Sashe 14
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kawai sai yaji bai gamsu ba ya kalli Dr Asif yace, "Zan bi bayan su" yana fad'a ya mik'e Dr Asif d'in ma ya biyo shi suka fito suka bi bayan su. D'aki aka shiga da ita babba mai d'auke da injina da na'uroro kala-kala suka kunna wata na'ura suka k'araso kusa da Rauda ita duk tsoro take ji ganin injinan harrrrr a idanun ta sai taji ta tsorata. Kan gado suka nuna mata alamun ta kwanta sai taji bazata iya ba sabida tsoron da take ciki ganin hakan ya k'araso kusa da ita ya kalli fuskar ta da take a kwab'e kamar zatayi kuka yace, "Relax."
Ya furta a hankali yana rik'o hannun ta ya jingina ta da jikin sa ta runtse idanun ta suka matso da gadon ya kwantar da ita ta rik'e hannun sa gam idanun ta a rufe, k'arar na'urar taji kusa da ita taji an tattare rigar jikin ta an saka na'urar a k'afar ta nan take kasusuwan k'afar ta suka bayyana a jikin wani babban screen dake gaban gadon.
Dr Asif yana kalla suna juya na'urar tana nuno ko ina na k'afar ra har inda matsalar take nan take ya gani ya bada umarnin a cire ta daga ciki har lokacin hannun ta na rik'e dana Asad, kashewa sukayi Dr Asif ya kalle ta yayi murmushi cikin larabci yake ce masa, "Tana da tsoro, amma tana da kyau irin na y'an Nigeria." Asad bai amsa ba ya share shi ya kuma cewa, "y'ar uwar kace? Kuma bakwa kama." Nan ma ya share shi baiyi magana ba ganin hakan sai Asif yaja bakin sa yayi shiru.
Dr Asif ya kuma cewa, "In kun shirya za'a yi mata aikin yanzu ba wani mai wahala bane." Asad ya kalli Rauda da take kwance har lokacin ya sunkuya da kansa daidai kunnen ta yace, "za'a yi aikin yanzu, kar kiji tsoro" abinda yace kenan ya d'ago ya kalli Dr Asif ya d'aga masa kai alamun ayi kawai.
Dr Asif ya kalli nurses d'in ya fad'a musu ayi shirin aiki shima ya fita, uniform suka ajjiyewa Rauda da hula da talamin da duk wanda zai kwanta asibitin yake amfani dashi suka fita suka bata waje dan ta shirya. Jin babu motsi sai ta bud'e idon ta ta kalle shi taga ita yake kallo yayi mata nunu da kayan da ido ta tashi zaune ya saki hannun ta ya fita.
Sun jima basu dawo ba lokacin da suka dawo ta cire kayan ta saka wanda suka bata aka ja gadon zuwa d'akin tiyata yana bin su a baya har cikin d'akin, kallon sa da yaga tana yi sai ya k'arasa kusa da ita ya rik'e hannun ta gam yace, "Kar kiji tsoro." sai ta kulle idon ta akayi mata allura daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba.
Cikin lokaci kad'an aka kammala aikin aka fito da ita zuwa d'akin da zata huta har lokacin bacci take a lokacin agogon Cairo karfe hud'u na yamma. Sai da yaga an fito da ita ta kwanta sannan ya samu damar yiwa mahaifinta message ya tura domin bazai iya doguwar magana ba ya fita zuwa masallaci yayi sallah.
Bata san adadin lokacin da ta d'auka a kwance ba ita dai taga ta bud'e idanun tane ta ganta a kwance a kan gado haske ko ga ina kuma babu kowa a d'akin sai k'arar a.c kad'an da yake tashi a ciki. "Sannu Rauda" aka fad'a daga gefen ta ana murmushi ana kallon ta. Gaban Rauda ya fad'i idanun ta suka had'u dana wanda yake mata magana ta ganshi fari tas dashi kana ganin sa kaga balarabe amma taji yana yi mata hausa duk sai ta gigice tana jan ayatul kursiyu a zuciyar ta.
A yanayin fuskar ta ya hango tsoro a ciki sai yayi murmushi yace, "Karki tsorata suna na Dr Khalifa ni bahaushe ne kamar ki." Duk da ta d'an ji dad'i amma bata nuna ba dan ba amincewa tayi da abinda yace ba kawai ita kallon aljani take masa. Murmushi yayi yace, "in kika ji tsoro kina kyau." Asad ta hango ya shigo yana amsa waya ya canja kaya zuwa riga da wando jajaye nasu kauri da tsaho dan rigar irin mai high neck ce kana ganin su kaga kayan sanyi.
