Sashe 11
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta kalle shi tace, "Hydar wa nake gani kamar Asad?." Hydar yaja fasali kana yace, "shine." Jidda tace, "Ina waje? Kuma kamar shida wata nake gani wacce ita?." Hydar ya k'are mata kallo kana ya tab'e bakin sa yace, "ki tambaye shi" yana fad'ar hakan ya fita daga wajan ya barsu da tunanin wacece da kuma inda Asad zaije bayan Mama ta sanar dasu shine zai zo ya d'auke su.
Ina yaje? Shida wace suka gani sun tafi....?. Babu mai basu amsa dole Mum tayi k'wafa suka fito suka tafi.
Asad kuwa suna wucewa basu tsaya ba daman jirgin su yana k'asa motar da zata kai su ga inda jirgin yake suka suka ba jimawa sai gasu a inda jirgin yake, fitowa yayi ya fito da ita daman jakar su an auna ta sai sun je waccan garin zasu d'auke ta suna tafiya a hankali har suka isa steps na jirgin, kallon ta yayi yaga kamar a tsorace take sai ya rik'e hannun ta guda ya matsa ta d'ago ta kalle shi ba tare da yayi magana ba ya girgiza mata kai kawai ya saki hannu ganin mara lafiya ce kujerar ta baza ta hau ta steps ba sai aka nufi d'aya k'ofar da ita ta hau kai har cikin jirgi.
Rauda duk ta rud'e ta gigice a tsorace take matuk'a ji take kamar ta saki fitsarin wando sabida tsoro, yana zaune kusa da ita yana kallon yanayin fuskar ta sai yayi murmushi haka kawai yake jin nishad'i ya rik'e hannun ta guda d'aya kamar d'azu itama sai tak'i kallon sa taushin hannun sa na ratsa ta amma ta jure bata kalle shi ba har aka sanar da tashin jirgi.
Ihuuu da jirgi ya fara alamun tashi yaga ta runtse ido ta kwace hannun ta toshe kunnen ta da sauri ya d'auki abinda aka tanada dan toshe kunne ya saka mata sai taji bata jin k'arar sosai ta kalle shi taga ba ita yake kallo ba a lokacin jirgi ya fara gudu a k'asa kafin ya d'aga ya lula sararin samaniya.
Tashin da yayi tayi gefe ta fad'a kafad'ar sa ya rik'e ta a haka bai sake ta ba har sai da ya tabbatar sunyi nisa a sama sannan ya cika ta ta koma ta zauna tana raba idanu tana kuma hawaye har lokaci.
A bangaren su Mum ko ta kan Hydar basu bi ba drop d'in mota suka d'auka zuwa katagum jikin Mum har rawa yake burin ta ta isa gida ta kira Mama taji ina Asad ya tafi sannan shida wa suka tafi. Tun a compound na gidan take mata waya bata d'auka ba har ta hau saman gidan ta sai a sannan Mama ta d'auka tana fad'in, "Sadiya kin san ina cikin jama'a." Mum tace, "abu ne na gaggawa Fulani shiyasa na dame ki da waya, ina Asad ya tafi na ganshi a airport a b'angaren international alamun k'asar zai bari? Sannan wacece wacce na gansu tare da ita?."
Mama tace, "What! Asad da wata kuma sun bar k'asar nan? Anya kuwa shine?."
"Shine mana bayan Hydar na gani shine ya kawo shi Airport d'in ma kuma na ganshi shima ya ganni."
"Sadiya relax babu inda Asad zaije ba tare da ya fad'a min ba, sannan kuma wacece zaiyi tafiya da ita?, sai dai in Aliyu kuka gani amma ba Asad ba."
Mum tayi shiru tana girgiza kanta cikin amincewa da maganar Mama tabbas Aliyu ta gani da wata budurwar tasa ba Asad ba Hydar ya raina mata hankali ne kawai, ajiyar zuciya tayi tace, "Haka ne fa kuma Fulani; duk na tsorata ne wallahi kar naje ko Asad d'in ne har wad'an can talakawan sun fara canja masa tunani yana yin abu baki sani ba."
Mama tayi dariya tace, "K'arya su tasha k'arya, ai nafi k'arfin su wallahi tunda na yanke alaqar nan dake tsakanin su ta riga ta yanku, tunda nace a bari nasan an bari, tunda nace bana so nasan shima yanzu baya so. Ta ko wanne b'angare na mamaye ko ina ko kara na ajiiye Asad bai isa ya tsallaka ba sai na bada umarnin hakan, zancen waccan y'ar talakawan ai ki d'auka ya zama tsohon labari."
