Sashe 12
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A b'angaren Asad yana zaune a falon yana cin nasa abincin hankali kwance babu tunanin an zuba masa wani abun a ciki ya gama ya d'auko kwalin sabuwar wayar da ya siya da sim card d'in k'asar ya kunna ya d'ora email d'in sa nan take komai nasa ya dawo kan wayar ya saka card d'in kana ya saka a chaji ya tashi domin bacci yake ji ya gaji, kallon d'akin da take yayi yaga haske har lokacin sai ya nufi d'akin k'irjin sa yana bugaw, yana bud'ewa ya ganta a kwance tana bacci ta cure waje d'aya da alama sanyi take ji.
Murmushi yayi kad'an wani abu yana motsawa a ransa wanda bai san meye shi baya k'arasa inda take ya rufa mata bargon ya kashe hasken d'akin sannan ya fita daga d'akin ya shiga nasa d'akin ya kwanta zuciyar sa cike da tunani kala-kala bacci ya d'auke shi.
Kiran asuba da ya karad'e d'akin da yake kwance ya farkar da Asad ya tashi yana yamutsa fuska dan rabon da yayi bacci mai tsaho irin sa babu farkawa har ya manta duk da ba wani mai tsahon bane amma a wajan sa mai tsaho ne, alwala yayi ya fito ya kalli d'akin da take yaga still babu haske ya k'arasa a nutse ya tura k'ofar d'akin sanyi ya dake shi yayi baya kad'an dan shi ba mutum ne mai son sanyi sosai ba, sake kutsa kai d'akin yayi har lokacin bacci take hankali kwance cikin bargo mai laushin gaske ta b'oye dukka jikin ta fuskar ta kawai ake gani.
A hankali yake takawa a nutse har ya isa kusa da ita fuskar ta yake kallo cikin shaukin sonta da kuma k'aunar ta da yake ji tana shiga cikin jikin sa a hankali kamar a lokacin ya fara sonta haka yake ji, kamar zai kai hannun sa kan fuskar ta sai kuma ya fasa ya janye tsaya ya nutsu sosai kamar na shi ba sannan ya fara bubbuga gadon a hankali. Bud'e ido yaga tayi suka had'a ido sai da yaga bacci ya sake ta baice komai ba ya fice ita kuma ta bishi da kallo kafin ta kalli agogon bangon d'akin sai kuma taji kira alamun za'a tayar da sallah.
Zaune ta mik'e tana goge idanun ta ta jawo kujerar ta zauna a kai zuwa band'aki tayi alwala ta fito ta tayar da sallah. Bayan ta idar d'auko wayar ta ta shiga application na karatun alkur'ani ta fara karantawa a zuciya amma bakin ta na motsawa. Bata jima sosai tana yi ba ta fara azkhar kamar koda yaushe har ta kai k'arshe ta ajjiye ta fara lazumi a zuciyar ta.
Motsin sa taji a bayan ta ya k'araso inda take ya kalli a.c d'akin har lokacin tana aiki ga kuma sanyin d'akin yace, "bakya jin sanyi?." Kallon sa tayi kamar baza tayi magana ba sai ta tuna nasihar Umma tace, "Ina kwana."
"Ya jiki?" Abinda yace kawai kenan ya ajjiye ledar hannun sa tace, "Da sauk'i."
Baice komai ba itama haka ya fita ta bishi da kallon mamaki tana jin zuciyar ta na karyewa hawaye suka fara zubo mata bata hana kanta ba ta dinga kuka har ta koma ta kwanta tana kuka bata kuma duba ledar ba.
Shima ya jima sosai yana karatun da ya saba yayi azkhar har k'arfe bakwai na safe yana zaune ya tashi ya shiga d'aki ya kwanta. K'arfe tara ya farka yayi wanka ya saka doguwar riga irin ta larabawa ya fito zuwa falon a lokacin ake danna door bell ya bud'e k'ofar ya karb'i abinci daga restaurant d'in hotel d'in ya mayar da k'ofar ya kulle. A kan table ya ajjiye abincin ya k'arasa inda ya jona ruwan zafi ya d'auko butar ya k'araso ya zauna ya had'a tea yana sha a nutse ya bud'e wanda aka kawo yaga kayan maiko ne kwai, dankali, planten, sai sandwich.
