Sashe 21
Kwantan Bauna Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu ruwan wani dasu tafiya suke tana takawa a hankali yana zamar mata garkuwa zuciyar sa na harbawa da sauri haka tata zuciyar ma. Dr muhibba suka gani a gaban su tana kallon su har suka zo daf da ita tace, "Sannu Sister ya k'afar?." Haushin ta Rauda take ji haka kawai hakan ya saka tace, "Da sauk'i" ta amsa a tak'aice tana kallon wani wajan daban. Gaban Asad ta tsaya tana kallon sa tace, "Handsome baka ce min komai ba, wallahi da gaske nake ina sonka. Sister baki fad'a masa sak'ona bane ba?."
Gaban Rauda ya fad'i matuk'a bata san ta matsa hannun sa da k'arfi ba ta dai ga ya kalle ta amma bata san me ta aikata ba idanun ta a runtse suke sai ya d'an saki fuska kad'an baiyi magana ba ya taka da niyar barin wajan. "Handsome pls" ta sake tsawaya a gaban sa tana kallon sa kamar zatayi masa kuka.
Kallon ta yayi na sacan d'aya, biyu, uku, kafin ya d'auke idon sa ya rab'a ta gefen ta ya wuce ta sake bin shi da kallo tana shak'ar khamshin turaren jikin sa.
Rauda tayi kicin-kicin da fuska bata san taqamemen abinda yake damun ta ba har suka gama zagayen suka koma d'aki ta zauna a akan kujera tana kallon wani wajan daban ba tare da ta kalle shi ba. Shima bai damu ba dan bai d'auka zata ji haushi ba ya zauna na wani lokaci kafin ya tashi ya fita tabi bayan sa da kallo tana jin wani iri a ranta.
Bayan kwana biyu.
K'afar Rauda tayi kyau sosai har tana takawa babu sanda ba kuma tare da an taimaka mata ba tana tafiya sai ka lura zaka ga tana d'ingishi. Tayi kyau tayi haske fatar ta ta murje tayi kib"a amma ba sosai ba kana dai ganin ta kasan ta samu canji rayuwa sosai musamman a fatar ta da take kyalli tamkar chocolate.
An basu sallama da magani a ranar sai zuwa da zata dinga yi ana duba k'afar sun fito da daddare zasu shiga mota zuwa hotel d'in da suka sauka babu mai magana a cikin su kamar koda yaushe shi yayi shiru itama haka. Yana bud'e motar tana tsaye tana kallon wani wajan daban Muhibba ta k'araso da sauri inda suke tsaye ta kalli Rauda tace, "Sis zaki tafi shine ba sallama?." Rauda ta kalle ta tace, "Ban ganki bane." Muhibba tace, "Saka min number ki ta Nigeria mu dinga gaisa." Rauda tayi jim tana kallon ta domin bata san sabuwar number da ya sake mata ba ita dai kawai tana kiran y'an gidan su amma bata tab'a dubawa ba.
Muhibba ta saci kallon Asad da yake zaune a mota tace, "ki saka min ta yayan ki ma." Rauda ta kalle ta tace, "Wayata ta fad'i ban san inda na ajjiye ta ba." Muhibba tace, "Kuma baki haddace ba?." Rauda ta d'aga kai alamun eh Muhibba ta kalli Asad ta matso kusa da inda yake zaune tace, "Handsome zaka tafi ko goodbye baka ce min ba." Rauda ta zaga ta shiga gaban motar suna har loakcin bataji ya kula Muhibba ba, Rauda na rufe k'ofar motar shima yaja tasa zai kulle Muhibba ta rik'e tace, "Ka bani koda number kane please."
Asad ya d'aga kai ya kalle ta yaja siririn tsaki yaja murfin motar ta saki ya kulle ta kalle shi tana murmushi har suka ja motar bata daina kallon su ba. Suna barin wajan Rauda tayi tsaki tace, "Bata da hankali gabad'aya yarinyar nan ta cika nacin tsiya, haushin ta nake ji" zancen zuci ya fito fili ba tare da ta san hakan ba.
