Sashe 5
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Habiba tace, "bata da imani wannan babar tasa tsaf zata aikata, bana son talaka bata son talaka ya rab'e ta, amma in sha Allah sai kin shiga gidan nan matsayin matar sa in yaso ta mutu." Walida tace, "Ai na rantse da Allah zan so naji ace ta aure sa domin a nuna mata in Allah ya k'addara abu babu wanda ya isa ya canja."
Rauda tace, "Nidai ku cigaba da yi min addu'a kawai amma ina cikin tsaka mai wuya. Kalli wuya na ku gani" ta fad'a tana d'aga kanta suka kalla ga shatin igiya a wajan tace, "jiya aka shigo har d'akin nan aka shak'e ni da igiya za'a kashe ni ashe sune suka aiko a kashe ni." Habiba ta dafe k'irji tace, "Mun shiga uku, daman ana irin haka a gaske?."
"Nima dai abinda na gani kenan Habiba, kisa fa." Rauda tace, "To kunga meye amfanin shiga ta gidan nan matsayin matar sa?." Walida tace, "Babu wallahi." Rauda tace, "Kuma nida shi bawan Allah nan bai tab'a cewa yana sona ba, maganar sacan biyar bata had'a mu balle na tabbatar da yana sona ko akasin haka."
Habiba tace, "Na fad'a miki dalilin sa baya iya doguwar magana haka Allah ya halicce shi ko ita babar tasa baya yi mata doguwar magana." Walida tace, "Amma matsayin wacce yake sonta yaci ace ya d'an yi mata magana kodan ya kafa gwamnatin sa a zuciyar ta. Itafa soyayya babu ruwan ta da wani mulki ko sarauta ko rashin maganar sa." Rauda tace, "gane min hanya Walida, babu maganar da ta tab'a had'a mu sai sau d'aya a haka zan aure shi shima?."
Habiba tace, "haka ne amma dai kun san halitta mutum baya canja kansa. Mudai muna addu'a Allah ya tabbatar da lamarin nan." Rauda bata ce komai ba tayi murmushi suka cigaba da hira sama-sama.
*☆☆*
Hankalin Mama baya jikin ta jin labarin jikin mahaifin ta yayi tsanani wajan ciwo ba b'ata lokaci ta d'auki hanyar Kano ita da jakadiyar ta da Suhaima. Da taje nan taga duk yadda ake fad'a mata yanayin jikin nasa yafi haka duka y'an uwan ta suna nan na nesa dana kusa kowa ka kalla kasan yana cikin yanayi mara dad'i.
Bayan sun baro inda yake suka ware kansu iya y'ay'an d'akin su kamar yadda suka saba tunda mahaifiyar su ta rasu basa shiga cikin y'an uwan su ware suke waje guda kamar ba jinin su ba. Suna tare su hud'u mata mazan guda uku suna nasu waje suke tattaunawa akan abubuwan da ya shafe su. Babbar cikin su itace mai hali d'aya da Mama ta kalle ta tace, "ya batun Asad kuwa?." Mama tace, "Hmm baki ga yadda na rame ba? Tashin hankali ya sako ni gaba akan auren nan nasa." Wacce take bin Mama tace, "Asad d'in aure zaiyi?." Mama tace, "Allah ya sawwake ai batun wannan aure an soke shi bai isa ya jawo min abinda fad'a a dangi ba." Y'ar autar su tace, "Abin fad'a a dangi? Auren shine zai zama abin fad'a?."
Babbar cikin su tace, "To abin fad'a mana in kuka ji yarinyar da ya d'auko zai aura sai abin ya baku mamaki; kamar Asad ace ya d'auko y'ar talakawa yace ita yake so?." Mama tace, "Ai baki K'arasa ba, gata bak'a ga muni gata gurguwa gata mai tallan abinci a kan titi." Wacce take bin Mama mai suna Maimuna tace, "Shi kuma a ina ya gano ta?." Mama tace, "Bari kedai kawai, Hydar ne ya buge ta a mota kafin ya kwanta ciwo shi kuma ya nemo ta da niyar yi mata magani shikenan fa sai ga magana wai sonta yake yi, kina jin maganar nan kin san akwai asiri a lamarin."
