Sashe 69
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suhaima tace, "Amma da an tura ance masa kece da kanki gani nake bazai ki sauraren ki ba." Mama tace, "Jiya an sanar dashi ashe shi baya alfarma. Banda dole me zai kawo ni wajan nan?, Sadiya ta cuce ni." Suhaima bata ce komai ba tabi bayan napep d'in da Rauda ta hau har k'ofar gidan su ta sauka ta biya shi sannan ta shiga.
Suhaima jira take Mama tayi magana ita kuma ta rasa me zata ce ne, a zahiri tana son ganin Baba malam kodan bakin da yayi yawa akan aikin sa amma kuma bata tunanin zata iya neman alfarma a wajan wasu mutanen duba da matsayin da take dashi.
Dan k'aramin tsaki taja kana tace, "Juya mu koma gida." Ba musu ta juya suka d'auki hanyar komawa gida. Bayan sun sauka direct b'angaren mai martaba Mama ta wuce kamar ko yaushe Hydar yana zaune a gefen sa idanun mai martaba a kulle alamun yana bacci. Zama tayi a inda Hydar ya tashi ya bata tana kallon mijin nata kawai sai ta fashe da kuka.
Kuka take yi sosai Hydar yana tsaye yana ji kamar shima yayi mata kukan dan yasan an mata rauni a zuciyar ta ga rashin lafiyar da take fama da ita, ga Asad ga kuma Abba. Ta jima tana kukan kafin yazo ya dafa ta yace, "Dan Allah Mama kiyi hak'uri, Allah ya wuci zuciyar ki." Sassauta kukan nata tayi ta kalle shi ta goge idanunta sai kuma ta mik'e tana kallon sa tace, "Hydar me ya same ka? Badai ciwon kane zai tashi ba? Kayi min rai kar ciwon ka ya tashi in hakan ta faru ban san ya zanyi ba, ba Asad ba kai ba Aliyu."
"Kiyi hak'uri Mama" ya fad'a a tausahe ta kalle shi tace, "Ina Asad?." Ya sauke numfashi yace, "Mai martaba ya tafi England shida matar sa." Runtse ido tayi bakin ta yana rawa tace, "ya tafi ban sani ba, meyasa yake min haka Hydar?" Ta fad'a hawaye na sake zubo mata Hydar ya rik'e ta sosai duk da ciwon da yake ji a zuciyar sa da kansa.
"Ranki ya dad'e dan Allah ki daina kuka mutane suna shigowa ba girman ki bane" ya fad'a a tausahe ta goge idanun ta ta sauke numfashi ta juya ta fita daga d'akin. Numfashi ya sauke domin shima dauriya kawai yake yi mugun ciwo kansa yake masa zai iya cewa ciwon sa yana gab da tashi baya so ya nuna mata ne dan kar hankalin ta ya tashi.
D'aki ta koma ta kwanta ta fashe da kuka mai tab'a zuciya kanta yana sarawa zuciyar ta na tsagaita bugawa, ta jima tana kuka kafin ta sassauta ta mik'e zaune kanta yana mugun sarawa ta dafe kai da hannu biyu sabida ji take kamar zai fashe. Wayar ta take ji tana ihu bata iya dauka ba sai da taji kiran yayi yawa ta mik'a hannu ta d'auka ba tare da ta duba ba taji ance, "Yaya Rabi'atu." Jin muryar k'anwar ta ya saka ta bud'e baki tace, "Uhumm." Daga can b'angaren tace, "Subahanallah Yaya meya same ki haka naji muyar ki kamar mai kuka?."
Jin bata amsa ba ya saka yace, "Ko akan maganar da Yaya Babba ta fad'a mana ne? Nasan ma itace ta mayar dake haka Yaya daman maganar gaskiya kin sake da wannan Sadiyan da yawa, ko wanne sirrin ki ta sani bakya b'oye mata komai ba dole ta samu lagon ki da sauri haka ba. Yanzu ba wannan ba ya riga ya faru ki daure a bazama nema masa magani muma nan muna tayi ko za'a dace."
Mama ta cize bakin ta tace, "Na rasa abinda zanyi."
"Ki tuna, sai kin tuna sannan zaki aiwatar da komai wannan zaman naki bazai haifar da komai ba sai dai ma ya saka ki sake nisanta dashi. Mahaifin sa bashi da lafiya balle ya taimake ki dole ki dage." Bata amsa ba ta yanke wayar ta kwanta tana sauke numfashi zuciyar ta cike da tunane-tunane kafin kuma bacci ya d'auke ta.