Kallon ta yayi kafin ya d'auke kansa ya cigaba da tafiya. Hotel d'in da suke dai nan suka koma d'akin yana nan tas dashi an gyara tana takawa a hankali ta shiga wanda ta sauka a ciki tana kallon sa tsaf dashi sai khamshi yake yi. Bata jima da zama ba ya shigo da ledar maganin nata ya ajjiye a gefen ta kanzil baice mata ba ya fita ta bishi da kallo kafin tace, "Ina ganin mulkin mallaka ni Rauda, magana ma ta dinga gagarar mutum kuma a haka ace wai yana tare da wacce yake so ne?, mtswwww" ta fad'a tana jin haushin hakan a ranta dan ita sam bata ga wata soyayya a tare dashi ba.
Tana nan zaune ya dawo ya canja kaya zuwa jallabiya blue ya saka hular sanyi blue itama har kunnen sa ya rufe yayi kyau sosai khamshi na tashi a jikin sa ya kalle ta itama shi take kallo yace, "Zaki iya fita?." Kamar tace a'a amma sai ta amsa masa da eh baice komai ba ya juya ya fita. Zaman ta tayi domin baice mata ta taso ba bata d'auka shirun yana nufin ta tawo ba kusan mintina goma tana zaune tana jiran yace ta tawo su tafi.
Gajiya tayi da jira ta fito falon bata ganshi ba kamar b'arauniya take takawa zuwa d'akin da ya sauka ta tura k'ofar ta shiga tana k'arewa d'akin kallo, kamar nata tsaf shima haka yake sai littafai da suke a kan gado na addini dana zamani. Burge ta d'akin yayi sosai ta taka tana k'are masa kallo a hankali domin ya had'u ga girma ga tagar d'akin nasa har tafi wanda take ciki kyau motoci kawai ake gani suna wucewa ta glass d'in.
Har zata juya ta fita kan mudubin ta hango wani katin magani kamar nata da ya b'ata ta dawo da baya ta k'arasa inda yake ta d'auka ta bud'e shi taga katin tane wanda ta yar ranar da suka fara had'uwa dashi ta dawo da wajan mai magani, juya katin take yi kafin tace, "Me ya kawo shi hannun sa har ya tawo dashi k'asar nan?" Ta tambayi kanta ba tare da tasan amsar ba tana sake kallon katin ga sunan tana nan rad'au a jiki.
"Maganin da aka zage ni aka wulak'anta ni a kansa, aka zage ni aka zagi iyayena dan kawai muna karb'ar bashi a kansa. Nifa kome ya faru dani a rayuwa silar gidan su ce" ta fad'a tana ajiiye katin maganin abinda ya faru yana dawo mata. 'Amma kuma ai an siya miki maganin har kika tawo baki daina shan sa ba, kinga kenan an wanke miki ciwon zagin da akayi miki' zuciyar ta ta bata amsa da sauri ta wara idanun ta a bayyane tace, "Kenan hakan yana nufin shine ya siyi maganin...? Anas yace bashi bane daman kuma shi muka d'auka ya siya yace bai siya ba kenan shine....?."
Sai kuma tayi shiru tace, "ta ya zai siya kin magani daga ganina a hanya?."
'Kin manta abinda Khalil ya fad'a a lokacin? Hakan zai iya sakawa ya siya miki magani tunda daman yasan k'anin sane ya buge ki' zuciyar ta ta kuma bata amsa. Rauda ta fito daga d'akin har lokacin tunani take ta zauna a falo tace, "Kenan shine ya siya min magani, shine ya bawa Baba na keke napep, shine ya kawo mana kayan abinci kud'i kuma Anas ne ya aiko dasu. Amma meyasa d'an aike d'aya ne duka ya kawo? Ya akayi yasan kuma Baba na son napep tunda da Anas sukayi magana?" Ta fad'a cikin d'aure kai tana so ta gano bakin zaren.
Bud'e k'ofar akayi aka shigo ta ganshi ya shigo da ledoji k'anana da alama har yaje ma inda yace zata je d'in ya dawo ta bishi da kallo har ya ajjiye ya zauna tace, "shine kaje ka dawo bayan nace zanje." Kallon ta yayi jin tama raina masa hankali wato zaman jiran ta zaiyi har sai sanda ta fito sannan zai tafi.
"Baki son zuwa" ya bata amsa a tak'aice yana bud'e leda guda d'aya ya fito da ice cream a roba sai gumi yake sabida sanyi ya bud'e ya fara sha kafin ya tura mata d'aya ledar gaban ta sai tace, "Ina so naje mana na fito ban ganka ba kuma baka ce min nazo muje ba."