Sandwich d'in ya d'auka guda d'aya yana ci bayan ya gama ya rufe sauran ya mik'e k'afa akan table d'in ya d'auki remote yana canja channel d'in TV. Ajjiyewa yayi ya d'auki wayar sa ya kira number Hydar dan yasan yana can yana neman sa, bai d'auka ba bai kuma kira ba sai ya kira layin mai martaba.
D'auka akayi hakan ya saka shi ya nutsu ya sauke k'afar sa k'asa a nutse yace, "Assslamu alaikum." Daga can b'angaren Mai martaba yace, "Wa'alaika salam, Zaki ya kwanan Misra?." Murmushi yayi kana yace, "Alhamdulillah, Barka da safiya Takawa."
"Barkan ka Asad, ya kuka tashi?."
"Alhamdulillah."
"Ka kira gidan su ka had'a su da ita dai ko?." Asad yayi shiru alamun baiyi ba Mai martaba jin yayi shiru sai yace, "Hakan bai kamata ba ai Asad duk inda suke yanzu hankalin su yana kanta suna so suji ya take, ka kira ka had'a su suyi magana."
"In sha Allah" ya furta a hankali kafin Asad yace, "Abba Mamaaaa ta dawo?." Mai martaba yayi murmushi yace, "Bata dawo ba Asad, koda ta dawo kar ka damu komai zai zo da sauk'i kaji." Kai ya d'aga kamar yana gaban sa kafin yace, "Kayi gaggawar kaita asibitin ayi mata aikin nan, ka duba ina tunanin yau ne date d'in aikin da akayi booking za'a mata, ka duba dai Hydar yayi booking a Saudi German." Nan ma kai ya d'aga kamar yana ganin sa kafin yace, "In sha Allah za'a yi abinda akace." Daga nan sallama suka yi ya yanke wayar daidai nan kiran Hydar ya shigo ya d'auka.
"Our groom, how was your first night? I hope you enjoy it" Hydar ya fad'a cikin tsokana. Tab'e baki Asad yayi ya murmusa kad'an Hydar yana bashi nishad'i ba kad'an b kana yace, "First night? With who?."
"Your wife mana."
"U are not serious Hydar." Dariya Hydar yayi kad'an yace, "Oga Deaf as mijin aure, wallahi ganin abun nake kamar wasa fa."
Bai bashi amsa ba yasan kuma daman bazai ce ba hakan ya saka ya kuma cewa, "U know what deaf? Kar ka bari kayi asarar wannan time d'in da kuka samu tare kayi k'okarin nuna mata kana sonta da gaske in ka lura zaka ga kamar gani take tilasta mata akayi ta aure ka, so Is better ka nuna mata kana sonta sosai sonta ya saka ka auro ta ba wani abun ba, ka gane ai abinda nake nufi ina nufin dai ayi komai."
Baice komai ba Hydar yace, "Yeah kayi k'ok'ari before Mama ta gano komai ta dawo da kai gida." Gaban sa ya fad'i matuk'a ya sauke numfashi yace, "lemme call her, excuse me" ya fad'a yana niyar kashe wayar yaji Hydar yace, "Amma dai bada number nan zaka kira ta ba ko?." Asad yayi shiru bai magana ba Hydar ya kuma cewa, "Naga number Egypt kasan kuma bata san baka nan ba so gwara ka kira ta da layin ka in ba haka ba zata gane baka nan, daman jiya mun had'u dasu Mum sun ga wucewar ka."
"Ohhh god! Hydar I lost my phone" ya fad'a yana dafe kansa. Hydar yace, "nayu mamaki dana ga number outside country dan nasan baka canja number kai da taka kake using a ko wacce k'asa, to yanzu ya za'ayi kenan gashi babu damar yin swap online dole sai kazo Nigeria, ga Mama indai ka kira ta da wannan number zatayi saurin d'agowa baka nan kuma kasan baka fad'a mata ba."
