Sashe 4
Dutse Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read
my alkalami
A pages na gaba in sha Allah..........
*WACECE ITA?*
*MEYE LABARINTA*
*SU WAYE DANGINTA?*
*WAYE MAHAIFINTA?*
*WAYE DOGARI?*
*MENENE TAKAMAIMAN MAFARKINTA?*
.................RAI DA LAFIA DAI IN SHA ALLAH...
DAGA ALKALAMIN SAJIDA YAR MUTAN NIGER.
11/14/21, 12:43 PM - Allah Akbar:
*TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_
*[ T.M.N.A]*
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*DUTSE*
RUBUTAWA: *SAJIDA*
SADAUKARWA: *GA MASOYANA*
LABARINA NA: *10*
*
2
An haifeta a shekarar 1997 a jamhuriyar Niger
Ita din y'a ce ga Elhaji Yunusa mai sari da kuma Rukayatu. Ta taso cikin gida mai tarin y'aya domin mahaifiyarta nada kishiyoyi har uku kwarara da suka san da su
Ahalin gidan elhaji Yunusa wasu irin ahali ne masu wuyar kwatance, sun kasance sakaku, bodararu, mararsa kunya da tarbiya, lamarin ya kasance abin tsoro domin ko a tsakanin iyayen da y'ayan ba jin kai da soyaya da ja a jiki bale tsakanin yayun da kannan.
Gida ne ginane mai shegen kyau, gida ne da ya gina shi dan ya yagawa makota da makiyansa, ya dage ya faso gari ya yi ginnin kece raini ne dan kawai ya keta raini a anguwa da jama'ar gari.
Yawancin y'ayan Elhaj Yunusa sun kasance masu girman kai, fadim rai, jiji da kai ko dan suna gannin gidan da suke fitowa a ciki ne? Sam basu dauki halitarsu ta dan adam a matsayin kasa wace gobe ana iya wayar gari su tsinci kansu a nanage a cikin kabari
Rayuwa ta yanci ce ake yi a cikin gidan Elhaji Yunusa, ba abinda ya dame shi da biyan karatun yaro na islamiya ko na gwamnati, idan kana so kar ka yi karatunma ba abinda ya dame shi, sannan idan mace na so kar ta yi aure ta yi ta zamanta a gidan matsalarta ce da ta uwarta, shi dai ba zai kori kowa ba, ba kuma matsalar wani zata saka masa ciwon kai ba, shi din kansa yana rayuwa ce tamkar ta marar adini, shi ba mai zage zage bane, sannan ba mai daurewa yaro gindi bane, shi ba mai yiwa yaro nasiha ko fada bane haka zalika idan ya ga ka matsawa yaronsa yakan ce da kai wai ina dalili ka yi rayuwarka ka sakarwa yaronsa mara shima ya yi fitsari son ransa.
A takaice rayuwa ce marar tsari, a cikinta ta taso mace daya tak a cikin yayunta maza uku, yayun da sai su tashi basa yiwa junna magana bayan ba fada suka yi da junna ba, ba wanda ya damu da dan uwansa, ba wanda yake da ra'ayin damuwa da dan uwansa domin mahaifiyar tasu kanta da ta haife su bata nuna masu mahinmancin hakan ba, a wajenta ita kanta bata damuwa da wani a cikinsu sai idan yana anfanar mata wani abin, sam bata damu da lamarin wani ya kula wani a cikinsu ba, bata tunanin wannan din matsalarta ce, ita dai ta yi mai wuyar tunda ta haifa idan sun ga dama su yi zumunci idan sun kiya su kashe kansu matsalarsu ce!, domin ita a rayuwarta ko kokowar ajiye masu abinci gaskiya ba zata iya ba, wasu iyayen zuwa suke su dibarwa y'ayansu dan kar su dawo su rasa abincin, ita ta fada masu gaskiya idan sun zo da wuri su samu idan basu samu ba su nema su ci a waje itama ta kanta take bata son damuwa
A duniyarta wanda take iya zabura a kowani lokaci ta biya masa bukatarsa mijinta ne, gyara take yiwa kanta na mamaki wanda hakan ya sa shi din kansa baya dadewa bai je mata ba, wannan kawai ya isheta farin ciki domin bata rasa na kashewa in dai zai zo inda take.