Y'ar autar su tace, "Ba wani asiri soyayya ce fa daga Allah ni banga aibu dan ya aure ta ba. Nidai nasan Asad bazai d'auko mara asali da ilimi ba, an fa daina wannan abun ace wai d'an sarauta sai y'ar sarauta indai Allah ya kulla kawai ayi." Maimuna tace, "Nima dai haka tunda har yana sonta ai zance ya k'are." Babbar cikin su tace, "Daman ku ai ba'a tab'a abin kirki daku. Yanzu namiji kamar Asad zaku goyawa baya ya auri yarinya mai kammin da aka lissafa?."
"To meye a ciki da ya auri Jiddan da take so ba gwara ita ba, Jiddan nan bata da tarbiya ko kad'an ga shegiyar rawar kai a cikin ta. Meye abin so a Jidda? Kyaunta ne kawai yake rud'ar Mama amma me take dashi?."
Babbar cikin su tace, "Ke malama bama son rashin kunya." Tab'e baki tayi suka tashi suka basu wajen yadda zasu fi jin dad'in tattaunawa.
Ta kalli Mama tace, "Kar fa ki amince da auren nan amincewar ki daidai yake da fad'uwar darajar ki a idanun kishiyoyin ki wallahi, ki dage kai da fata wajan ganin auren nan bai yu ba in kuwa ba haka ba kina ji kina gani wata y'ar talakawa zata kwance miki d'an ki domin nan gaba in zaki ganshi sai kin neme ta sabida ta fiki kusanci dashi." Mama ta sake zuwa wuya tace, "Bari kawai Yaya zan san abinda zanyi."
"Ya dai kamata" ta fad'a daga na suka cigaba da tattaunawa a kan lamarin jikin mahaifin su.
A Katagum kuma da yamma mai martaba ya nemi ganin Baba kamar yadda aka tsara su biyu ne kacal a d'akin ganin bak'i na musamman mai martaba yana kan kujara shi kuma yana k'asa a zaune mai martaba yace, "Dalilin da ya saka nace a kira min kai akan batun auren y'arka da Asad, wanne mataki ake kai a yanzu ta amince ita yarinyar?."
Baba ya gyara zaman sa yace, "Ranka ya dad'e ta amince; sai dai tana jin tsoron Fulani duba da abubuwan da suka faru bayan furta zai aure ta d'in da yayi."
Mai martaba ya murmusa har cikin zuciyar sa yaji dad'in hakan domin kuwa shi kad'ai yasan alkhairin da ya gani a auren Asad da Rauda yace, "Ba abar tsoro bace; kamar yadda ta isa dashi muma mun isa da ita kar taji tsoro indai ta amince shine abinda nake so naji." Ba tare da tunanin komai ba Baba yace, "ta amince ranka ya dad'e, naso ma ta biyo ni sai ta nuna min baza ta iya zuwan ba shiyasa nazo ni kad'ai."
Mai martaba yace, "Alhamdulillah. D'aurin auren nan kusa nake so ayi shi in yaso sai su tafi k'asar da za'a ayi mata aikin k'afar tare in sun dawo sai ayi biki a tare. Bana so ma yasan an d'aura auren sai bayan an d'aura in ba haka ba mahaifiyar sa zata iya canja masa ra'ayi lokaci guda. In Allah ya kai mu asabar jibi kenan ina so a d'aura musu aure da ita in da hali."
"Allah yaja da ran mai martaba ai babu komai umarni kawai zaka yanke mu namu aikin mu bi." Mai martaba yaji dad'in kalaman Baba ya d'auko wata leda a kusa dashi ya mik'awa Baba yace, "kud'in na gani ina so, kud'in lefe da duk wani abu dake yiwa mace. Bana so a d'auki lokacin da za'ace sai an had'o kaya shiyasa na bada wannan kud'in ayi amfani dasu." Baba ya karb'a ya koma ya zauna kana yace, "Allah ya taimake ka, muna godiya Allah yaja da rai Allah yasa ayi damu."
"Amin. Nine da godiya ai duk da abubuwan da suka faru aka amince aka bamu y'a kamar ta mai ilimin addini da tarbiyya." Baba dad'i yake ji har cikin b'argon sa yace, "Ranka ya dad'e dad'i mune ya kamata muji shi baku ba, Allah ya k'arawa mai martaba lafiya da imani muda aka had'a jini damu ai mune zamu gode."