Asad ya kasa cewa komai duk tsoro ya cika masa zuciya sam baya son abinda Mama zatayi fushi dashi gashi bazai iya jurewa har ya koma bai mata waya ba, beside bai san lokacin da zai koma Nigeria ba tunda ko aikin ma ba'a yi mata ba, laifi goma da shirin kenan ga laifin ya tawo babu izinin ta, ga laifin auren da yayi bata so, ga laifi rashin kiran ta waya sabida rashin layin sa bazai iya ba sam. Hydar ya katse masa tunani yace, "Ya za'ayi kenan Deaf?." Asad ya sauke numfashi kana yace, "bazan iya d'aukar wannan lokacin without nayi magana da Mama ba Hydar, I can't" ya fad'a a raunane kamar zaiyi kuka.
Hydar yace, "Yaushe za'a yi mata aikin da akayi booking? Ina jin yau ne in akayi mata aikin kaga zata jima a kwance sai ka siyi ticket kazo kayi swapping ka koma a gani na hakan zai fi." Asad baice komai ba ya yanke kiran dan bai san me zaice masa ba.
Shiru yayi yana kallon wani wajan daban dan Allah ya sani bazai iya jure har gobe ko jibi ba sannan yayi magana da Mama bazai iya jurewa ba sam. Motsin k'ofa yaji hakan ya saka ya juyo ya kalli inda yaji motsin ya ganta zaune a kan kujerar ta sanye da doguwar riga ta saka hula tayi kyau sosai kwana d'aya tal fuskar ta ta washe har annuri yake fitarwa, Kasa d'auke ido yayi daga kallon ta tana tawowa a kan keken wayar ta a cinyar da alama bata kula dashi bama.
Idon ta takai inda yake suka had'a ido sai gabanta ya fad'i ta d'auke ido gashi tazo kusa dashi ya bita da kallo ji yake kamar ya jawo ta jikin sa gabad'aya ko zai samu sassaucin abinda yake a ji a zuciyar sa, kallon sa take shima yana kallon ta kafin ya fara janye idanun sa daga kanta ya mayar kan TV. Itama bata ce komai tayi shiru bata motsa ba taji maganar sa yace, "your breakfast." Bata motsa ba taji kuma me yace shi kuma yasan taji shiyasa ya share ta.
Wayar sa ya d'auka ya kira number Baba aka d'auka suka gaisa ya mik'a mata wayar alamun ta karb'a, karb'a tayi ta saka a kunne jin muryar mahaifinta sai ta saki fara'a suka gaisa ta saka aka kaiwa Umma suka gaisa farin ciki ya cika zuciyar ta sun jima suna magana da Umma har ta fara kuka kafin ta kashe wayar bata bashi ba ta rik'e a hannun ta tana kuka sosai.
Murmushi yayi kad'an wani abu yana motsawa a ransa wanda bai san meye shi baya k'arasa inda take ya rufa mata bargon ya kashe hasken d'akin sannan ya fita daga d'akin ya shiga nasa d'akin ya kwanta zuciyar sa cike da tunani kala-kala bacci ya d'auke shi.
Kiran asuba da ya karad'e d'akin da yake kwance ya farkar da Asad ya tashi yana yamutsa fuska dan rabon da yayi bacci mai tsaho irin sa babu farkawa har ya manta duk da ba wani mai tsahon bane amma a wajan sa mai tsaho ne, alwala yayi ya fito ya kalli d'akin da take yaga still babu haske ya k'arasa a nutse ya tura k'ofar d'akin sanyi ya dake shi yayi baya kad'an dan shi ba mutum ne mai son sanyi sosai ba, sake kutsa kai d'akin yayi har lokacin bacci take hankali kwance cikin bargo mai laushin gaske ta b'oye dukka jikin ta fuskar ta kawai ake gani.
A hankali yake takawa a nutse har ya isa kusa da ita fuskar ta yake kallo cikin shaukin sonta da kuma k'aunar ta da yake ji tana shiga cikin jikin sa a hankali kamar a lokacin ya fara sonta haka yake ji, kamar zai kai hannun sa kan fuskar ta sai kuma ya fasa ya janye tsaya ya nutsu sosai kamar na shi ba sannan ya fara bubbuga gadon a hankali. Bud'e ido yaga tayi suka had'a ido sai da yaga bacci ya sake ta baice komai ba ya fice ita kuma ta bishi da kallo kafin ta kalli agogon bangon d'akin sai kuma taji kira alamun za'a tayar da sallah.