Sai dai du iya gyaranta a banza ya tashi domin y'ar da ta haifa da cikinta ba abinda ta iya na fannin gyara, ko girki bata iya ba, abinda kawai ta iya a rayuwarta shine tsafta, bata gajiya da shara da wanke bayi da wanke tufafinta da abin shinfidarta, takan share falonsu a kowani lokaci hakan baya hanna daga ta gama shararta su lalata mata su dawo su yi ta masifa a tsakaninsu tamkar zasu cinye junna danye
*MUNEERATH* ta taso a cikin rayuwa mai duhu, tun Muneerath na da shekaru goma sha daya da ta taba cin sa'ar gannin irin hawan sarki ta dawo gida cike da bege da wani irin tunani, tashin farko ta sanar da mahaifiyarta magana kamar haka" Mama, na ga kwaliya, mama ina burin na auri sarki"
Sai dai amsar da ta samu ita ta saka gwuiwowinta da mafarkinta cenzawa nan take a lokacin da mahaifiyarta ta yi daria tana fadin" Ke mumunan namiji mai kudi kyawawan mata ke wawa, mace bak'a mai muni irinki ai sai dai ki dan lalaba da rokon Allah ko Allah zai sa a cikin bayin gidan wani ya ce yana so, idan kin taki sa'a Dogaro ya yaba kuma shikenan ko ba komai sunnanku yan kusa da sarki!"
Daga wannan rana ta ringa kokaron sannin shin wai wanenema shi *DOGARI* din nan?, meye kusancinsa da sarki? Shin akoy dogari a duniya? Domin sam batama san menene dogari din ba.
A hankali ta gane meye hakan kuma waye hakan, sannan ta ga haza cewar dogari yana da kusanci da sarki har ya taki mukamin rike lemarsa, hakan ya saka ta sauko daga burin da ta ci na sarki ta dawo dogari.
To abin ne yake ta hauhawa, a hankali lamarin yake neman yin kamari da wuce tunanin bawa, ta saka abin a ranta ta yadda ya zamo burinta na biyu a cikin gidan duniya, wanda na farkon kuwa mahaifinta da kansa ne ya yi mata daria kafin ya girgiza kansa ya barta nan tsaye a lokacin da take sanar masa burinta na karatun da take bayan ta kawo masa sakamakon makarantar gwamnatin da take wanda tunda ta shiga makaranta itace ke cin ta farko a kowace jarabawa ta dadage ta ce" *Pa*, da ka ga ina kokarin nan burina na biyu a duniya shine na zama *HOTTEST* "
Da matukar mamaki ya tambayeta " Hottest fa? Na jirgi? "
Cike da kwarin gwuiwa ta gyada kanta tana kallonsa
Idannuwanta dake da color blue mai duhu ya kala da kalar datar jikinta , Muneerath dai ba fara bace ko daya bata da hasken fata aman kuma ba bak'a bace lut, fatarta kalar fatar hausawa ce mai kyan gaske domin a fatarta babu wani waje fari wani waje bak'i, ta yi uniform ne gaba dayanta ta yadda take ba ko fararen sha'a, ba a nan abin yake ba, ba wai matsalar fatarta ba duda a yanzu an waye ba sai farare kawai ake dauka a matsayin hottest ba dan kuwa yanzun ana anfani harda bak'ar fatar da kuma yannayin tsarin halitar mutun da irin yaren da ya iya da iliminsa , sai dai halitar MUNEERATH halita ce da bawa ba zai fahinta ba sai a nan gaba, da ace ita din ta san me Allah ya tara mata a wajen duwawunta da ta ja wa'inda ke yawo da zariyar wando a hannu a kasa ba da komai ba sai da kada luntsuma luntsuman duwawunta da gaya, sai dai rashin sannin ya saka take rayuwarta a yadda ta zo mata
Kansa ya kada ya barta a nan tsaye ba tare da ya bata amsar burinta ba, haka kuma bai karfafa mata gwuiwa ba, sai kishiyar mahaifiyarta da ta gyada kai ta shige dakinta take sanarwa da d'anta cewa lale a yau ta kara yarda cewa MUNEERATH bata da hankali, domin kuwa a yanzu bayan mafarkin dogarin da take ta dawo burinta na kasancewa Hottest, in ba jaraba irin na yarinyar nan ba ina ta ga yannayi na Hottest? "
A haka ta ci gaba da tafiar da tata kalar rayuwar, karatu take ba ji ba gani, abin birgewar sai ka ji tana karatun alkur'ani, tamkar ba yar cikin wannan gida mai wuyar rayuwa ba