Data farka taji dad'in baccin sosai tayi wanka ta fito babban falon ta hadimai suna ta hidama ta zauna ta kalli Jakadiyar ta tayi mata alama da tazo, jiki na rawa ta k'araso ta zube a gabanta Mama tayi banza da ita kamar bata san wata wajan ba sai daga baya tace, "Kin san wani Baba Malam?." Jakadiya ta duk'ar da kai tace, "Allah yaja da ran fulani na san shi, kwanaki akwai matsalar sammu da aka yiwa dan wajena dana je na same shi cikin ikon Allah an samu waraka."
Mama ta sake yin shiru kamar bata ji ba kafin tace, "Taya kika samu ganin sa?." Jakadiya tace, "Ranki ya dad'e ta hanyar Gwaggo da take b'angaren k'aramar Fulani na ganshi." Mama ta sauke numfashi tace, "Jeki ki kira min ita."
"An gama ranki ya dad'e" tana fad'a ta mik'e ta fita da sauri Mama ta kwantar da kai a jikin kujera tana jiran dawowar su.
Ba jimawa suka shigo su biyu suka zube a a gabanta Gwaggo tace, "Allah yaja zamanin Fulani, yaja da ranki ya k'ara miki lafiya." Mama tace, "Wa kika sani ya kai ki wajan wani malami Baba Malam?." Tayi mata jinjina kana tace, "Allah yaja zamanin ki akwai wata mahaifiyar k'awar y'ata Binta ita kuma k'anwar sace ta dalilin ta na ganshi har na yiwa Jakadiya iso wajan sa." Mama ta furzar da iska tace, "Abinda nake kuje gidan su kuzo min da k'anwar tasa nan." A tare suka amsa da fad'in, "An gama ranki ya dad'e" suka mik'e suka fita.
Suna fita mota suka hau zuwa gidan su Rauda suka same su kamar ko yaushe suna tare a zaune harda Inna ana ta hira suka shiga da sallama, bayan sun gaisa ne Gwaggo tace, "Rauda shugabar muce ta taso mu yanzu ta aiko mu." Umma tace, "Wacce kenan?."
Gwaggo tace, "Fulani Rabi'atu mana mahaifiyar Asad.." Umma da mamaki tace, "To lafiya dai?."
Gwaggo tace, "lafiya lau, cewa tayi nazo na tawo mata dake wajan ta." Rauda tace, "Wacce shugabar taku kenan Gwaggo wai?."
"Yanzu fa na fad'a Rauda, Shugabar mu gimbiya mana, matar sarki kuma babar sarki. Fulani Rabi'atu babar sarki Asad."
Gaban Rauda ya yanke ya fad'i ta daure tace, "to me Umma zatayi mata zata ce a kai mata ita?." Jakadiya tace, "Kwantar da hankalin ki yarinya, tana son ganin Baba malam ne akan matsalar mai martaba duk da bata fad'a mana matsalar ba amma nasan akan sane zata je, to kunfi kowa sanin halin sa baya danne lokacin talakawa sabida masu mulki taje amma bata samu ganin sa ba shine take tambaya ta na sani nake sanar da ita na tab'a zuwa na ganshi ta dalilin Gwaggo itama kuma ta dalilin ku, shine tace muzo aje da Umman ki."
Inna tace, "Kenan alfarma take so ayi mata?." Jakadiya tace, "Eh to kusan hakan zamu ce." Rauda tace, "Wallahil azim Ummana bazata je ba, in ita bazata tako k'afar ta tazo nan ta nemi alfarmar ba tasha zaman ta ita take nema ba mu ba."
Jakadiya tace, "Hattara y'an mata magana ake ta Fulani Rabi'atu" ta fad'a tana murmushi tana kallon Rauda. Rauda tace, "in ma Asad d'in ne da kansa ba babar saba wallahi bazata je ba. Dan ma ta raina mana hankali tana neman alfarma kuma ace Umman ce ma zata je wajanta kamar itace take nema?. Itafa take nema bami ba in bazata zo ba tasha zaman ta Umma ce dai bazata ba." Gwaggo tace, "Haba Rauda sai magana kike baki bari munji ta bakin Umman taki ba."
Umma tace, "Abinda Rauda tace shine daidai ai Gwaggon Habiba, zan iya yi mata alfarmar ganin Baba malam wannan ba komai bane amma sai dai tazo inda nake badai ni naje ba. Itace take nema bani nake nema ba dan haka bazan je inda take ba."