Dr Khalifa ya kalli Asad yace, "Asad da alama wannan sister naka kallon aljani take min dan taji ina hausa" ya fad'a yana murmushi ya k'arasa inda drip stand yake ruwan da yake shiga jikin ta ya tsayar dashi kana yace, "But tana dakyau." Asad baice komai ba ya k'arasa kusa da ita yana kallon k'afar da take cikin wani abu kamar akwati an d'aure ta da farin bandage a mike sanb'al.
"Kina jin ciwo a k'afar taki?" Dr ya fad'a yana kallon ta.
Kai ta girgiza kafin tace, "Akwai ciwon amma ba sosai ba."
"Zai daina shima nan da anjima kad'an zaki daina jin komai." Kai ta d'aga kawai ya juya ya kalli Asad kafin yayi magana aka bud'e k'ofar aka shigo. Kyakykyawar matashiyar budurwa ce d'auke da rigar likitoci ta yafa karamin mayafi a kanta tayi kyau sosai duk da kana kallon ta kasan ba balarabiya bace amma ta had'a jini dasu.
Asad ta kalla cikin mamaki tace, "dana ganka d'azu ban d'auka kaine ba shine nazo da kaina. Ohh Aliyu da gaske kaine?." Kallon ta yake yana so ya tuna inda ya santa amma ya kasa yadai san ya Santa a wani wajan ganin hakan sai ta kama k'ugu tace, "You forgot me right?." Nan ma bai amsa ba sai kallon ta da yake yi tace, "You forgot your school friend Muheeba?." Shiru ya kuma yi alamun yaso dai ya gane ganin hakan sai ta hard'e hannu a k'irji tana kallon sa da wani irin murmushi a fuskar ta kafin tace, "Muheebba!" Ta maimaita a hankali.
Wara ido yayi sai kuma ya tab'e baki tunawa da ya san fuskar ta a wajan Aliyu lokacin da suna makaranta yace, "bani bane." Muhibba tace, "Lallai prince." Khalifa da yake jin su yace, "Dr wa kike nema ne ke?." Tace, "shine fa Prince Aliyu bin Nasir." Khalifa yayi murmushi yace, "Bashi bane wannan triples d'in Aliyu ne Asad."
Wara idanu tayi cikin mamaki tace, "like seriously?."
"Sure."
Dawo da kallon ta tayi ga Asad tana binsa da kallo cikin mamaki da al'ajabi tace, "I see, kasan sai yanzu na gane Khalifa? Cos inda Aliyu ne da yanzu ya bani welcome hug, Wow Allah mai iko babu inda ya bar Aliyu."
Khalifa bai bata amsa ba ta mik'a masa hannu tace, "nice to meet u prince Asad." Kallon hannun nata yayi sannan ya kalle ta sai ya d'auke kai a iya lab'ban sa ya amsa da, "Thanks" yana fad'ar hakan yayo gaban wajan gadon da take kwance ba tare da ya sake kallon ta ba dan Allah ya sani ya tsani mace mara kamun kai da nuna zaqewa a kan namiji da sunan wayewa.
Muhibba kam kallon sa take da mamaki bata tab'a ganin kama irin ta Aliyu da Asad ba duk da Aliyu ya fishi kamar faran-faran musamman ga mata dan da shine yadda suka had'u d'in nan sai yayi hugging d'in ta amma babu ta inda ya barshi.
Murmushi tayi domin ya burge ta sosai ajin sa ya burge ta matuk'a musamman lokacin da take masa magana yake d'aga girar sa sama yana kallon ta ya k'ayatar da ita har taji bata gaji da kallon sa ba. Khalifa ya kalle shi yace, "Deaf yana da kyau tayi sallah." Asad ya d'aga kansa ya kalle ta ya kalli agogon hannun sa lokacin asuba gab da take da yi amma bai ce komai ba.
Muhibba tace, "she's your sister?" Ta fad'a tana kallon Asad ya runtse ido ya bud'e alamun ta dame shi baya son yawan magana amma ta kasa ganewa kafin ya bata amsa Khalifa yace, "Yeah, sister shi ce."
