Sashe 105
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Umma ta girgiza kai tace, "Har yanzu nutsuwa ta tak'i dawowa jikina, kaina jinsa nake a cushe bana fahimtar komai wallahi. D'an uwa na jini uwa d'aya uba d'aya amma akan mulki ya nemi salwantar da jinin sa? Meye abin so a mulkin?." Baba yace, "Baki san dad'in mulki bane shiyasa kike fad'ar haka, duk wani mai mulki da ya lashi zumar sa baya so ya daina lasar ta har abada, shiyasa hankalin su yake tashi in suka rasa kujerar su wasu kiga kamar ma zasuyi hauka. Mulki babu abinda baya sakawa ayi dan a d'auki rai a neman mulki abu ne mai sauk'i."
Umma tace, "Ni kuwa nasan abu ne mai sauk'i tunda gashi naji da kunne na. Babu wanda ya bami tausayi sai Asad d'in da mahaifin sa, duk irin abubuwan da mahaifiyar sa tayi mana amma wallahi sai nake jin zuciyata tana tausaya mata dan Allah kad'ai yasan halin da take ciki a yanzu. Y'ay'anta da take alfahari take tutiya ace d'aya ne kawai mai amfani a cikin su? Muguntar wannan tana wane ta wannan, kowa a cikin su burin sa ya kawar da d'an uwan sa?."
Baba yace, "Hydar d'in shine abin mamaki, ki tuna yadda yake shigewa Asad d'in gaba a akan komai hatta auren sa da Rauda shine ya assa shi ashe yana da manufar yin hakan badan Allah ya aikata ba. Yafi kowa bani mamaki ya kuma fi kowa bani tsoro, domin kaji tsoron maqiyin ka mai fuska biyu gwar wanda zai nuna maka kai tsaye baya sonka da wanda zai dinga yi maka kwantan b'auna."
Umma tace, "Shi mai martaban ya zaiji?. K'anin sa uwa d'aya uba d'aya, matar sa kuma uwar gidan sa, ga ita kanta babar Asad d'in, ga y'ay'an sa guda biyu. In ba namijin gaske mai dakakkiyar zuciya ba sai ya yanke jiki ya fad'i ya had'u da lalurar shanyewar b'arin jiki. Ace duk wanda ya aikata maka sharri jinin kane da matan ka?."
Baba yace, "Allah baya cutar da bawa akan laifin da bai aikata ba, duk wanda ya kasance mai yawan addu'a da neman zab'in Allah Allah bazai barshi da kansa ba sai ya shiga cikin lamarin sa. Yanzu ki duba shi Wazirin cikin lokaci kad'an Allah ya nuna masa sakayya babu b'ata lokaci y'ay'an sa biyu sun rasu a lokaci d'aya. Ni na d'auka ma yara ne fa ashe dukkan su babu wanda bai kai munzalin aure ba babu kamar namijin ma da ya girma sosai. Abin mamaki da d'aure kai turaren da aka bashi da nufin kashe Asad da baban sa suka d'auka sukayi amfani dashi su suka mutu. Dan Allah in baka ji tsoron Allah a lamarin nan ba tsoron me zaka ji?. In bakayi imani da Allah ba dawa zakayi imani?. Kai Allah kasa mufi k'arfin zuciyar mu."
Umma girgiza kai kawai take yi cikin rud'ani zuciyar ta ta karye tace, "Kaji tsoron wanda aka zalunta in Allah ya tashi saka masa, yanzu kalli cikin lokaci kad'an Allah ya nuna masa bai isa yayi abinda bai nufa ba. Ita kuma uwar gidan garin son a kashe wani kaso kashe ta in mai hankali ce iya wannan ya isheta ishara, kalli ita mahaifiyar tasu duk alfaharin da take dasu da nuna talaka ba komai bane sai gashi alfarmar talakan taci kuma y'ay'an nata guda ukun d'aya ne kawai mai amfani a ciki. Shi Aliyun da ake nufin kashe d'an uwan sa dashi har ana so a saka shi hauka sai gashi......." umma bata k'arasa ba sai tace, "Kai Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, ya hayyu ya qayyum ka saka mufi k'arfin zuciyar mu, ka tsare mu ka kare mu a duk inda muke kasa mu rinyaji zuciyar mu ba ita ta rinjaye mu ba" Umma ta fad'a tana d'aga hannun ta sama.