Da farko MUNEERATH bata kula samari, bata kula da ko dan gidan waye, daidaikun samarin da a yanzu suka ja suka tsaya suka rike nasu ra'ayin na ba zasu taba kula matan zamani da koda da farinmu muke kara bealiting ba bale bakak'en da muke zama farare dare daya dan lalacewar abokanan rayuwar da suka nuna su sai hasken gida, sai alkyabar mata ba, suka jajirce suka nuna mata kauna, da wa'inda suka gane wannan yarinya mota ce da za'a jima ana tukawa nan gaba, irin manyan motocin zamani masu tafe da bed, watau hutu ce, dunia ce guda suka lalabo dan gwada tasu sa'ar ko za'a dace sai dai ina haka ta ringa tizgawa duda rashin kwaliyarta, haka ta ringa nuna cewar lalala bata yi komai kyankya da kudinka! , sai da ta zauna ta yiwa kanta karatun ta nutsu a kan halayar mahaifiyarta da ta kula cewar eh lale uwarta ce ita ta kawota dunia, aman idan so take mu'amalarsu ta dore ya kasance tana da saurayi mai dan yi mata ihsani , hakan zai saka itama ta samu yanci da soyayar uwa irin na kowa, ba wai dan mamansu bata samu bane, aa, tana samu na mamaki a wajen abansu da yayansu, aman cewa take yaro tun yana yaro ya san ciwonta ya yi mata idan ta mutu ba shikenan ba? Ta more tun harshenta na gane dandanon magi da siga, a haka ta dage, ta mike tsaye, take kula samari daidaiku daga nesa kafin Dogari yake kawo kansa inda take, dan kuwa a soyayarta da dogari Allah kadai take fadawa , ba zata taba iya tarbar namiji ta ce da shi tana sonsa ba, ba wai dan ta san irin ilar da hakan zai iya haifar mata ba, aa, sai dan kawai ita bata ga anfanin aikata hakan ba!
A yanzu shekarun MUNEERATH goma sha takwas ta kawo matakin zana jarabawar dake iya bata damar ahiga University a maysayinta na wace ta bada hankalinta kai da fata take karatunta ya kasance a jarabawar uku sa ake yo har zuwa yanzu bata fadi a ko daya ba, haka kuma a ci gaba daga karamin aji zuwa na gaba da shi ba'a taba mayar da ita baya ba
BAC shine jarabawar da ta damka, wace ta zama mai wuyar samu, a yanzu da shugaban kasarmu ya tsaya tsayin daka ya rufe ido kan irin yadda wasu malaman makarantar da iyayen da son y'ayansu suka rufe masu ido suke mika dan abin ihsani ana tsalakar da y'ayansi, da samarin dake yiwa yan matansu, da mazan dake tsalake matayensu, da dangi, da sannin sanni du ya ture ya ja ya tsaya a kan kafafuwansa ya kafa matalan tsaro ta yadda iliminki zai kwato maka, sai ta kara daura damarar karatu ba dare ba rana, idan suka je aji suka dauko karatun da malamai ke masu duda yawanci a irin shekarun nata yan mata kai na hayaki, ido na tsaitsaye, abinda suka fi hangowa shine show......a je makarantar a ki yin karatun a hade da yan mata a restaurant a ci abinci a bige da selfi, a saka kida a sha casu, a ringa kule kulen samari ana abubuwa sai an zo shiga a haukace ana kame kame.....sam sam Muneerath bata kasance a cikin irin yan matan nan ba, wannan abin ya saka take da masu son kulata sosai, ko dan mutun ya karu da baiwar ilimin da Allah ya yi mata, ita din ba za'a kireta da mafadaciya ba domin bata fadan da ba dalili, idan ka ga fadanta tabata an tabata ne, wannan kuma takan ce a gaskiya ba zata iya kawar da kai a mayar da ita sakarai ba
..................back
Yinwar da take ji tun ta rana da ta riko daga makaranta ita ta ci gaba da rikewa har dare ya yi kafin ta cenza tufafin jikinta ta shanya wa'inda ta cire din bayan ta wanke su a bayin tsakiyar gidan ta zo ta dauki litafinta ta zauna ta dukufa ta shiga karatu tana jin juwa na son kadata a zaunen da take
Yayanta ne daya daga cikin yayunta mudaseer ya shigo har dakinta
Ido hudu suka yi kafin ya zauna saman yar kujerar dakin nata yana bin dakin da kallo ya ce"
*Sajida ce*
11/14/21, 12:43 PM - Allah Akbar:
*TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_
*[ T.M.N.A]*
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
A pages na gaba in sha Allah..........
