mama tace, "Yace ganin sa yau bazai yu ba gaskiya, sai dai ki bari zuwa gobe in Allah ya nuna mana." Mama kamar zata zubar da hawaye ta kalli Umma muryar ta har rawa take yi tace, "Ina so na ganshi a yau d'in matsalar da take tare dani a yanzu har tafi ta baya." Umma tace, "To ga abinda yace ban san me zan miki bayan wannan ba."
Mama tace, "a nema min alfarma a wajan sa dan Allah. Maganin sa yayi min tasiri matuk'a a kwanakin baya yanzu matsalar da Asad yake ciki har tafi wancan, dan Allah ki sake masa magana" Mama ta fad'a kamar da alama ta manta da talaka kamar Umma take magana jin yadda take karyar da murya baza ka d'auka ita bace ba, kana jin maganar ta kasan tabbas akwai damuwa sosai a tare da ita.
Ambatar Asad da Mama tayi sai gaban Umma ya yanke ya fad'i amma sai ta jure bata nuna ba tace, "To ya kike so nayi miki? Nayi iya abinda zan iya tunda yace haka babu damar ganin naki ne a yau." Mama ta sauke numfashi jikin ta duk yayi sanyi ta kasa furta komai domin bata san me zata ce ba, duka burin ta akan maganin sane gashi bazata samu ba.
K'arar wayar Umma ya saka Umma ta kalli wayar ganin mai kiran sai ta d'auka ta saka a kunne tayi magana kafin ta kashe ta kalli Mama tace, "Yace kije nan da mintina ashirin, kika wuce haka baza ki same shi ba." Nan take fuskar Mama ta washe farin ciki ya bayyana tace, "Yanzu kuwa zanje. Na gode sosai" ta mik'e tsaye ta kalli Rauda nan take sai gaban ta ya fad'i sosai amma bata nuna hakan ba tace, "Allah ya baki lafiya."
Har lokacin bata kalle ta ba Mama ta fita zuciyar ta cikin farin ciki amma wani b'angaren na zuciyar ta mamakin kanta take yau itace ya nemi alfarma wajan k'ananun mutane kamar su Umma har tana had'a su da Allah. Tana fita Umma ta kalli Rauda tace, "Ke Rauda sai naji tace Asad ne babu lafiya, kenan wanda yake tare dake waye?." Nan take gaban Rauda ya buga ta d'ago ta kalli Umma itama ita take kallo ido cikin ido ta had'd'iye yawu tana kallon Umma.
Umma tace, "Naji tace shine babu lafiya da alama jikin yayi zafi kuma ciwon duk yadda akayi bana asibiti bane ba duba da yadda ta tashi hankalin ta har take had'ani da Allah, kenan bayan ya daina zuwa wajan ki ya fara rashin lafiya ko kuma daman ba shi bane yake tare dake? Nifa jikina ya bani k'anin sane a tare dake bashi ba Rauda" Umma ta fad'a cikin tashin hankali tana kallon Rauda.
Dumm gaban Rauda ya buga ta zaro idanu waje ta kasa magana ta rasa me zata ce tana kallon Umma itama cikin tsananin tsoro, Umma tace, "Bara baban ki yazo yana dakyau a bincika dakyau zuwan babar sa gidan nan ya saka ni a rud'ani, tunanina yana bani bashi ne a tare dake ba Aliyu ne." Rauda tayi shiru tana sauke numfashi hankalin ta har yafi na Umma tashi bata da kuzarin da zata nuna ne.
Umma ta kuma cewa, "in kuma Asad din ne kenan bashi da lafiya? Babar sa bata san har yanzu da auren sa a tare dake ba kenan kome?. Tabd'ijam gaskiya akwai sauran rina a kaba." Ita dai Rauda shiru tayi amma yadda gaban ta yake fad'uwa Allah kad'ai yasan abinda take ji a zuciyar ta.
Tashi tayi ta shiga d'aki kafin ta zauna wayar ta ta fara ihu ta kalli wayar taga Anty Ramla a kai sai ta samu kanta da yin murmushi har cikin zuciyarta ta samu waje ta zauna ta d'auki wayar ta saka a kunne, daga can b'angaren tace, "Amarsu ta ango, amarya kin sha khamshi." Y'ar dariya Rauda tayi kad'an kafin tace, "Ina kwana Anty."
"Kin tashi lafiya Amarya? Ya kwanan amarci?." Rauda bata amsa ba sai tace, "Ina Dr fatan yana lafiya?."
"Lafiya lau Rauda. Munyi miki laifi bamu shigo Nigeria bikin ki ba ko?. Wallahi Dr ne aiki ya masa yawa a asibiti ni kuma exams muke shiyasa baki ganmu ba amma dan Allah kiyi hak'uri, ki bawa Umma hak'uri zamu zo takanas dan ke."