"Woww! Amma basa kama, ya akayi kika bari yayan ki ya fiki kyau haka?. Kalle shi kamar arab in ya shiga cikin larabawan asibitin nan babu wanda zai gane shi" ta fad'a tana kallon sa da murmushi a fuskar ta.
Rauda bata kula ta ba dan haushi ta bata ta lura irin matan nan ne masu shigewa maza ta saci kallon sa taga shima ba ita yake kallo ba, kusa da Khalifa ta k'arasa tace, "Baya magana ne kamar Brother d'insa? Naji kana ce masa deaf kuma naji yayi magana sau d'aya."
"Baya son magana ko kad'an kinji wannan maganar da yayi miki babu lallai ya kuma yi miki wata har ki bar nan gwara ma kiyi shiru" ya fad'a mata a hankali a kunnen ta sai taji ya sake burge ta ta wara idanu tace, "Woww! He impressed me."
Kallon Asad tayi tace, "Lemme help my sister tayi sallah before asuba" ta fad'a tana k'arasowa inda Rauda take tana kallon sa har lokacin. Da hannu Asad ya dakatar da ita alamun ta barshi ya kalli Khalifa shima shi yake kallo kafin Khalifa yace, "Kana kallona kasan ba ko yaushe nake gane me kallon ka yake nufi ba, ka yi magana abeg." Baice komai ba sai ya bar wajan ya fita daga d'akin jim kad'an sai gashi yazo da nurses d'in da alhakin kula da ita yake a wuyan su suna shigowa shi kuma ya juya ya fita.
Dole suma suka fito dan su bar su suyi aikin su suka ganshi zaune akan kujera yana danna wayar sa a nutse bai damu da kowa ana wajan ba, yadda larabawa suke zirga-zirga sai ka d'auka shima balaraben ne hutawa yake yi sabida yadda ya dace da zama balaraben musamman shigar jikin sa da ta sake haska fatar sa. Muhibba ta k'arasa kusa dashi ta zauna a gefen sa tace, "Aliyu abokina ne a school yana ina yanzu? Ko zan iya samun number shi?." In kujerar da suke kai tayi magana tabbas shima yayi bai kalle ta ba wayar kawai yake dannawa.
Zata kuma magana kawai ya mik'e ya bar mata wajan ta bishi da kallo cikin tsantsar burgewa har ya b'acewa ganin ta tayi murmushi tace, "I like his acting" ta fad'a tana murmushi sosai dan ba k'aramin burge ta yayi ba.
Ya furta a hankali yana rik'o hannun ta ya jingina ta da jikin sa ta runtse idanun ta suka matso da gadon ya kwantar da ita ta rik'e hannun sa gam idanun ta a rufe, k'arar na'urar taji kusa da ita taji an tattare rigar jikin ta an saka na'urar a k'afar ta nan take kasusuwan k'afar ta suka bayyana a jikin wani babban screen dake gaban gadon.
Dr Asif yana kalla suna juya na'urar tana nuno ko ina na k'afar ra har inda matsalar take nan take ya gani ya bada umarnin a cire ta daga ciki har lokacin hannun ta na rik'e dana Asad, kashewa sukayi Dr Asif ya kalle ta yayi murmushi cikin larabci yake ce masa, "Tana da tsoro, amma tana da kyau irin na y'an Nigeria." Asad bai amsa ba ya share shi ya kuma cewa, "y'ar uwar kace? Kuma bakwa kama." Nan ma ya share shi baiyi magana ba ganin hakan sai Asif yaja bakin sa yayi shiru.
Dr Asif ya kuma cewa, "In kun shirya za'a yi mata aikin yanzu ba wani mai wahala bane." Asad ya kalli Rauda da take kwance har lokacin ya sunkuya da kansa daidai kunnen ta yace, "za'a yi aikin yanzu, kar kiji tsoro" abinda yace kenan ya d'ago ya kalli Dr Asif ya d'aga masa kai alamun ayi kawai.
Dr Asif ya kalli nurses d'in ya fad'a musu ayi shirin aiki shima ya fita, uniform suka ajjiyewa Rauda da hula da talamin da duk wanda zai kwanta asibitin yake amfani dashi suka fita suka bata waje dan ta shirya. Jin babu motsi sai ta bud'e idon ta ta kalle shi taga ita yake kallo yayi mata nunu da kayan da ido ta tashi zaune ya saki hannun ta ya fita.