*WACECE ITA?*
*MEYE LABARINTA*
*SU WAYE DANGINTA?*
*WAYE MAHAIFINTA?*
*WAYE DOGARI?*
*MENENE TAKAMAIMAN MAFARKINTA?*
.................RAI DA LAFIA DAI IN SHA ALLAH...
DAGA ALKALAMIN SAJIDA YAR MUTAN NIGER.
11/14/21, 12:43 PM - Allah Akbar:
*TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_
*[ T.M.N.A]*
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
*DUTSE*
RUBUTAWA: *SAJIDA*
SADAUKARWA: *GA MASOYANA*
LABARINA NA: *10*
*
2
An haifeta a shekarar 1997 a jamhuriyar Niger
Ita din y'a ce ga Elhaji Yunusa mai sari da kuma Rukayatu. Ta taso cikin gida mai tarin y'aya domin mahaifiyarta nada kishiyoyi har uku kwarara da suka san da su
Ahalin gidan elhaji Yunusa wasu irin ahali ne masu wuyar kwatance, sun kasance sakaku, bodararu, mararsa kunya da tarbiya, lamarin ya kasance abin tsoro domin ko a tsakanin iyayen da y'ayan ba jin kai da soyaya da ja a jiki bale tsakanin yayun da kannan.
Gida ne ginane mai shegen kyau, gida ne da ya gina shi dan ya yagawa makota da makiyansa, ya dage ya faso gari ya yi ginnin kece raini ne dan kawai ya keta raini a anguwa da jama'ar gari.
Yawancin y'ayan Elhaj Yunusa sun kasance masu girman kai, fadim rai, jiji da kai ko dan suna gannin gidan da suke fitowa a ciki ne? Sam basu dauki halitarsu ta dan adam a matsayin kasa wace gobe ana iya wayar gari su tsinci kansu a nanage a cikin kabari
Rayuwa ta yanci ce ake yi a cikin gidan Elhaji Yunusa, ba abinda ya dame shi da biyan karatun yaro na islamiya ko na gwamnati, idan kana so kar ka yi karatunma ba abinda ya dame shi, sannan idan mace na so kar ta yi aure ta yi ta zamanta a gidan matsalarta ce da ta uwarta, shi dai ba zai kori kowa ba, ba kuma matsalar wani zata saka masa ciwon kai ba, shi din kansa yana rayuwa ce tamkar ta marar adini, shi ba mai zage zage bane, sannan ba mai daurewa yaro gindi bane, shi ba mai yiwa yaro nasiha ko fada bane haka zalika idan ya ga ka matsawa yaronsa yakan ce da kai wai ina dalili ka yi rayuwarka ka sakarwa yaronsa mara shima ya yi fitsari son ransa.
A takaice rayuwa ce marar tsari, a cikinta ta taso mace daya tak a cikin yayunta maza uku, yayun da sai su tashi basa yiwa junna magana bayan ba fada suka yi da junna ba, ba wanda ya damu da dan uwansa, ba wanda yake da ra'ayin damuwa da dan uwansa domin mahaifiyar tasu kanta da ta haife su bata nuna masu mahinmancin hakan ba, a wajenta ita kanta bata damuwa da wani a cikinsu sai idan yana anfanar mata wani abin, sam bata damu da lamarin wani ya kula wani a cikinsu ba, bata tunanin wannan din matsalarta ce, ita dai ta yi mai wuyar tunda ta haifa idan sun ga dama su yi zumunci idan sun kiya su kashe kansu matsalarsu ce!, domin ita a rayuwarta ko kokowar ajiye masu abinci gaskiya ba zata iya ba, wasu iyayen zuwa suke su dibarwa y'ayansu dan kar su dawo su rasa abincin, ita ta fada masu gaskiya idan sun zo da wuri su samu idan basu samu ba su nema su ci a waje itama ta kanta take bata son damuwa
A duniyarta wanda take iya zabura a kowani lokaci ta biya masa bukatarsa mijinta ne, gyara take yiwa kanta na mamaki wanda hakan ya sa shi din kansa baya dadewa bai je mata ba, wannan kawai ya isheta farin ciki domin bata rasa na kashewa in dai zai zo inda take.