Baba ya amsa da amin sukayi shiru dukkan su kafin Baba yace, "Ni daman nasan babu ta yadda za'ayi Asad ya rsntse yace bashi ya saki Rauda ba akan k'arya, ashe duka aikin d'an uwan sane." Umma bata ce komai ba girgiza kai kawai take yi kafin ta sauke numfashi tace, "Duka haka Allah ya nufa ya kuma k'addara, shekara har ta kusa zagowa da bikin sai yanzu ake samun sassauci a lamarin auren nasu. Ni wallahi yanzu abin yafi na baya bani tsoro, kaga Hydar d'in nan gani nake kamar bazai bar Rauda ba dan babu alamun nadama fa a tare dashi."
Baba yace, "yadda Allah ya kare Asad da mahaifin sa haka Allah zai kare ta, zuciyar ta a wanke take bata tab'a nufar wani da sharri ba Allah bazai bari a cuce ta ba." Umma ta d'aga kai kawai Baba ya tashi ya fita zuwa masallaci dan yaji kiran sallar i'sha itama ta tashi ta tayar da sallah.
Sai bayan ta idar ta duba Rauda ta ganta a zaune da alama ma tayi sallah itama ta koma ta kawo mata abinci da kanta ta tilasta mata taci badan taso ba dan ita har yanzu zuciyar ta bata amince cikin Asad ne a jikin ta ba.
*☆☆☆*
Cikin awa da bai wuce uku ba an chanja komai na b'angaren mai Martaba Asad hatta carpet an cire shi an saka wani dan mahaifin sa yace bai amince da komai na ciki ba. Dukka kayan sawar Asad dana Aliyu an fito dasu daman mai martaba ya bayar da order dinki da alkyabba manya-manya ta Asad duk an kawo an saka ya koma sabo dal.
Yana tsaye a jikin window yana kallon jama'ar gidan da suke ta kai kawo ya sauke numfashi ya juyo yana kallon falon ba komai ne yake fad'o masa ba sai zaman Jidda a cikin sa ita da Yayan sa. Tsaki yaja ya d'auke kansa yana cize baki, "Hydar!" Ya furta a bayyane yana lumshe idanun sa da suka kankance sabida tashin hankali da b'acin rai.
Zuciyar sa bugawa take yi Allah ya sani yana qaunar Hydar da zuciya d'aya duk abin nan da fari baiji son sa ya fita daga zuciyar sa ba saima cutar dashi da son yake so yayi. Barin jikin window d'in yayi ya k'araso cikin falon yana niyar sauka yaga mahaifin sa na yawowa saman.
Dole ya koma da baya ya bashi hanya ya wuce ya zauna ya k'araso ya zauna a k'asan carpet yace, "Barka da zuwa." Mai martaba yace, "Ina kake niyar zuwa haka?." Asad yace, "Zanje wajan Mama ne hankalina yak'i kwanciya ina so na ganta."
"Ban amince da fitar sirrin nan da kake yi ba kayi fitar da ko wanne saraki yake yi." Asad yace, "In Allah ya amince zanyi abinda akace." Mai martaba yace, "Ya batun matar ka Jidda?."
Gaban sa ya fad'i matuk'a ya d'ago yace, "Allah ya k'ara maka lafiya ni ba matata bace ba." Mai martaba yace, "Matar kace Asad, shari'a ta baka d'an cikin ta duk da ba naka bane. Ka tambayi ya lafiyar ta take?."
Asad yace, "Ina neman afuwar ka dan ni gaskiya indai dan igiyar aurena da yake kanta ne na jima da datse ta, na sake ta!" Ya furta a sanyaye yana kallon mahaifin nasa da shima yake kallon sa da nasa mamakin.
"Ka sake ta fa kace Asad? Waye ya fad'a maka shugaba yana saki?. Kaifa sarki ne shugaba ne da zaka daqile yawaitar sakin aure da ake yi amma da kanka kake furta ka sake ta?."