Sun jima basu dawo ba lokacin da suka dawo ta cire kayan ta saka wanda suka bata aka ja gadon zuwa d'akin tiyata yana bin su a baya har cikin d'akin, kallon sa da yaga tana yi sai ya k'arasa kusa da ita ya rik'e hannun ta gam yace, "Kar kiji tsoro." sai ta kulle idon ta akayi mata allura daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba.
Cikin lokaci kad'an aka kammala aikin aka fito da ita zuwa d'akin da zata huta har lokacin bacci take a lokacin agogon Cairo karfe hud'u na yamma. Sai da yaga an fito da ita ta kwanta sannan ya samu damar yiwa mahaifinta message ya tura domin bazai iya doguwar magana ba ya fita zuwa masallaci yayi sallah.
Bata san adadin lokacin da ta d'auka a kwance ba ita dai taga ta bud'e idanun tane ta ganta a kwance a kan gado haske ko ga ina kuma babu kowa a d'akin sai k'arar a.c kad'an da yake tashi a ciki. "Sannu Rauda" aka fad'a daga gefen ta ana murmushi ana kallon ta. Gaban Rauda ya fad'i idanun ta suka had'u dana wanda yake mata magana ta ganshi fari tas dashi kana ganin sa kaga balarabe amma taji yana yi mata hausa duk sai ta gigice tana jan ayatul kursiyu a zuciyar ta.
A yanayin fuskar ta ya hango tsoro a ciki sai yayi murmushi yace, "Karki tsorata suna na Dr Khalifa ni bahaushe ne kamar ki." Duk da ta d'an ji dad'i amma bata nuna ba dan ba amincewa tayi da abinda yace ba kawai ita kallon aljani take masa. Murmushi yayi yace, "in kika ji tsoro kina kyau." Asad ta hango ya shigo yana amsa waya ya canja kaya zuwa riga da wando jajaye nasu kauri da tsaho dan rigar irin mai high neck ce kana ganin su kaga kayan sanyi.
Dr Khalifa ya kalli Asad yace, "Asad da alama wannan sister naka kallon aljani take min dan taji ina hausa" ya fad'a yana murmushi ya k'arasa inda drip stand yake ruwan da yake shiga jikin ta ya tsayar dashi kana yace, "But tana dakyau." Asad baice komai ba ya k'arasa kusa da ita yana kallon k'afar da take cikin wani abu kamar akwati an d'aure ta da farin bandage a mike sanb'al.
"Kina jin ciwo a k'afar taki?" Dr ya fad'a yana kallon ta.
Kai ta girgiza kafin tace, "Akwai ciwon amma ba sosai ba."
"Zai daina shima nan da anjima kad'an zaki daina jin komai." Kai ta d'aga kawai ya juya ya kalli Asad kafin yayi magana aka bud'e k'ofar aka shigo. Kyakykyawar matashiyar budurwa ce d'auke da rigar likitoci ta yafa karamin mayafi a kanta tayi kyau sosai duk da kana kallon ta kasan ba balarabiya bace amma ta had'a jini dasu.
Asad ta kalla cikin mamaki tace, "dana ganka d'azu ban d'auka kaine ba shine nazo da kaina. Ohh Aliyu da gaske kaine?." Kallon ta yake yana so ya tuna inda ya santa amma ya kasa yadai san ya Santa a wani wajan ganin hakan sai ta kama k'ugu tace, "You forgot me right?." Nan ma bai amsa ba sai kallon ta da yake yi tace, "You forgot your school friend Muheeba?." Shiru ya kuma yi alamun yaso dai ya gane ganin hakan sai ta hard'e hannu a k'irji tana kallon sa da wani irin murmushi a fuskar ta kafin tace, "Muheebba!" Ta maimaita a hankali.
Wara ido yayi sai kuma ya tab'e baki tunawa da ya san fuskar ta a wajan Aliyu lokacin da suna makaranta yace, "bani bane." Muhibba tace, "Lallai prince." Khalifa da yake jin su yace, "Dr wa kike nema ne ke?." Tace, "shine fa Prince Aliyu bin Nasir." Khalifa yayi murmushi yace, "Bashi bane wannan triples d'in Aliyu ne Asad."