Mum tace, "An gama ranki ya dad'e, mayi magana anjima ki huta lafiya" ta fad'a tana yanke wayar ta bita da kallo a bayyane tace, "Saura lokaci kad'an ya dawo a bayan hannun ki ba tafin hannun ki ba, in na fara sarrafa Asad baki isa ya saurare ki ba daga ni sai Jidda kawai zai dinga gani. Hmmmmm Rabi'atu kenan sai kin yabawa aya zak'in ta zumud'in zama uwar sarki zai bar zuciyar ki domin a zahiri zaki zama uwar sarki a bad'ini kuma nice uwar sarkin domin komai sai abinda nace za'ayi, zan nuna miki a wannan fannin na dame ki na shanye wallahi sai Jidda ta zamar miki ciwon ido a cikin gidan nan. ki kiyayi had'uwar mu" ta fad'a da murmushi tana kallon wayar ta kamar da Maman take magana.....
*Nikam nace kun makara*🏃🏼♀️😂
[17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*032.*
*Four Seasons hotel Cairo.*
D'aya daga cikin manyan hotels d'in da ake ji dasu kenan dake cikin birnin Cairo wato babban birinin dake cikin k'asar Egypt kenan suka sauka, duk da kasancewar dare yayi amma haske tarrr ko ina kamar rana fitulu sun haske ko ina baza kace dare bane sai ka kalli sararin samaniya. Babban falo ne guda d'aya mai d'auke da d'aki guda biyu manya babu abinda babu a cikin su girman su kuwa ba'a cewa komai.
Tunda suka shiga falon take wara ido take kallon falon dan bata tab'a ganin irin sa ba a rayuwar ta gabad'aya shiyasa take kalla kodan ta kashe kwarkwatar idanun ta, yayi kyau komai na cikin blue hatta carpet da komai na cikin sa blue ne. Asad zama yayi a gefen kujerar dake d'aya daga cikin kujerun wajan ya shafa aljihun sa yana neman wayar sa amma yaji babu ita, ya mik'e tsaye yana duba jikin amma babu wayar sa a jikin sa.
Dafe kansa yayi ya kalli Rauda da take k'arewa falon kallo har lokacin yaga wayar ta akan cinyar ta ba tare da yace komai ba ya d'auki wayar sai a lokacin ta kalle shi amma ba ita yake kallo ba ya danna number sa ya kira, a kashe yake jin sim card d'in nasa yaja k'aramin tsaki ya ajjiye wayar tata ya kama k'ugu ya rik'e yana kallon wani wajan daban dan yasan ya yar da wayar a wani wajan. Juyowa yayi ya kalle ta suka had'a ido ta d'auke kanta baice komai ba yaja jakar ta zuwa d'aki guda d'aya ya ajjiye yana fitowa ya nuna mata d'akin da hannu baice komai ba ya fita da sauri.
Da kallo ta bishi ta sauke ajiyar tace, "Allah gani gare ka, ka kawo min d'auki da gaggawa" ta fad'a tana danna inda ya danna d'azu kujerar ta fara tafiya da yake ba tudu har tazo k'ofar d'akin, tsayawa tayi tana kallon kanta a k'aton mudubin da yake dogo tayi murmushi a bayyane tace, "Rauda a Cairo." shiga d'akin tayi lafiya wani abun bai tokare ta ba.
"kan bala'i" ta furta ganin d'akin har yafi falon ma kyau ta bishi da kallo babu abinda ya d'auki hankalin ta sai wata taga ta glass doguwa wacce kake hango titi motoci suna ta wucewa ko kana zaune basai ka tashi ba. Kallon d'akin take tana tafiya a hankali har ta isa wata k'ofa da take tunanin band'aki ce ta bud'e girman sa dakyaun band'akin ta shagala da kallo kafin ta samu damar cire kayan jikin ta tayi wanka.
Tana iya tsayawa da k'afa d'aya hakan ya saka a tsaye tayi wankan da k'afa guda d'aya sai dq ta gama taga towels da yawa a ma'ajiyar su sai khamshi suke yi ta d'auki d'aya ta d'aura tana fad'in, "Wai nima irin y'ar gayun nan, ikon Allah kenan Rauda ce yau a wata k'asar daba Nigeria ba."