Gwaggo ta kalli Jakadiya tace, "to kinji." Jakadiya tace, "ta yaya zamu sanar da ita wannan sak'on mai tsauri? Kinfi kowa sanin halin ta fa." Gwaggo tace, "koma meye haka zamu jure, tashi muje." Suka tashi suka yi sallama dasu suka koma.
Da suka koma basu ganinta ba sai da yamma suka zauna a gabanta dukkan su tace, "Ina jin ku." Gwaggo tayi k'arfin halin cewa, "Ina neman afuwar fulani akan abinda zai fito daga bakina. Munje gidan amma sun tabbatar mana da sai dai Fulani da kanta taje ta nemi alfarma a wajan su amma su baza su zo ba, Tuba nake ranki ya dad'e" ta fad'a da girmamawa tana kallon Mama.
Mama tayi k'aramin tsaki tace, "kun fad'a musu wacece ni?." Jakadiya tace, "kwarai ranki ya dad'e."
Ta daki kujera tace, "Me ake yi da neman alfarma wajan talakawa...? Mtswww basu kai matsayin na nemi alfarma a wajan su ba. Ku bani waje" ta fad'a tana yi musu alamun su tashi da hannun ta suka fita jiki na rawa ita kuma ta shiga kiran number Asad.
Bata samun sa haka ta hak'ura ta ajjiye wayar a gefen ta lumshe idanu abubuwa sun taru sun cushe mata kanta da zuciyar ta. Bayan sallar i'sha suna zaune ita da Hydar da Suhaima babu mai magana cikin su sai Hydar da yake dafe kansa sabida ciwon da yake masa yana zaune amma jiri yake ji sosai kamar ma zai kifa. Mama ce ta kalle shi tace, "Hydar ya dai?." Ido ya bud'e ya kalle ta sai kuma ya kulle ya furta, "Washhhhh" sai ya kifa kansa a kan kujera yana juya kansa.
Mama tace, "Subahanallah, Hydar lafiya?." Ta fad'a tana tasowa tazo inda yake ta rik'e shi taji kansa yayi mugun zafi tana jijjiga shi amma sai taga yayi luf alamun ya suma.
Suhaima hankalin ta ya tashi tana kusa da Mama ta jijjiga shi Mama ma haka, "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Hydar! Ka tashi dan Allah kar ciwon ka ya tashi a wannan yanayin da nake ciki. Hydar! Hydar!!" Ta fad'a tana sake girgiza shi amma babu alamun motsi a tare dashi alamun ya tafi doguwar suman da ya saba tafiya lokaci zuwa lokaci.
Suhaima jira take Mama tayi magana ita kuma ta rasa me zata ce ne, a zahiri tana son ganin Baba malam kodan bakin da yayi yawa akan aikin sa amma kuma bata tunanin zata iya neman alfarma a wajan wasu mutanen duba da matsayin da take dashi.
Dan k'aramin tsaki taja kana tace, "Juya mu koma gida." Ba musu ta juya suka d'auki hanyar komawa gida. Bayan sun sauka direct b'angaren mai martaba Mama ta wuce kamar ko yaushe Hydar yana zaune a gefen sa idanun mai martaba a kulle alamun yana bacci. Zama tayi a inda Hydar ya tashi ya bata tana kallon mijin nata kawai sai ta fashe da kuka.
Kuka take yi sosai Hydar yana tsaye yana ji kamar shima yayi mata kukan dan yasan an mata rauni a zuciyar ta ga rashin lafiyar da take fama da ita, ga Asad ga kuma Abba. Ta jima tana kukan kafin yazo ya dafa ta yace, "Dan Allah Mama kiyi hak'uri, Allah ya wuci zuciyar ki." Sassauta kukan nata tayi ta kalle shi ta goge idanunta sai kuma ta mik'e tana kallon sa tace, "Hydar me ya same ka? Badai ciwon kane zai tashi ba? Kayi min rai kar ciwon ka ya tashi in hakan ta faru ban san ya zanyi ba, ba Asad ba kai ba Aliyu."
"Kiyi hak'uri Mama" ya fad'a a tausahe ta kalle shi tace, "Ina Asad?." Ya sauke numfashi yace, "Mai martaba ya tafi England shida matar sa." Runtse ido tayi bakin ta yana rawa tace, "ya tafi ban sani ba, meyasa yake min haka Hydar?" Ta fad'a hawaye na sake zubo mata Hydar ya rik'e ta sosai duk da ciwon da yake ji a zuciyar sa da kansa.