Asad yace, "Allah ya wuci zuciyar mahaifina, bazan iya zama da ita ba mahaifina ya shaida ita d'in fasiqa ce taya zan iya zama da wacce tayi alfasha da auren ta tana sane?. Daman can zab'in Mama ce nayi biyayya ne na aure ta badan ina so ba sai dan gudun b'acin ran Mama, yanzu kuma ga abinda ya biyo baya zama na da ita ya haramta har abada. Batun da da mai martaba yake yi jinin Aliyu jinina ne zan iya rik'e masa y'ay'a d'ari indai akace jinin sane koda ba y'ay'an sunnah bane ba, amma bazan iya zama da ita ba."
Mai martaba da yake jin sa yasan gaskiya yake fad'a masa amma yana gudun zubewar k'imar gidan dan in akaji labarin Asad ya saki Jidda ga d'a kuma sunan gidan da tarihin gidan gabad'aya ya lalace. Duk sanda aka bud'e ido akaga baby Jidda sai Rauda kowa zai ta tunanin inda take k'arshe a fara mumman zato a kan hakan. Yace, "Asad nasan gaskiya kake fad'a, amma ina so ka duba yanayin gidan da kake da kuma matsayin da kake dashi, me mutanen gari dama jama'ar gidan nan da basu san abinda ya faru ba in akace ka saki matar ka bayan tana da cikin ka?." Asad ya kalli mahaifin sa jin ya ambaci ciki sa sai mai martaba yayi murmushi yace, "Nasan ba jinin ka bane amma cikin Aliyu naka ne, abinda yayi ka shine yayi Aliyu. Kowa yasan Jidda matar kace ya kenan in akace yau babu Jidda a gidan sai wata daban me hakan yake nufi?."
Asad yace, "Ban tari numfashin mai martaba ba, amma ina so a duba lamarin wallahi bazan iya zama da ita ba, kuma ni na riga na yanke hukunci gashi na sanar da mahaifina bana tunanin zan iya yin wani hukuncin da ba wannan ba, ina neman afuwar ka akan wannan bazan iya ba wallahi" ya fad'a yana kallon k'asa zuciyar sa na rawa in ya tuna abinda ya faru sai yaji jikin sa kamar ana kwashe masa kuzari sa gabad'aya komai sai ya tsaya masa cak.
[17/12, 10:45 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*083.*
Mai martaba kallon sa yake yi ganin yadda jikin sa yayi sanyi ya sauke numfashi yasan daman abu ne mai wahala amma ya za'ayi dole ayi wani abun dan b'oye wani abun. Yace, "Asad bank'i ta taka ba, amma yanzu ya kenan in mutanen gari suka ji ka rabu da matar ka?." Asad yace, "Allah ya taimaki Abba ni a yanzu ba matata bace, tasan na saketa na fad'a mata baki da baki tun lokacin da take kirana da Aliyu."
Umma tace, "Ni kuwa nasan abu ne mai sauk'i tunda gashi naji da kunne na. Babu wanda ya bami tausayi sai Asad d'in da mahaifin sa, duk irin abubuwan da mahaifiyar sa tayi mana amma wallahi sai nake jin zuciyata tana tausaya mata dan Allah kad'ai yasan halin da take ciki a yanzu. Y'ay'anta da take alfahari take tutiya ace d'aya ne kawai mai amfani a cikin su? Muguntar wannan tana wane ta wannan, kowa a cikin su burin sa ya kawar da d'an uwan sa?."
Baba yace, "Hydar d'in shine abin mamaki, ki tuna yadda yake shigewa Asad d'in gaba a akan komai hatta auren sa da Rauda shine ya assa shi ashe yana da manufar yin hakan badan Allah ya aikata ba. Yafi kowa bani mamaki ya kuma fi kowa bani tsoro, domin kaji tsoron maqiyin ka mai fuska biyu gwar wanda zai nuna maka kai tsaye baya sonka da wanda zai dinga yi maka kwantan b'auna."
Umma tace, "Shi mai martaban ya zaiji?. K'anin sa uwa d'aya uba d'aya, matar sa kuma uwar gidan sa, ga ita kanta babar Asad d'in, ga y'ay'an sa guda biyu. In ba namijin gaske mai dakakkiyar zuciya ba sai ya yanke jiki ya fad'i ya had'u da lalurar shanyewar b'arin jiki. Ace duk wanda ya aikata maka sharri jinin kane da matan ka?."