Zama tayi akan kujerar tata ta fito ta koma bakin gado ta sauka akan kujerar ta zauna gefen gado ta bud'e jakar ta tana dubawa, dogayen riguna masu mayafi da riga da wando shi Yaya Ummi ta zuba mata a ciki sai na bacci doguwa guda biyu sai k'ananu sauran, ta d'auki doguwar ta saka ta saka turare mai khamshi ta hau kam kujerar tana kallon d'akin da tunanin ko ina ne alqibla, wata takarda ta gani da take nuna gabas ta juya kujerar ta tayar da sallar magariba da i'sha.
K'asaru tayi bayan ta idar taji bacci na k'okarin kama ta ga kuma yunwar da take ji a cikin ta, agogo ta kalla na d'akin taga k'arfe d'aya na dare tayi hamma ta koma kan gadon ta zauna sanyin a.c na rantsa ta amma rashin sabo da tsoro ya hana ta kwanciya. Wayar ta da take gefe ta gani ta d'auka tana duba number da ya kira d'azu ta danna number sai taga tayi kama da number da aka tab'a kiran ta ga kiran nan ma yana nan da adadin lokacin da aka d'auka ana wayar hakan ya tabbatar mata itace, ajjiye wayar tayi tace, "Kenan daman shine ya kira ni?."
K'arar bud'e k'ofa ya saka ta kalli wanda ya shigo ta ganshi ya canja kaya zuwa k'ananu riga da wando marasa nauyi hannun sa rik'e da ledar abinci ya ajjiye mata a gefen ta ba tare da yayi magana ba ya juya zai fita tace, "Baka ji ba." Cak ya tsaya kafin ya juyo ya kalle ta ya d'aga gira alamun yana jinta tace, "Zan iya kiran Ummana yanzu?." Kai ya girgiza alamun a'a da hannu yayi mata alamun ta bari sai da safe daga haka ya fita baice komai ba.
Tsaki taja tace, "Aikin banza shi a lallai ga d'an sarki, koma me kayi min dai Allah sai ya saka min" ta fad'a tana jawo ledar ta bud'e tayi karo da lafiyayyar shinkafa da kaza sai khamshi take zubawa ga ruwa da lemo a ciki ba shiri ta baje a kan gadon taci ta k'oshi tasha ruwa. Ta d'an jima a zaune kafin ta kwashe kayan ta zame ta kwanta cikin lokaci kad'an bacci ya d'auke ta.
Ina yaje? Shida wace suka gani sun tafi....?. Babu mai basu amsa dole Mum tayi k'wafa suka fito suka tafi.
Asad kuwa suna wucewa basu tsaya ba daman jirgin su yana k'asa motar da zata kai su ga inda jirgin yake suka suka ba jimawa sai gasu a inda jirgin yake, fitowa yayi ya fito da ita daman jakar su an auna ta sai sun je waccan garin zasu d'auke ta suna tafiya a hankali har suka isa steps na jirgin, kallon ta yayi yaga kamar a tsorace take sai ya rik'e hannun ta guda ya matsa ta d'ago ta kalle shi ba tare da yayi magana ba ya girgiza mata kai kawai ya saki hannu ganin mara lafiya ce kujerar ta baza ta hau ta steps ba sai aka nufi d'aya k'ofar da ita ta hau kai har cikin jirgi.
Rauda duk ta rud'e ta gigice a tsorace take matuk'a ji take kamar ta saki fitsarin wando sabida tsoro, yana zaune kusa da ita yana kallon yanayin fuskar ta sai yayi murmushi haka kawai yake jin nishad'i ya rik'e hannun ta guda d'aya kamar d'azu itama sai tak'i kallon sa taushin hannun sa na ratsa ta amma ta jure bata kalle shi ba har aka sanar da tashin jirgi.
Ihuuu da jirgi ya fara alamun tashi yaga ta runtse ido ta kwace hannun ta toshe kunnen ta da sauri ya d'auki abinda aka tanada dan toshe kunne ya saka mata sai taji bata jin k'arar sosai ta kalle shi taga ba ita yake kallo ba a lokacin jirgi ya fara gudu a k'asa kafin ya d'aga ya lula sararin samaniya.
Tashin da yayi tayi gefe ta fad'a kafad'ar sa ya rik'e ta a haka bai sake ta ba har sai da ya tabbatar sunyi nisa a sama sannan ya cika ta ta koma ta zauna tana raba idanu tana kuma hawaye har lokaci.