Wara idanu tayi cikin mamaki tace, "like seriously?."
"Sure."
Dawo da kallon ta tayi ga Asad tana binsa da kallo cikin mamaki da al'ajabi tace, "I see, kasan sai yanzu na gane Khalifa? Cos inda Aliyu ne da yanzu ya bani welcome hug, Wow Allah mai iko babu inda ya bar Aliyu."
Khalifa bai bata amsa ba ta mik'a masa hannu tace, "nice to meet u prince Asad." Kallon hannun nata yayi sannan ya kalle ta sai ya d'auke kai a iya lab'ban sa ya amsa da, "Thanks" yana fad'ar hakan yayo gaban wajan gadon da take kwance ba tare da ya sake kallon ta ba dan Allah ya sani ya tsani mace mara kamun kai da nuna zaqewa a kan namiji da sunan wayewa.
Muhibba kam kallon sa take da mamaki bata tab'a ganin kama irin ta Aliyu da Asad ba duk da Aliyu ya fishi kamar faran-faran musamman ga mata dan da shine yadda suka had'u d'in nan sai yayi hugging d'in ta amma babu ta inda ya barshi.
Murmushi tayi domin ya burge ta sosai ajin sa ya burge ta matuk'a musamman lokacin da take masa magana yake d'aga girar sa sama yana kallon ta ya k'ayatar da ita har taji bata gaji da kallon sa ba. Khalifa ya kalle shi yace, "Deaf yana da kyau tayi sallah." Asad ya d'aga kansa ya kalle ta ya kalli agogon hannun sa lokacin asuba gab da take da yi amma bai ce komai ba.
Muhibba tace, "she's your sister?" Ta fad'a tana kallon Asad ya runtse ido ya bud'e alamun ta dame shi baya son yawan magana amma ta kasa ganewa kafin ya bata amsa Khalifa yace, "Yeah, sister shi ce."
"Woww! Amma basa kama, ya akayi kika bari yayan ki ya fiki kyau haka?. Kalle shi kamar arab in ya shiga cikin larabawan asibitin nan babu wanda zai gane shi" ta fad'a tana kallon sa da murmushi a fuskar ta.
Rauda bata kula ta ba dan haushi ta bata ta lura irin matan nan ne masu shigewa maza ta saci kallon sa taga shima ba ita yake kallo ba, kusa da Khalifa ta k'arasa tace, "Baya magana ne kamar Brother d'insa? Naji kana ce masa deaf kuma naji yayi magana sau d'aya."
"Baya son magana ko kad'an kinji wannan maganar da yayi miki babu lallai ya kuma yi miki wata har ki bar nan gwara ma kiyi shiru" ya fad'a mata a hankali a kunnen ta sai taji ya sake burge ta ta wara idanu tace, "Woww! He impressed me."
Kallon Asad tayi tace, "Lemme help my sister tayi sallah before asuba" ta fad'a tana k'arasowa inda Rauda take tana kallon sa har lokacin. Da hannu Asad ya dakatar da ita alamun ta barshi ya kalli Khalifa shima shi yake kallo kafin Khalifa yace, "Kana kallona kasan ba ko yaushe nake gane me kallon ka yake nufi ba, ka yi magana abeg." Baice komai ba sai ya bar wajan ya fita daga d'akin jim kad'an sai gashi yazo da nurses d'in da alhakin kula da ita yake a wuyan su suna shigowa shi kuma ya juya ya fita.
Dole suma suka fito dan su bar su suyi aikin su suka ganshi zaune akan kujera yana danna wayar sa a nutse bai damu da kowa ana wajan ba, yadda larabawa suke zirga-zirga sai ka d'auka shima balaraben ne hutawa yake yi sabida yadda ya dace da zama balaraben musamman shigar jikin sa da ta sake haska fatar sa. Muhibba ta k'arasa kusa dashi ta zauna a gefen sa tace, "Aliyu abokina ne a school yana ina yanzu? Ko zan iya samun number shi?." In kujerar da suke kai tayi magana tabbas shima yayi bai kalle ta ba wayar kawai yake dannawa.
Zata kuma magana kawai ya mik'e ya bar mata wajan ta bishi da kallo cikin tsantsar burgewa har ya b'acewa ganin ta tayi murmushi tace, "I like his acting" ta fad'a tana murmushi sosai dan ba k'aramin burge ta yayi ba.