"Ranki ya dad'e dan Allah ki daina kuka mutane suna shigowa ba girman ki bane" ya fad'a a tausahe ta goge idanun ta ta sauke numfashi ta juya ta fita daga d'akin. Numfashi ya sauke domin shima dauriya kawai yake yi mugun ciwo kansa yake masa zai iya cewa ciwon sa yana gab da tashi baya so ya nuna mata ne dan kar hankalin ta ya tashi.
D'aki ta koma ta kwanta ta fashe da kuka mai tab'a zuciya kanta yana sarawa zuciyar ta na tsagaita bugawa, ta jima tana kuka kafin ta sassauta ta mik'e zaune kanta yana mugun sarawa ta dafe kai da hannu biyu sabida ji take kamar zai fashe. Wayar ta take ji tana ihu bata iya dauka ba sai da taji kiran yayi yawa ta mik'a hannu ta d'auka ba tare da ta duba ba taji ance, "Yaya Rabi'atu." Jin muryar k'anwar ta ya saka ta bud'e baki tace, "Uhumm." Daga can b'angaren tace, "Subahanallah Yaya meya same ki haka naji muyar ki kamar mai kuka?."
Jin bata amsa ba ya saka yace, "Ko akan maganar da Yaya Babba ta fad'a mana ne? Nasan ma itace ta mayar dake haka Yaya daman maganar gaskiya kin sake da wannan Sadiyan da yawa, ko wanne sirrin ki ta sani bakya b'oye mata komai ba dole ta samu lagon ki da sauri haka ba. Yanzu ba wannan ba ya riga ya faru ki daure a bazama nema masa magani muma nan muna tayi ko za'a dace."
Mama ta cize bakin ta tace, "Na rasa abinda zanyi."
"Ki tuna, sai kin tuna sannan zaki aiwatar da komai wannan zaman naki bazai haifar da komai ba sai dai ma ya saka ki sake nisanta dashi. Mahaifin sa bashi da lafiya balle ya taimake ki dole ki dage." Bata amsa ba ta yanke wayar ta kwanta tana sauke numfashi zuciyar ta cike da tunane-tunane kafin kuma bacci ya d'auke ta.
Data farka taji dad'in baccin sosai tayi wanka ta fito babban falon ta hadimai suna ta hidama ta zauna ta kalli Jakadiyar ta tayi mata alama da tazo, jiki na rawa ta k'araso ta zube a gabanta Mama tayi banza da ita kamar bata san wata wajan ba sai daga baya tace, "Kin san wani Baba Malam?." Jakadiya ta duk'ar da kai tace, "Allah yaja da ran fulani na san shi, kwanaki akwai matsalar sammu da aka yiwa dan wajena dana je na same shi cikin ikon Allah an samu waraka."
Mama ta sake yin shiru kamar bata ji ba kafin tace, "Taya kika samu ganin sa?." Jakadiya tace, "Ranki ya dad'e ta hanyar Gwaggo da take b'angaren k'aramar Fulani na ganshi." Mama ta sauke numfashi tace, "Jeki ki kira min ita."
"An gama ranki ya dad'e" tana fad'a ta mik'e ta fita da sauri Mama ta kwantar da kai a jikin kujera tana jiran dawowar su.
Ba jimawa suka shigo su biyu suka zube a a gabanta Gwaggo tace, "Allah yaja zamanin Fulani, yaja da ranki ya k'ara miki lafiya." Mama tace, "Wa kika sani ya kai ki wajan wani malami Baba Malam?." Tayi mata jinjina kana tace, "Allah yaja zamanin ki akwai wata mahaifiyar k'awar y'ata Binta ita kuma k'anwar sace ta dalilin ta na ganshi har na yiwa Jakadiya iso wajan sa." Mama ta furzar da iska tace, "Abinda nake kuje gidan su kuzo min da k'anwar tasa nan." A tare suka amsa da fad'in, "An gama ranki ya dad'e" suka mik'e suka fita.
Suna fita mota suka hau zuwa gidan su Rauda suka same su kamar ko yaushe suna tare a zaune harda Inna ana ta hira suka shiga da sallama, bayan sun gaisa ne Gwaggo tace, "Rauda shugabar muce ta taso mu yanzu ta aiko mu." Umma tace, "Wacce kenan?."
Gwaggo tace, "Fulani Rabi'atu mana mahaifiyar Asad.." Umma da mamaki tace, "To lafiya dai?."
Gwaggo tace, "lafiya lau, cewa tayi nazo na tawo mata dake wajan ta." Rauda tace, "Wacce shugabar taku kenan Gwaggo wai?."