Murmushi yayi kana yace, "Aje ayi komai yadda ya kamata in Allah ya kaimu jibin koma gobe juma'a za'a d'aura musu aure da ita dan bana so wani abu ya jifta da za'a fasa." Baba yace, "Goben ma yayi ranka ya dad'e Allah ya nuna mana." Daga haka sukayi sallama da Baba ya yi godiya sosai ya tashi ya tafi zuwa gida zuciyar sa fari kallllll kamar an wanke masa ita haka yake ji.
*sai Baba*💃🤣
[17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*029.*
Cikin tsantsar farin ciki Baba ya koma gida koda yaje bai sanar dasu komai ba ya adana kud'in a waje mai kyau ya cigaba da sabgar sa hankali kwance domin ya lashi takobin babu abinda zai hana auren Asad da Rauda koda bata so, daman Anas ya saka yake d'aga k'afa yanzu tunda babu batun sa ko ana muzuru ana shawo sai ya zama sirikin sarki mai jiran gado.
Lokacin da ya shiga gidan da magariba suna zazaaune a waje d'aya har su Inna suna kallon tv ya samu waje ya zauna ya kalli Rauda yace, "ya jikin naki?." Rauda tace, "Da sauk'i."
"Haka ake so. Wacce irin shawara kika yanke?." Rauda ta kalli Baba tace, "Akan me Baba?."
"Auren ki" ya bata amsa yana kallon ta. Kai ta saukar k'asa kana tace, "Bana ra'ayin auren sa gaskiya." Baba ya d'aure fuska yana kallon ta yace, "Kamar ya bakya ra'ayi?."
Rauda ta d'ago ido tace, "Eh Baba, bana son na aure shi." Baba yace, "To akan me bakya son auren sa? Wani abun kika fishi da bakya sonsa?." Umma ta bud'e baki da niyar bashi amsa ya d'aga mata hannu kana yace, "Kar naji bakin kowa a nan indai ba Rauda ba, da ita nake magana bada ku ba kar a saka min baki"ya fad'a a kausashe yana kallon ta. Dole tayi shiru ya mayar da kallon sa ga Rauda yace, "Ina jin ki." Rauda tace, "Ya fini komai Baba, kawai ni bana son auren sa ne sabida bana son sa." Baba ya gyara zama yana kallon ta yace, "ya kamata ki fara son sa kuwa domin auren ki dashi babu fashi."
Rauda tace, "Nidai ku cigaba da yi min addu'a kawai amma ina cikin tsaka mai wuya. Kalli wuya na ku gani" ta fad'a tana d'aga kanta suka kalla ga shatin igiya a wajan tace, "jiya aka shigo har d'akin nan aka shak'e ni da igiya za'a kashe ni ashe sune suka aiko a kashe ni." Habiba ta dafe k'irji tace, "Mun shiga uku, daman ana irin haka a gaske?."
"Nima dai abinda na gani kenan Habiba, kisa fa." Rauda tace, "To kunga meye amfanin shiga ta gidan nan matsayin matar sa?." Walida tace, "Babu wallahi." Rauda tace, "Kuma nida shi bawan Allah nan bai tab'a cewa yana sona ba, maganar sacan biyar bata had'a mu balle na tabbatar da yana sona ko akasin haka."
Habiba tace, "Na fad'a miki dalilin sa baya iya doguwar magana haka Allah ya halicce shi ko ita babar tasa baya yi mata doguwar magana." Walida tace, "Amma matsayin wacce yake sonta yaci ace ya d'an yi mata magana kodan ya kafa gwamnatin sa a zuciyar ta. Itafa soyayya babu ruwan ta da wani mulki ko sarauta ko rashin maganar sa." Rauda tace, "gane min hanya Walida, babu maganar da ta tab'a had'a mu sai sau d'aya a haka zan aure shi shima?."
Habiba tace, "haka ne amma dai kun san halitta mutum baya canja kansa. Mudai muna addu'a Allah ya tabbatar da lamarin nan." Rauda bata ce komai ba tayi murmushi suka cigaba da hira sama-sama.
*☆☆*
Hankalin Mama baya jikin ta jin labarin jikin mahaifin ta yayi tsanani wajan ciwo ba b'ata lokaci ta d'auki hanyar Kano ita da jakadiyar ta da Suhaima. Da taje nan taga duk yadda ake fad'a mata yanayin jikin nasa yafi haka duka y'an uwan ta suna nan na nesa dana kusa kowa ka kalla kasan yana cikin yanayi mara dad'i.