A bangaren su Mum ko ta kan Hydar basu bi ba drop d'in mota suka d'auka zuwa katagum jikin Mum har rawa yake burin ta ta isa gida ta kira Mama taji ina Asad ya tafi sannan shida wa suka tafi. Tun a compound na gidan take mata waya bata d'auka ba har ta hau saman gidan ta sai a sannan Mama ta d'auka tana fad'in, "Sadiya kin san ina cikin jama'a." Mum tace, "abu ne na gaggawa Fulani shiyasa na dame ki da waya, ina Asad ya tafi na ganshi a airport a b'angaren international alamun k'asar zai bari? Sannan wacece wacce na gansu tare da ita?."
Mama tace, "What! Asad da wata kuma sun bar k'asar nan? Anya kuwa shine?."
"Shine mana bayan Hydar na gani shine ya kawo shi Airport d'in ma kuma na ganshi shima ya ganni."
"Sadiya relax babu inda Asad zaije ba tare da ya fad'a min ba, sannan kuma wacece zaiyi tafiya da ita?, sai dai in Aliyu kuka gani amma ba Asad ba."
Mum tayi shiru tana girgiza kanta cikin amincewa da maganar Mama tabbas Aliyu ta gani da wata budurwar tasa ba Asad ba Hydar ya raina mata hankali ne kawai, ajiyar zuciya tayi tace, "Haka ne fa kuma Fulani; duk na tsorata ne wallahi kar naje ko Asad d'in ne har wad'an can talakawan sun fara canja masa tunani yana yin abu baki sani ba."
Mama tayi dariya tace, "K'arya su tasha k'arya, ai nafi k'arfin su wallahi tunda na yanke alaqar nan dake tsakanin su ta riga ta yanku, tunda nace a bari nasan an bari, tunda nace bana so nasan shima yanzu baya so. Ta ko wanne b'angare na mamaye ko ina ko kara na ajiiye Asad bai isa ya tsallaka ba sai na bada umarnin hakan, zancen waccan y'ar talakawan ai ki d'auka ya zama tsohon labari."
Mum tace, "An gama ranki ya dad'e, mayi magana anjima ki huta lafiya" ta fad'a tana yanke wayar ta bita da kallo a bayyane tace, "Saura lokaci kad'an ya dawo a bayan hannun ki ba tafin hannun ki ba, in na fara sarrafa Asad baki isa ya saurare ki ba daga ni sai Jidda kawai zai dinga gani. Hmmmmm Rabi'atu kenan sai kin yabawa aya zak'in ta zumud'in zama uwar sarki zai bar zuciyar ki domin a zahiri zaki zama uwar sarki a bad'ini kuma nice uwar sarkin domin komai sai abinda nace za'ayi, zan nuna miki a wannan fannin na dame ki na shanye wallahi sai Jidda ta zamar miki ciwon ido a cikin gidan nan. ki kiyayi had'uwar mu" ta fad'a da murmushi tana kallon wayar ta kamar da Maman take magana.....
*Nikam nace kun makara*🏃🏼♀️😂
[17/12, 10:39 pm] Nafisat Alwasa: Arewabooks@nanahaleema11
*032.*
*Four Seasons hotel Cairo.*
D'aya daga cikin manyan hotels d'in da ake ji dasu kenan dake cikin birnin Cairo wato babban birinin dake cikin k'asar Egypt kenan suka sauka, duk da kasancewar dare yayi amma haske tarrr ko ina kamar rana fitulu sun haske ko ina baza kace dare bane sai ka kalli sararin samaniya. Babban falo ne guda d'aya mai d'auke da d'aki guda biyu manya babu abinda babu a cikin su girman su kuwa ba'a cewa komai.
Tunda suka shiga falon take wara ido take kallon falon dan bata tab'a ganin irin sa ba a rayuwar ta gabad'aya shiyasa take kalla kodan ta kashe kwarkwatar idanun ta, yayi kyau komai na cikin blue hatta carpet da komai na cikin sa blue ne. Asad zama yayi a gefen kujerar dake d'aya daga cikin kujerun wajan ya shafa aljihun sa yana neman wayar sa amma yaji babu ita, ya mik'e tsaye yana duba jikin amma babu wayar sa a jikin sa.