Zaune ta mik'e tana goge idanun ta ta jawo kujerar ta zauna a kai zuwa band'aki tayi alwala ta fito ta tayar da sallah. Bayan ta idar d'auko wayar ta ta shiga application na karatun alkur'ani ta fara karantawa a zuciya amma bakin ta na motsawa. Bata jima sosai tana yi ba ta fara azkhar kamar koda yaushe har ta kai k'arshe ta ajjiye ta fara lazumi a zuciyar ta.
Motsin sa taji a bayan ta ya k'araso inda take ya kalli a.c d'akin har lokacin tana aiki ga kuma sanyin d'akin yace, "bakya jin sanyi?." Kallon sa tayi kamar baza tayi magana ba sai ta tuna nasihar Umma tace, "Ina kwana."
"Ya jiki?" Abinda yace kawai kenan ya ajjiye ledar hannun sa tace, "Da sauk'i."
Baice komai ba itama haka ya fita ta bishi da kallon mamaki tana jin zuciyar ta na karyewa hawaye suka fara zubo mata bata hana kanta ba ta dinga kuka har ta koma ta kwanta tana kuka bata kuma duba ledar ba.
Shima ya jima sosai yana karatun da ya saba yayi azkhar har k'arfe bakwai na safe yana zaune ya tashi ya shiga d'aki ya kwanta. K'arfe tara ya farka yayi wanka ya saka doguwar riga irin ta larabawa ya fito zuwa falon a lokacin ake danna door bell ya bud'e k'ofar ya karb'i abinci daga restaurant d'in hotel d'in ya mayar da k'ofar ya kulle. A kan table ya ajjiye abincin ya k'arasa inda ya jona ruwan zafi ya d'auko butar ya k'araso ya zauna ya had'a tea yana sha a nutse ya bud'e wanda aka kawo yaga kayan maiko ne kwai, dankali, planten, sai sandwich.
Sandwich d'in ya d'auka guda d'aya yana ci bayan ya gama ya rufe sauran ya mik'e k'afa akan table d'in ya d'auki remote yana canja channel d'in TV. Ajjiyewa yayi ya d'auki wayar sa ya kira number Hydar dan yasan yana can yana neman sa, bai d'auka ba bai kuma kira ba sai ya kira layin mai martaba.
D'auka akayi hakan ya saka shi ya nutsu ya sauke k'afar sa k'asa a nutse yace, "Assslamu alaikum." Daga can b'angaren Mai martaba yace, "Wa'alaika salam, Zaki ya kwanan Misra?." Murmushi yayi kana yace, "Alhamdulillah, Barka da safiya Takawa."
"Barkan ka Asad, ya kuka tashi?."
"Alhamdulillah."
"Ka kira gidan su ka had'a su da ita dai ko?." Asad yayi shiru alamun baiyi ba Mai martaba jin yayi shiru sai yace, "Hakan bai kamata ba ai Asad duk inda suke yanzu hankalin su yana kanta suna so suji ya take, ka kira ka had'a su suyi magana."
"In sha Allah" ya furta a hankali kafin Asad yace, "Abba Mamaaaa ta dawo?." Mai martaba yayi murmushi yace, "Bata dawo ba Asad, koda ta dawo kar ka damu komai zai zo da sauk'i kaji." Kai ya d'aga kamar yana gaban sa kafin yace, "Kayi gaggawar kaita asibitin ayi mata aikin nan, ka duba ina tunanin yau ne date d'in aikin da akayi booking za'a mata, ka duba dai Hydar yayi booking a Saudi German." Nan ma kai ya d'aga kamar yana ganin sa kafin yace, "In sha Allah za'a yi abinda akace." Daga nan sallama suka yi ya yanke wayar daidai nan kiran Hydar ya shigo ya d'auka.
"Our groom, how was your first night? I hope you enjoy it" Hydar ya fad'a cikin tsokana. Tab'e baki Asad yayi ya murmusa kad'an Hydar yana bashi nishad'i ba kad'an b kana yace, "First night? With who?."
"Your wife mana."
"U are not serious Hydar." Dariya Hydar yayi kad'an yace, "Oga Deaf as mijin aure, wallahi ganin abun nake kamar wasa fa."