Bayan sun baro inda yake suka ware kansu iya y'ay'an d'akin su kamar yadda suka saba tunda mahaifiyar su ta rasu basa shiga cikin y'an uwan su ware suke waje guda kamar ba jinin su ba. Suna tare su hud'u mata mazan guda uku suna nasu waje suke tattaunawa akan abubuwan da ya shafe su. Babbar cikin su itace mai hali d'aya da Mama ta kalle ta tace, "ya batun Asad kuwa?." Mama tace, "Hmm baki ga yadda na rame ba? Tashin hankali ya sako ni gaba akan auren nan nasa." Wacce take bin Mama tace, "Asad d'in aure zaiyi?." Mama tace, "Allah ya sawwake ai batun wannan aure an soke shi bai isa ya jawo min abinda fad'a a dangi ba." Y'ar autar su tace, "Abin fad'a a dangi? Auren shine zai zama abin fad'a?."
Babbar cikin su tace, "To abin fad'a mana in kuka ji yarinyar da ya d'auko zai aura sai abin ya baku mamaki; kamar Asad ace ya d'auko y'ar talakawa yace ita yake so?." Mama tace, "Ai baki K'arasa ba, gata bak'a ga muni gata gurguwa gata mai tallan abinci a kan titi." Wacce take bin Mama mai suna Maimuna tace, "Shi kuma a ina ya gano ta?." Mama tace, "Bari kedai kawai, Hydar ne ya buge ta a mota kafin ya kwanta ciwo shi kuma ya nemo ta da niyar yi mata magani shikenan fa sai ga magana wai sonta yake yi, kina jin maganar nan kin san akwai asiri a lamarin."
Y'ar autar su tace, "Ba wani asiri soyayya ce fa daga Allah ni banga aibu dan ya aure ta ba. Nidai nasan Asad bazai d'auko mara asali da ilimi ba, an fa daina wannan abun ace wai d'an sarauta sai y'ar sarauta indai Allah ya kulla kawai ayi." Maimuna tace, "Nima dai haka tunda har yana sonta ai zance ya k'are." Babbar cikin su tace, "Daman ku ai ba'a tab'a abin kirki daku. Yanzu namiji kamar Asad zaku goyawa baya ya auri yarinya mai kammin da aka lissafa?."
"To meye a ciki da ya auri Jiddan da take so ba gwara ita ba, Jiddan nan bata da tarbiya ko kad'an ga shegiyar rawar kai a cikin ta. Meye abin so a Jidda? Kyaunta ne kawai yake rud'ar Mama amma me take dashi?."
Babbar cikin su tace, "Ke malama bama son rashin kunya." Tab'e baki tayi suka tashi suka basu wajen yadda zasu fi jin dad'in tattaunawa.
Ta kalli Mama tace, "Kar fa ki amince da auren nan amincewar ki daidai yake da fad'uwar darajar ki a idanun kishiyoyin ki wallahi, ki dage kai da fata wajan ganin auren nan bai yu ba in kuwa ba haka ba kina ji kina gani wata y'ar talakawa zata kwance miki d'an ki domin nan gaba in zaki ganshi sai kin neme ta sabida ta fiki kusanci dashi." Mama ta sake zuwa wuya tace, "Bari kawai Yaya zan san abinda zanyi."
"Ya dai kamata" ta fad'a daga na suka cigaba da tattaunawa a kan lamarin jikin mahaifin su.
A Katagum kuma da yamma mai martaba ya nemi ganin Baba kamar yadda aka tsara su biyu ne kacal a d'akin ganin bak'i na musamman mai martaba yana kan kujara shi kuma yana k'asa a zaune mai martaba yace, "Dalilin da ya saka nace a kira min kai akan batun auren y'arka da Asad, wanne mataki ake kai a yanzu ta amince ita yarinyar?."
Baba ya gyara zaman sa yace, "Ranka ya dad'e ta amince; sai dai tana jin tsoron Fulani duba da abubuwan da suka faru bayan furta zai aure ta d'in da yayi."