Dafe kansa yayi ya kalli Rauda da take k'arewa falon kallo har lokacin yaga wayar ta akan cinyar ta ba tare da yace komai ba ya d'auki wayar sai a lokacin ta kalle shi amma ba ita yake kallo ba ya danna number sa ya kira, a kashe yake jin sim card d'in nasa yaja k'aramin tsaki ya ajjiye wayar tata ya kama k'ugu ya rik'e yana kallon wani wajan daban dan yasan ya yar da wayar a wani wajan. Juyowa yayi ya kalle ta suka had'a ido ta d'auke kanta baice komai ba yaja jakar ta zuwa d'aki guda d'aya ya ajjiye yana fitowa ya nuna mata d'akin da hannu baice komai ba ya fita da sauri.
Da kallo ta bishi ta sauke ajiyar tace, "Allah gani gare ka, ka kawo min d'auki da gaggawa" ta fad'a tana danna inda ya danna d'azu kujerar ta fara tafiya da yake ba tudu har tazo k'ofar d'akin, tsayawa tayi tana kallon kanta a k'aton mudubin da yake dogo tayi murmushi a bayyane tace, "Rauda a Cairo." shiga d'akin tayi lafiya wani abun bai tokare ta ba.
"kan bala'i" ta furta ganin d'akin har yafi falon ma kyau ta bishi da kallo babu abinda ya d'auki hankalin ta sai wata taga ta glass doguwa wacce kake hango titi motoci suna ta wucewa ko kana zaune basai ka tashi ba. Kallon d'akin take tana tafiya a hankali har ta isa wata k'ofa da take tunanin band'aki ce ta bud'e girman sa dakyaun band'akin ta shagala da kallo kafin ta samu damar cire kayan jikin ta tayi wanka.
Tana iya tsayawa da k'afa d'aya hakan ya saka a tsaye tayi wankan da k'afa guda d'aya sai dq ta gama taga towels da yawa a ma'ajiyar su sai khamshi suke yi ta d'auki d'aya ta d'aura tana fad'in, "Wai nima irin y'ar gayun nan, ikon Allah kenan Rauda ce yau a wata k'asar daba Nigeria ba."
Zama tayi akan kujerar tata ta fito ta koma bakin gado ta sauka akan kujerar ta zauna gefen gado ta bud'e jakar ta tana dubawa, dogayen riguna masu mayafi da riga da wando shi Yaya Ummi ta zuba mata a ciki sai na bacci doguwa guda biyu sai k'ananu sauran, ta d'auki doguwar ta saka ta saka turare mai khamshi ta hau kam kujerar tana kallon d'akin da tunanin ko ina ne alqibla, wata takarda ta gani da take nuna gabas ta juya kujerar ta tayar da sallar magariba da i'sha.
K'asaru tayi bayan ta idar taji bacci na k'okarin kama ta ga kuma yunwar da take ji a cikin ta, agogo ta kalla na d'akin taga k'arfe d'aya na dare tayi hamma ta koma kan gadon ta zauna sanyin a.c na rantsa ta amma rashin sabo da tsoro ya hana ta kwanciya. Wayar ta da take gefe ta gani ta d'auka tana duba number da ya kira d'azu ta danna number sai taga tayi kama da number da aka tab'a kiran ta ga kiran nan ma yana nan da adadin lokacin da aka d'auka ana wayar hakan ya tabbatar mata itace, ajjiye wayar tayi tace, "Kenan daman shine ya kira ni?."
K'arar bud'e k'ofa ya saka ta kalli wanda ya shigo ta ganshi ya canja kaya zuwa k'ananu riga da wando marasa nauyi hannun sa rik'e da ledar abinci ya ajjiye mata a gefen ta ba tare da yayi magana ba ya juya zai fita tace, "Baka ji ba." Cak ya tsaya kafin ya juyo ya kalle ta ya d'aga gira alamun yana jinta tace, "Zan iya kiran Ummana yanzu?." Kai ya girgiza alamun a'a da hannu yayi mata alamun ta bari sai da safe daga haka ya fita baice komai ba.
Tsaki taja tace, "Aikin banza shi a lallai ga d'an sarki, koma me kayi min dai Allah sai ya saka min" ta fad'a tana jawo ledar ta bud'e tayi karo da lafiyayyar shinkafa da kaza sai khamshi take zubawa ga ruwa da lemo a ciki ba shiri ta baje a kan gadon taci ta k'oshi tasha ruwa. Ta d'an jima a zaune kafin ta kwashe kayan ta zame ta kwanta cikin lokaci kad'an bacci ya d'auke ta.