Bai bashi amsa ba yasan kuma daman bazai ce ba hakan ya saka ya kuma cewa, "U know what deaf? Kar ka bari kayi asarar wannan time d'in da kuka samu tare kayi k'okarin nuna mata kana sonta da gaske in ka lura zaka ga kamar gani take tilasta mata akayi ta aure ka, so Is better ka nuna mata kana sonta sosai sonta ya saka ka auro ta ba wani abun ba, ka gane ai abinda nake nufi ina nufin dai ayi komai."
Baice komai ba Hydar yace, "Yeah kayi k'ok'ari before Mama ta gano komai ta dawo da kai gida." Gaban sa ya fad'i matuk'a ya sauke numfashi yace, "lemme call her, excuse me" ya fad'a yana niyar kashe wayar yaji Hydar yace, "Amma dai bada number nan zaka kira ta ba ko?." Asad yayi shiru bai magana ba Hydar ya kuma cewa, "Naga number Egypt kasan kuma bata san baka nan ba so gwara ka kira ta da layin ka in ba haka ba zata gane baka nan, daman jiya mun had'u dasu Mum sun ga wucewar ka."
"Ohhh god! Hydar I lost my phone" ya fad'a yana dafe kansa. Hydar yace, "nayu mamaki dana ga number outside country dan nasan baka canja number kai da taka kake using a ko wacce k'asa, to yanzu ya za'ayi kenan gashi babu damar yin swap online dole sai kazo Nigeria, ga Mama indai ka kira ta da wannan number zatayi saurin d'agowa baka nan kuma kasan baka fad'a mata ba."
Asad ya kasa cewa komai duk tsoro ya cika masa zuciya sam baya son abinda Mama zatayi fushi dashi gashi bazai iya jurewa har ya koma bai mata waya ba, beside bai san lokacin da zai koma Nigeria ba tunda ko aikin ma ba'a yi mata ba, laifi goma da shirin kenan ga laifin ya tawo babu izinin ta, ga laifin auren da yayi bata so, ga laifi rashin kiran ta waya sabida rashin layin sa bazai iya ba sam. Hydar ya katse masa tunani yace, "Ya za'ayi kenan Deaf?." Asad ya sauke numfashi kana yace, "bazan iya d'aukar wannan lokacin without nayi magana da Mama ba Hydar, I can't" ya fad'a a raunane kamar zaiyi kuka.
Hydar yace, "Yaushe za'a yi mata aikin da akayi booking? Ina jin yau ne in akayi mata aikin kaga zata jima a kwance sai ka siyi ticket kazo kayi swapping ka koma a gani na hakan zai fi." Asad baice komai ba ya yanke kiran dan bai san me zaice masa ba.
Shiru yayi yana kallon wani wajan daban dan Allah ya sani bazai iya jure har gobe ko jibi ba sannan yayi magana da Mama bazai iya jurewa ba sam. Motsin k'ofa yaji hakan ya saka ya juyo ya kalli inda yaji motsin ya ganta zaune a kan kujerar ta sanye da doguwar riga ta saka hula tayi kyau sosai kwana d'aya tal fuskar ta ta washe har annuri yake fitarwa, Kasa d'auke ido yayi daga kallon ta tana tawowa a kan keken wayar ta a cinyar da alama bata kula dashi bama.
Idon ta takai inda yake suka had'a ido sai gabanta ya fad'i ta d'auke ido gashi tazo kusa dashi ya bita da kallo ji yake kamar ya jawo ta jikin sa gabad'aya ko zai samu sassaucin abinda yake a ji a zuciyar sa, kallon sa take shima yana kallon ta kafin ya fara janye idanun sa daga kanta ya mayar kan TV. Itama bata ce komai tayi shiru bata motsa ba taji maganar sa yace, "your breakfast." Bata motsa ba taji kuma me yace shi kuma yasan taji shiyasa ya share ta.
Wayar sa ya d'auka ya kira number Baba aka d'auka suka gaisa ya mik'a mata wayar alamun ta karb'a, karb'a tayi ta saka a kunne jin muryar mahaifinta sai ta saki fara'a suka gaisa ta saka aka kaiwa Umma suka gaisa farin ciki ya cika zuciyar ta sun jima suna magana da Umma har ta fara kuka kafin ta kashe wayar bata bashi ba ta rik'e a hannun ta tana kuka sosai.