Mai martaba ya murmusa har cikin zuciyar sa yaji dad'in hakan domin kuwa shi kad'ai yasan alkhairin da ya gani a auren Asad da Rauda yace, "Ba abar tsoro bace; kamar yadda ta isa dashi muma mun isa da ita kar taji tsoro indai ta amince shine abinda nake so naji." Ba tare da tunanin komai ba Baba yace, "ta amince ranka ya dad'e, naso ma ta biyo ni sai ta nuna min baza ta iya zuwan ba shiyasa nazo ni kad'ai."
Mai martaba yace, "Alhamdulillah. D'aurin auren nan kusa nake so ayi shi in yaso sai su tafi k'asar da za'a ayi mata aikin k'afar tare in sun dawo sai ayi biki a tare. Bana so ma yasan an d'aura auren sai bayan an d'aura in ba haka ba mahaifiyar sa zata iya canja masa ra'ayi lokaci guda. In Allah ya kai mu asabar jibi kenan ina so a d'aura musu aure da ita in da hali."
"Allah yaja da ran mai martaba ai babu komai umarni kawai zaka yanke mu namu aikin mu bi." Mai martaba yaji dad'in kalaman Baba ya d'auko wata leda a kusa dashi ya mik'awa Baba yace, "kud'in na gani ina so, kud'in lefe da duk wani abu dake yiwa mace. Bana so a d'auki lokacin da za'ace sai an had'o kaya shiyasa na bada wannan kud'in ayi amfani dasu." Baba ya karb'a ya koma ya zauna kana yace, "Allah ya taimake ka, muna godiya Allah yaja da rai Allah yasa ayi damu."
"Amin. Nine da godiya ai duk da abubuwan da suka faru aka amince aka bamu y'a kamar ta mai ilimin addini da tarbiyya." Baba dad'i yake ji har cikin b'argon sa yace, "Ranka ya dad'e dad'i mune ya kamata muji shi baku ba, Allah ya k'arawa mai martaba lafiya da imani muda aka had'a jini damu ai mune zamu gode."
Murmushi yayi kana yace, "Aje ayi komai yadda ya kamata in Allah ya kaimu jibin koma gobe juma'a za'a d'aura musu aure da ita dan bana so wani abu ya jifta da za'a fasa." Baba yace, "Goben ma yayi ranka ya dad'e Allah ya nuna mana." Daga haka sukayi sallama da Baba ya yi godiya sosai ya tashi ya tafi zuwa gida zuciyar sa fari kallllll kamar an wanke masa ita haka yake ji.
*sai Baba*💃🤣
[17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*029.*
Cikin tsantsar farin ciki Baba ya koma gida koda yaje bai sanar dasu komai ba ya adana kud'in a waje mai kyau ya cigaba da sabgar sa hankali kwance domin ya lashi takobin babu abinda zai hana auren Asad da Rauda koda bata so, daman Anas ya saka yake d'aga k'afa yanzu tunda babu batun sa ko ana muzuru ana shawo sai ya zama sirikin sarki mai jiran gado.
Lokacin da ya shiga gidan da magariba suna zazaaune a waje d'aya har su Inna suna kallon tv ya samu waje ya zauna ya kalli Rauda yace, "ya jikin naki?." Rauda tace, "Da sauk'i."
"Haka ake so. Wacce irin shawara kika yanke?." Rauda ta kalli Baba tace, "Akan me Baba?."
"Auren ki" ya bata amsa yana kallon ta. Kai ta saukar k'asa kana tace, "Bana ra'ayin auren sa gaskiya." Baba ya d'aure fuska yana kallon ta yace, "Kamar ya bakya ra'ayi?."
Rauda ta d'ago ido tace, "Eh Baba, bana son na aure shi." Baba yace, "To akan me bakya son auren sa? Wani abun kika fishi da bakya sonsa?." Umma ta bud'e baki da niyar bashi amsa ya d'aga mata hannu kana yace, "Kar naji bakin kowa a nan indai ba Rauda ba, da ita nake magana bada ku ba kar a saka min baki"ya fad'a a kausashe yana kallon ta. Dole tayi shiru ya mayar da kallon sa ga Rauda yace, "Ina jin ki." Rauda tace, "Ya fini komai Baba, kawai ni bana son auren sa ne sabida bana son sa." Baba ya gyara zama yana kallon ta yace, "ya kamata ki fara son sa kuwa domin auren ki dashi babu fashi."