"Oh sai nace kizo?" Ya sake fad'a ba tare da ya kalle ta ba tace, "Eh mana, ai da sai kace min tawo mu tafi sai kawai kayi tafiyar ka bayan nace zanje."
Kai ya girgiza kawai baice komai ba ta bud'e ice cream d'in ta fara sha kamar yadda taga yana sha itama tayi shiru kamar yadda yayi shiru. Knocking d'in k'ofar akayi kafin ya tashi karanbanin Rauda ta riga shi mik'ewa dan tana so ta buɗe k'ofar yadda take bada sauti in an bud'e yana burge ta sosai tana bud'ewa suka had'a ido da Dr Khalifa.
"Lallai patient k'afa yayi kyau" ya fad'a yana shigo yana kallon ta. Murmushi tayi domin sun saba dashi sosai tace, "Alhamdulillah."
"Haka ake so ai" ya fad'a yana kawo hannu yaja kumatun ta yana murmushi itama haka. D'ago idon da zatayi suka had'a ido da Asad ya tsaya cak da shan ice cream d'in yana kallon su kafin ya d'auke kansa ya mayar kan TV.
K'arasawa Khalifa yayi ya zauna kusa dashi yana kallon sa yace, "Prince ga ragowar maganin nata da ba'a karb'a ba d'azu, Sister zo na nuna miki duration d'in kar kiyi mistake." Ba musu Rauda tazo ta zauna ya nuna mata yadda zata sha da yadda zata shafa da ya gama ya bata duka tace, "na gode." Murmushi yayi yace, "haba chocolate colour you deserve anythings from me."
Murmushi tayi bata ce komai ba Asad dai bai tanka musu ba Khalifa ya mik'e yace, "bye deaf dan nasan ba kula ni zakayi ba. Sister Allah ya k'ara lafiya" ya fad'a yana fita ta amsa da amin yaja k'ofar ta zauna ta cigaba da shan ice cream d'inta.
Kallon da taga yanayi mata ne ya saka ta kasa sakewa da ta d'ago sai taga sun had'a ido in ta sauke idon ta ta sake d'agowa sai taga dai kallon ta yake sai ta rud'e ta fara juya cokalin ice cream d'in a cikin robar ba tare da tana sha ba ji take kamar ta tashi ta zura a guje sabida yadda take jin idanun sa a jikin ta.
"Raudaaaa!" Ya kira sunan ta can k'asan makogwaron sa har lokacin idanun sa yana kanta.
Gaban Rauda ya fad'i matuk'a bata san ta matsa hannun sa da k'arfi ba ta dai ga ya kalle ta amma bata san me ta aikata ba idanun ta a runtse suke sai ya d'an saki fuska kad'an baiyi magana ba ya taka da niyar barin wajan. "Handsome pls" ta sake tsawaya a gaban sa tana kallon sa kamar zatayi masa kuka.
Kallon ta yayi na sacan d'aya, biyu, uku, kafin ya d'auke idon sa ya rab'a ta gefen ta ya wuce ta sake bin shi da kallo tana shak'ar khamshin turaren jikin sa.
Rauda tayi kicin-kicin da fuska bata san taqamemen abinda yake damun ta ba har suka gama zagayen suka koma d'aki ta zauna a akan kujera tana kallon wani wajan daban ba tare da ta kalle shi ba. Shima bai damu ba dan bai d'auka zata ji haushi ba ya zauna na wani lokaci kafin ya tashi ya fita tabi bayan sa da kallo tana jin wani iri a ranta.
Bayan kwana biyu.
K'afar Rauda tayi kyau sosai har tana takawa babu sanda ba kuma tare da an taimaka mata ba tana tafiya sai ka lura zaka ga tana d'ingishi. Tayi kyau tayi haske fatar ta ta murje tayi kib"a amma ba sosai ba kana dai ganin ta kasan ta samu canji rayuwa sosai musamman a fatar ta da take kyalli tamkar chocolate.