Sai dai du iya gyaranta a banza ya tashi domin y'ar da ta haifa da cikinta ba abinda ta iya na fannin gyara, ko girki bata iya ba, abinda kawai ta iya a rayuwarta shine tsafta, bata gajiya da shara da wanke bayi da wanke tufafinta da abin shinfidarta, takan share falonsu a kowani lokaci hakan baya hanna daga ta gama shararta su lalata mata su dawo su yi ta masifa a tsakaninsu tamkar zasu cinye junna danye
*MUNEERATH* ta taso a cikin rayuwa mai duhu, tun Muneerath na da shekaru goma sha daya da ta taba cin sa'ar gannin irin hawan sarki ta dawo gida cike da bege da wani irin tunani, tashin farko ta sanar da mahaifiyarta magana kamar haka" Mama, na ga kwaliya, mama ina burin na auri sarki"
Sai dai amsar da ta samu ita ta saka gwuiwowinta da mafarkinta cenzawa nan take a lokacin da mahaifiyarta ta yi daria tana fadin" Ke mumunan namiji mai kudi kyawawan mata ke wawa, mace bak'a mai muni irinki ai sai dai ki dan lalaba da rokon Allah ko Allah zai sa a cikin bayin gidan wani ya ce yana so, idan kin taki sa'a Dogaro ya yaba kuma shikenan ko ba komai sunnanku yan kusa da sarki!"
Daga wannan rana ta ringa kokaron sannin shin wai wanenema shi *DOGARI* din nan?, meye kusancinsa da sarki? Shin akoy dogari a duniya? Domin sam batama san menene dogari din ba.
A hankali ta gane meye hakan kuma waye hakan, sannan ta ga haza cewar dogari yana da kusanci da sarki har ya taki mukamin rike lemarsa, hakan ya saka ta sauko daga burin da ta ci na sarki ta dawo dogari.
To abin ne yake ta hauhawa, a hankali lamarin yake neman yin kamari da wuce tunanin bawa, ta saka abin a ranta ta yadda ya zamo burinta na biyu a cikin gidan duniya, wanda na farkon kuwa mahaifinta da kansa ne ya yi mata daria kafin ya girgiza kansa ya barta nan tsaye a lokacin da take sanar masa burinta na karatun da take bayan ta kawo masa sakamakon makarantar gwamnatin da take wanda tunda ta shiga makaranta itace ke cin ta farko a kowace jarabawa ta dadage ta ce" *Pa*, da ka ga ina kokarin nan burina na biyu a duniya shine na zama *HOTTEST* "
Da matukar mamaki ya tambayeta " Hottest fa? Na jirgi? "
Cike da kwarin gwuiwa ta gyada kanta tana kallonsa
Idannuwanta dake da color blue mai duhu ya kala da kalar datar jikinta , Muneerath dai ba fara bace ko daya bata da hasken fata aman kuma ba bak'a bace lut, fatarta kalar fatar hausawa ce mai kyan gaske domin a fatarta babu wani waje fari wani waje bak'i, ta yi uniform ne gaba dayanta ta yadda take ba ko fararen sha'a, ba a nan abin yake ba, ba wai matsalar fatarta ba duda a yanzu an waye ba sai farare kawai ake dauka a matsayin hottest ba dan kuwa yanzun ana anfani harda bak'ar fatar da kuma yannayin tsarin halitar mutun da irin yaren da ya iya da iliminsa , sai dai halitar MUNEERATH halita ce da bawa ba zai fahinta ba sai a nan gaba, da ace ita din ta san me Allah ya tara mata a wajen duwawunta da ta ja wa'inda ke yawo da zariyar wando a hannu a kasa ba da komai ba sai da kada luntsuma luntsuman duwawunta da gaya, sai dai rashin sannin ya saka take rayuwarta a yadda ta zo mata
Kansa ya kada ya barta a nan tsaye ba tare da ya bata amsar burinta ba, haka kuma bai karfafa mata gwuiwa ba, sai kishiyar mahaifiyarta da ta gyada kai ta shige dakinta take sanarwa da d'anta cewa lale a yau ta kara yarda cewa MUNEERATH bata da hankali, domin kuwa a yanzu bayan mafarkin dogarin da take ta dawo burinta na kasancewa Hottest, in ba jaraba irin na yarinyar nan ba ina ta ga yannayi na Hottest? "
A haka ta ci gaba da tafiar da tata kalar rayuwar, karatu take ba ji ba gani, abin birgewar sai ka ji tana karatun alkur'ani, tamkar ba yar cikin wannan gida mai wuyar rayuwa ba