"Yanzu fa na fad'a Rauda, Shugabar mu gimbiya mana, matar sarki kuma babar sarki. Fulani Rabi'atu babar sarki Asad."
Gaban Rauda ya yanke ya fad'i ta daure tace, "to me Umma zatayi mata zata ce a kai mata ita?." Jakadiya tace, "Kwantar da hankalin ki yarinya, tana son ganin Baba malam ne akan matsalar mai martaba duk da bata fad'a mana matsalar ba amma nasan akan sane zata je, to kunfi kowa sanin halin sa baya danne lokacin talakawa sabida masu mulki taje amma bata samu ganin sa ba shine take tambaya ta na sani nake sanar da ita na tab'a zuwa na ganshi ta dalilin Gwaggo itama kuma ta dalilin ku, shine tace muzo aje da Umman ki."
Inna tace, "Kenan alfarma take so ayi mata?." Jakadiya tace, "Eh to kusan hakan zamu ce." Rauda tace, "Wallahil azim Ummana bazata je ba, in ita bazata tako k'afar ta tazo nan ta nemi alfarmar ba tasha zaman ta ita take nema ba mu ba."
Jakadiya tace, "Hattara y'an mata magana ake ta Fulani Rabi'atu" ta fad'a tana murmushi tana kallon Rauda. Rauda tace, "in ma Asad d'in ne da kansa ba babar saba wallahi bazata je ba. Dan ma ta raina mana hankali tana neman alfarma kuma ace Umman ce ma zata je wajanta kamar itace take nema?. Itafa take nema bami ba in bazata zo ba tasha zaman ta Umma ce dai bazata ba." Gwaggo tace, "Haba Rauda sai magana kike baki bari munji ta bakin Umman taki ba."
Umma tace, "Abinda Rauda tace shine daidai ai Gwaggon Habiba, zan iya yi mata alfarmar ganin Baba malam wannan ba komai bane amma sai dai tazo inda nake badai ni naje ba. Itace take nema bani nake nema ba dan haka bazan je inda take ba."
Gwaggo ta kalli Jakadiya tace, "to kinji." Jakadiya tace, "ta yaya zamu sanar da ita wannan sak'on mai tsauri? Kinfi kowa sanin halin ta fa." Gwaggo tace, "koma meye haka zamu jure, tashi muje." Suka tashi suka yi sallama dasu suka koma.
Da suka koma basu ganinta ba sai da yamma suka zauna a gabanta dukkan su tace, "Ina jin ku." Gwaggo tayi k'arfin halin cewa, "Ina neman afuwar fulani akan abinda zai fito daga bakina. Munje gidan amma sun tabbatar mana da sai dai Fulani da kanta taje ta nemi alfarma a wajan su amma su baza su zo ba, Tuba nake ranki ya dad'e" ta fad'a da girmamawa tana kallon Mama.
Mama tayi k'aramin tsaki tace, "kun fad'a musu wacece ni?." Jakadiya tace, "kwarai ranki ya dad'e."
Ta daki kujera tace, "Me ake yi da neman alfarma wajan talakawa...? Mtswww basu kai matsayin na nemi alfarma a wajan su ba. Ku bani waje" ta fad'a tana yi musu alamun su tashi da hannun ta suka fita jiki na rawa ita kuma ta shiga kiran number Asad.
Bata samun sa haka ta hak'ura ta ajjiye wayar a gefen ta lumshe idanu abubuwa sun taru sun cushe mata kanta da zuciyar ta. Bayan sallar i'sha suna zaune ita da Hydar da Suhaima babu mai magana cikin su sai Hydar da yake dafe kansa sabida ciwon da yake masa yana zaune amma jiri yake ji sosai kamar ma zai kifa. Mama ce ta kalle shi tace, "Hydar ya dai?." Ido ya bud'e ya kalle ta sai kuma ya kulle ya furta, "Washhhhh" sai ya kifa kansa a kan kujera yana juya kansa.
Mama tace, "Subahanallah, Hydar lafiya?." Ta fad'a tana tasowa tazo inda yake ta rik'e shi taji kansa yayi mugun zafi tana jijjiga shi amma sai taga yayi luf alamun ya suma.
Suhaima hankalin ta ya tashi tana kusa da Mama ta jijjiga shi Mama ma haka, "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Hydar! Ka tashi dan Allah kar ciwon ka ya tashi a wannan yanayin da nake ciki. Hydar! Hydar!!" Ta fad'a tana sake girgiza shi amma babu alamun motsi a tare dashi alamun ya tafi doguwar suman da ya saba tafiya lokaci zuwa lokaci.