An basu sallama da magani a ranar sai zuwa da zata dinga yi ana duba k'afar sun fito da daddare zasu shiga mota zuwa hotel d'in da suka sauka babu mai magana a cikin su kamar koda yaushe shi yayi shiru itama haka. Yana bud'e motar tana tsaye tana kallon wani wajan daban Muhibba ta k'araso da sauri inda suke tsaye ta kalli Rauda tace, "Sis zaki tafi shine ba sallama?." Rauda ta kalle ta tace, "Ban ganki bane." Muhibba tace, "Saka min number ki ta Nigeria mu dinga gaisa." Rauda tayi jim tana kallon ta domin bata san sabuwar number da ya sake mata ba ita dai kawai tana kiran y'an gidan su amma bata tab'a dubawa ba.
Muhibba ta saci kallon Asad da yake zaune a mota tace, "ki saka min ta yayan ki ma." Rauda ta kalle ta tace, "Wayata ta fad'i ban san inda na ajjiye ta ba." Muhibba tace, "Kuma baki haddace ba?." Rauda ta d'aga kai alamun eh Muhibba ta kalli Asad ta matso kusa da inda yake zaune tace, "Handsome zaka tafi ko goodbye baka ce min ba." Rauda ta zaga ta shiga gaban motar suna har loakcin bataji ya kula Muhibba ba, Rauda na rufe k'ofar motar shima yaja tasa zai kulle Muhibba ta rik'e tace, "Ka bani koda number kane please."
Asad ya d'aga kai ya kalle ta yaja siririn tsaki yaja murfin motar ta saki ya kulle ta kalle shi tana murmushi har suka ja motar bata daina kallon su ba. Suna barin wajan Rauda tayi tsaki tace, "Bata da hankali gabad'aya yarinyar nan ta cika nacin tsiya, haushin ta nake ji" zancen zuci ya fito fili ba tare da ta san hakan ba.
Kallon ta yayi kafin ya d'auke kansa ya cigaba da tafiya. Hotel d'in da suke dai nan suka koma d'akin yana nan tas dashi an gyara tana takawa a hankali ta shiga wanda ta sauka a ciki tana kallon sa tsaf dashi sai khamshi yake yi. Bata jima da zama ba ya shigo da ledar maganin nata ya ajjiye a gefen ta kanzil baice mata ba ya fita ta bishi da kallo kafin tace, "Ina ganin mulkin mallaka ni Rauda, magana ma ta dinga gagarar mutum kuma a haka ace wai yana tare da wacce yake so ne?, mtswwww" ta fad'a tana jin haushin hakan a ranta dan ita sam bata ga wata soyayya a tare dashi ba.
Tana nan zaune ya dawo ya canja kaya zuwa jallabiya blue ya saka hular sanyi blue itama har kunnen sa ya rufe yayi kyau sosai khamshi na tashi a jikin sa ya kalle ta itama shi take kallo yace, "Zaki iya fita?." Kamar tace a'a amma sai ta amsa masa da eh baice komai ba ya juya ya fita. Zaman ta tayi domin baice mata ta taso ba bata d'auka shirun yana nufin ta tawo ba kusan mintina goma tana zaune tana jiran yace ta tawo su tafi.
Gajiya tayi da jira ta fito falon bata ganshi ba kamar b'arauniya take takawa zuwa d'akin da ya sauka ta tura k'ofar ta shiga tana k'arewa d'akin kallo, kamar nata tsaf shima haka yake sai littafai da suke a kan gado na addini dana zamani. Burge ta d'akin yayi sosai ta taka tana k'are masa kallo a hankali domin ya had'u ga girma ga tagar d'akin nasa har tafi wanda take ciki kyau motoci kawai ake gani suna wucewa ta glass d'in.
Har zata juya ta fita kan mudubin ta hango wani katin magani kamar nata da ya b'ata ta dawo da baya ta k'arasa inda yake ta d'auka ta bud'e shi taga katin tane wanda ta yar ranar da suka fara had'uwa dashi ta dawo da wajan mai magani, juya katin take yi kafin tace, "Me ya kawo shi hannun sa har ya tawo dashi k'asar nan?" Ta tambayi kanta ba tare da tasan amsar ba tana sake kallon katin ga sunan tana nan rad'au a jiki.
"Maganin da aka zage ni aka wulak'anta ni a kansa, aka zage ni aka zagi iyayena dan kawai muna karb'ar bashi a kansa. Nifa kome ya faru dani a rayuwa silar gidan su ce" ta fad'a tana ajiiye katin maganin abinda ya faru yana dawo mata. 'Amma kuma ai an siya miki maganin har kika tawo baki daina shan sa ba, kinga kenan an wanke miki ciwon zagin da akayi miki' zuciyar ta ta bata amsa da sauri ta wara idanun ta a bayyane tace, "Kenan hakan yana nufin shine ya siyi maganin...? Anas yace bashi bane daman kuma shi muka d'auka ya siya yace bai siya ba kenan shine....?."