Da farko MUNEERATH bata kula samari, bata kula da ko dan gidan waye, daidaikun samarin da a yanzu suka ja suka tsaya suka rike nasu ra'ayin na ba zasu taba kula matan zamani da koda da farinmu muke kara bealiting ba bale bakak'en da muke zama farare dare daya dan lalacewar abokanan rayuwar da suka nuna su sai hasken gida, sai alkyabar mata ba, suka jajirce suka nuna mata kauna, da wa'inda suka gane wannan yarinya mota ce da za'a jima ana tukawa nan gaba, irin manyan motocin zamani masu tafe da bed, watau hutu ce, dunia ce guda suka lalabo dan gwada tasu sa'ar ko za'a dace sai dai ina haka ta ringa tizgawa duda rashin kwaliyarta, haka ta ringa nuna cewar lalala bata yi komai kyankya da kudinka! , sai da ta zauna ta yiwa kanta karatun ta nutsu a kan halayar mahaifiyarta da ta kula cewar eh lale uwarta ce ita ta kawota dunia, aman idan so take mu'amalarsu ta dore ya kasance tana da saurayi mai dan yi mata ihsani , hakan zai saka itama ta samu yanci da soyayar uwa irin na kowa, ba wai dan mamansu bata samu bane, aa, tana samu na mamaki a wajen abansu da yayansu, aman cewa take yaro tun yana yaro ya san ciwonta ya yi mata idan ta mutu ba shikenan ba? Ta more tun harshenta na gane dandanon magi da siga, a haka ta dage, ta mike tsaye, take kula samari daidaiku daga nesa kafin Dogari yake kawo kansa inda take, dan kuwa a soyayarta da dogari Allah kadai take fadawa , ba zata taba iya tarbar namiji ta ce da shi tana sonsa ba, ba wai dan ta san irin ilar da hakan zai iya haifar mata ba, aa, sai dan kawai ita bata ga anfanin aikata hakan ba!
A yanzu shekarun MUNEERATH goma sha takwas ta kawo matakin zana jarabawar dake iya bata damar ahiga University a maysayinta na wace ta bada hankalinta kai da fata take karatunta ya kasance a jarabawar uku sa ake yo har zuwa yanzu bata fadi a ko daya ba, haka kuma a ci gaba daga karamin aji zuwa na gaba da shi ba'a taba mayar da ita baya ba
BAC shine jarabawar da ta damka, wace ta zama mai wuyar samu, a yanzu da shugaban kasarmu ya tsaya tsayin daka ya rufe ido kan irin yadda wasu malaman makarantar da iyayen da son y'ayansu suka rufe masu ido suke mika dan abin ihsani ana tsalakar da y'ayansi, da samarin dake yiwa yan matansu, da mazan dake tsalake matayensu, da dangi, da sannin sanni du ya ture ya ja ya tsaya a kan kafafuwansa ya kafa matalan tsaro ta yadda iliminki zai kwato maka, sai ta kara daura damarar karatu ba dare ba rana, idan suka je aji suka dauko karatun da malamai ke masu duda yawanci a irin shekarun nata yan mata kai na hayaki, ido na tsaitsaye, abinda suka fi hangowa shine show......a je makarantar a ki yin karatun a hade da yan mata a restaurant a ci abinci a bige da selfi, a saka kida a sha casu, a ringa kule kulen samari ana abubuwa sai an zo shiga a haukace ana kame kame.....sam sam Muneerath bata kasance a cikin irin yan matan nan ba, wannan abin ya saka take da masu son kulata sosai, ko dan mutun ya karu da baiwar ilimin da Allah ya yi mata, ita din ba za'a kireta da mafadaciya ba domin bata fadan da ba dalili, idan ka ga fadanta tabata an tabata ne, wannan kuma takan ce a gaskiya ba zata iya kawar da kai a mayar da ita sakarai ba
..................back
Yinwar da take ji tun ta rana da ta riko daga makaranta ita ta ci gaba da rikewa har dare ya yi kafin ta cenza tufafin jikinta ta shanya wa'inda ta cire din bayan ta wanke su a bayin tsakiyar gidan ta zo ta dauki litafinta ta zauna ta dukufa ta shiga karatu tana jin juwa na son kadata a zaunen da take
Yayanta ne daya daga cikin yayunta mudaseer ya shigo har dakinta
Ido hudu suka yi kafin ya zauna saman yar kujerar dakin nata yana bin dakin da kallo ya ce"
*Sajida ce*
11/14/21, 12:43 PM - Allah Akbar:
*TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_
*[ T.M.N.A]*
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/