Baba yace, "Allah baya cutar da bawa akan laifin da bai aikata ba, duk wanda ya kasance mai yawan addu'a da neman zab'in Allah Allah bazai barshi da kansa ba sai ya shiga cikin lamarin sa. Yanzu ki duba shi Wazirin cikin lokaci kad'an Allah ya nuna masa sakayya babu b'ata lokaci y'ay'an sa biyu sun rasu a lokaci d'aya. Ni na d'auka ma yara ne fa ashe dukkan su babu wanda bai kai munzalin aure ba babu kamar namijin ma da ya girma sosai. Abin mamaki da d'aure kai turaren da aka bashi da nufin kashe Asad da baban sa suka d'auka sukayi amfani dashi su suka mutu. Dan Allah in baka ji tsoron Allah a lamarin nan ba tsoron me zaka ji?. In bakayi imani da Allah ba dawa zakayi imani?. Kai Allah kasa mufi k'arfin zuciyar mu."
Umma girgiza kai kawai take yi cikin rud'ani zuciyar ta ta karye tace, "Kaji tsoron wanda aka zalunta in Allah ya tashi saka masa, yanzu kalli cikin lokaci kad'an Allah ya nuna masa bai isa yayi abinda bai nufa ba. Ita kuma uwar gidan garin son a kashe wani kaso kashe ta in mai hankali ce iya wannan ya isheta ishara, kalli ita mahaifiyar tasu duk alfaharin da take dasu da nuna talaka ba komai bane sai gashi alfarmar talakan taci kuma y'ay'an nata guda ukun d'aya ne kawai mai amfani a ciki. Shi Aliyun da ake nufin kashe d'an uwan sa dashi har ana so a saka shi hauka sai gashi......." umma bata k'arasa ba sai tace, "Kai Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, ya hayyu ya qayyum ka saka mufi k'arfin zuciyar mu, ka tsare mu ka kare mu a duk inda muke kasa mu rinyaji zuciyar mu ba ita ta rinjaye mu ba" Umma ta fad'a tana d'aga hannun ta sama.
Baba ya amsa da amin sukayi shiru dukkan su kafin Baba yace, "Ni daman nasan babu ta yadda za'ayi Asad ya rsntse yace bashi ya saki Rauda ba akan k'arya, ashe duka aikin d'an uwan sane." Umma bata ce komai ba girgiza kai kawai take yi kafin ta sauke numfashi tace, "Duka haka Allah ya nufa ya kuma k'addara, shekara har ta kusa zagowa da bikin sai yanzu ake samun sassauci a lamarin auren nasu. Ni wallahi yanzu abin yafi na baya bani tsoro, kaga Hydar d'in nan gani nake kamar bazai bar Rauda ba dan babu alamun nadama fa a tare dashi."
Baba yace, "yadda Allah ya kare Asad da mahaifin sa haka Allah zai kare ta, zuciyar ta a wanke take bata tab'a nufar wani da sharri ba Allah bazai bari a cuce ta ba." Umma ta d'aga kai kawai Baba ya tashi ya fita zuwa masallaci dan yaji kiran sallar i'sha itama ta tashi ta tayar da sallah.
Sai bayan ta idar ta duba Rauda ta ganta a zaune da alama ma tayi sallah itama ta koma ta kawo mata abinci da kanta ta tilasta mata taci badan taso ba dan ita har yanzu zuciyar ta bata amince cikin Asad ne a jikin ta ba.
*☆☆☆*
Cikin awa da bai wuce uku ba an chanja komai na b'angaren mai Martaba Asad hatta carpet an cire shi an saka wani dan mahaifin sa yace bai amince da komai na ciki ba. Dukka kayan sawar Asad dana Aliyu an fito dasu daman mai martaba ya bayar da order dinki da alkyabba manya-manya ta Asad duk an kawo an saka ya koma sabo dal.
Yana tsaye a jikin window yana kallon jama'ar gidan da suke ta kai kawo ya sauke numfashi ya juyo yana kallon falon ba komai ne yake fad'o masa ba sai zaman Jidda a cikin sa ita da Yayan sa. Tsaki yaja ya d'auke kansa yana cize baki, "Hydar!" Ya furta a bayyane yana lumshe idanun sa da suka kankance sabida tashin hankali da b'acin rai.
Zuciyar sa bugawa take yi Allah ya sani yana qaunar Hydar da zuciya d'aya duk abin nan da fari baiji son sa ya fita daga zuciyar sa ba saima cutar dashi da son yake so yayi. Barin jikin window d'in yayi ya k'araso cikin falon yana niyar sauka yaga mahaifin sa na yawowa saman.