Sai kuma tayi shiru tace, "ta ya zai siya kin magani daga ganina a hanya?."
'Kin manta abinda Khalil ya fad'a a lokacin? Hakan zai iya sakawa ya siya miki magani tunda daman yasan k'anin sane ya buge ki' zuciyar ta ta kuma bata amsa. Rauda ta fito daga d'akin har lokacin tunani take ta zauna a falo tace, "Kenan shine ya siya min magani, shine ya bawa Baba na keke napep, shine ya kawo mana kayan abinci kud'i kuma Anas ne ya aiko dasu. Amma meyasa d'an aike d'aya ne duka ya kawo? Ya akayi yasan kuma Baba na son napep tunda da Anas sukayi magana?" Ta fad'a cikin d'aure kai tana so ta gano bakin zaren.
Bud'e k'ofar akayi aka shigo ta ganshi ya shigo da ledoji k'anana da alama har yaje ma inda yace zata je d'in ya dawo ta bishi da kallo har ya ajjiye ya zauna tace, "shine kaje ka dawo bayan nace zanje." Kallon ta yayi jin tama raina masa hankali wato zaman jiran ta zaiyi har sai sanda ta fito sannan zai tafi.
"Baki son zuwa" ya bata amsa a tak'aice yana bud'e leda guda d'aya ya fito da ice cream a roba sai gumi yake sabida sanyi ya bud'e ya fara sha kafin ya tura mata d'aya ledar gaban ta sai tace, "Ina so naje mana na fito ban ganka ba kuma baka ce min nazo muje ba."
"Oh sai nace kizo?" Ya sake fad'a ba tare da ya kalle ta ba tace, "Eh mana, ai da sai kace min tawo mu tafi sai kawai kayi tafiyar ka bayan nace zanje."
Kai ya girgiza kawai baice komai ba ta bud'e ice cream d'in ta fara sha kamar yadda taga yana sha itama tayi shiru kamar yadda yayi shiru. Knocking d'in k'ofar akayi kafin ya tashi karanbanin Rauda ta riga shi mik'ewa dan tana so ta buɗe k'ofar yadda take bada sauti in an bud'e yana burge ta sosai tana bud'ewa suka had'a ido da Dr Khalifa.
"Lallai patient k'afa yayi kyau" ya fad'a yana shigo yana kallon ta. Murmushi tayi domin sun saba dashi sosai tace, "Alhamdulillah."
"Haka ake so ai" ya fad'a yana kawo hannu yaja kumatun ta yana murmushi itama haka. D'ago idon da zatayi suka had'a ido da Asad ya tsaya cak da shan ice cream d'in yana kallon su kafin ya d'auke kansa ya mayar kan TV.
K'arasawa Khalifa yayi ya zauna kusa dashi yana kallon sa yace, "Prince ga ragowar maganin nata da ba'a karb'a ba d'azu, Sister zo na nuna miki duration d'in kar kiyi mistake." Ba musu Rauda tazo ta zauna ya nuna mata yadda zata sha da yadda zata shafa da ya gama ya bata duka tace, "na gode." Murmushi yayi yace, "haba chocolate colour you deserve anythings from me."
Murmushi tayi bata ce komai ba Asad dai bai tanka musu ba Khalifa ya mik'e yace, "bye deaf dan nasan ba kula ni zakayi ba. Sister Allah ya k'ara lafiya" ya fad'a yana fita ta amsa da amin yaja k'ofar ta zauna ta cigaba da shan ice cream d'inta.
Kallon da taga yanayi mata ne ya saka ta kasa sakewa da ta d'ago sai taga sun had'a ido in ta sauke idon ta ta sake d'agowa sai taga dai kallon ta yake sai ta rud'e ta fara juya cokalin ice cream d'in a cikin robar ba tare da tana sha ba ji take kamar ta tashi ta zura a guje sabida yadda take jin idanun sa a jikin ta.
"Raudaaaa!" Ya kira sunan ta can k'asan makogwaron sa har lokacin idanun sa yana kanta.