Dole ya koma da baya ya bashi hanya ya wuce ya zauna ya k'araso ya zauna a k'asan carpet yace, "Barka da zuwa." Mai martaba yace, "Ina kake niyar zuwa haka?." Asad yace, "Zanje wajan Mama ne hankalina yak'i kwanciya ina so na ganta."
"Ban amince da fitar sirrin nan da kake yi ba kayi fitar da ko wanne saraki yake yi." Asad yace, "In Allah ya amince zanyi abinda akace." Mai martaba yace, "Ya batun matar ka Jidda?."
Gaban sa ya fad'i matuk'a ya d'ago yace, "Allah ya k'ara maka lafiya ni ba matata bace ba." Mai martaba yace, "Matar kace Asad, shari'a ta baka d'an cikin ta duk da ba naka bane. Ka tambayi ya lafiyar ta take?."
Asad yace, "Ina neman afuwar ka dan ni gaskiya indai dan igiyar aurena da yake kanta ne na jima da datse ta, na sake ta!" Ya furta a sanyaye yana kallon mahaifin nasa da shima yake kallon sa da nasa mamakin.
"Ka sake ta fa kace Asad? Waye ya fad'a maka shugaba yana saki?. Kaifa sarki ne shugaba ne da zaka daqile yawaitar sakin aure da ake yi amma da kanka kake furta ka sake ta?."
Asad yace, "Allah ya wuci zuciyar mahaifina, bazan iya zama da ita ba mahaifina ya shaida ita d'in fasiqa ce taya zan iya zama da wacce tayi alfasha da auren ta tana sane?. Daman can zab'in Mama ce nayi biyayya ne na aure ta badan ina so ba sai dan gudun b'acin ran Mama, yanzu kuma ga abinda ya biyo baya zama na da ita ya haramta har abada. Batun da da mai martaba yake yi jinin Aliyu jinina ne zan iya rik'e masa y'ay'a d'ari indai akace jinin sane koda ba y'ay'an sunnah bane ba, amma bazan iya zama da ita ba."
Mai martaba da yake jin sa yasan gaskiya yake fad'a masa amma yana gudun zubewar k'imar gidan dan in akaji labarin Asad ya saki Jidda ga d'a kuma sunan gidan da tarihin gidan gabad'aya ya lalace. Duk sanda aka bud'e ido akaga baby Jidda sai Rauda kowa zai ta tunanin inda take k'arshe a fara mumman zato a kan hakan. Yace, "Asad nasan gaskiya kake fad'a, amma ina so ka duba yanayin gidan da kake da kuma matsayin da kake dashi, me mutanen gari dama jama'ar gidan nan da basu san abinda ya faru ba in akace ka saki matar ka bayan tana da cikin ka?." Asad ya kalli mahaifin sa jin ya ambaci ciki sa sai mai martaba yayi murmushi yace, "Nasan ba jinin ka bane amma cikin Aliyu naka ne, abinda yayi ka shine yayi Aliyu. Kowa yasan Jidda matar kace ya kenan in akace yau babu Jidda a gidan sai wata daban me hakan yake nufi?."
Asad yace, "Ban tari numfashin mai martaba ba, amma ina so a duba lamarin wallahi bazan iya zama da ita ba, kuma ni na riga na yanke hukunci gashi na sanar da mahaifina bana tunanin zan iya yin wani hukuncin da ba wannan ba, ina neman afuwar ka akan wannan bazan iya ba wallahi" ya fad'a yana kallon k'asa zuciyar sa na rawa in ya tuna abinda ya faru sai yaji jikin sa kamar ana kwashe masa kuzari sa gabad'aya komai sai ya tsaya masa cak.
[17/12, 10:45 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*083.*
Mai martaba kallon sa yake yi ganin yadda jikin sa yayi sanyi ya sauke numfashi yasan daman abu ne mai wahala amma ya za'ayi dole ayi wani abun dan b'oye wani abun. Yace, "Asad bank'i ta taka ba, amma yanzu ya kenan in mutanen gari suka ji ka rabu da matar ka?." Asad yace, "Allah ya taimaki Abba ni a yanzu ba matata bace, tasan na saketa na fad'a mata baki da baki tun lokacin da take kirana da Aliyu."