← Book details Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 85 OF 121

Chapter 84

Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

By
Gentle Lady💃🏽


Zaune suke dadare suna cin abinci lubabatu tace nikuwa yau akwai maganarda nakeso muyi dakai""" yakalleta yace Allah yasadai lafiya ??? Tarausayarda kai tana kallon khadija cikin fara a tace insha Allah baridai mukarasa cin abincin"" yace nidai kifadamun yanzu kinsanni da zumudi kamar sabon angwo gabadaya suka kwashe da dariya harsu labila""


Yace tokokunga laifina ninafison idan za afadamun Abu kawai afada yanzu kafin mugama bakisan iyah jaye jayenda zuciyata zatayiba""" adaure afadamun

Cikin siririyar muryanta tace daddy kasanfa ba amfanie ana cin abinci ana magana kamar bakabawa abincin mahimmanciba""" yakalleta gaskiyarkifa Deejarh tobari mugama yayi maganar yana kallon lubabatu murmushi kawai tayi tacigaba dacin abincinta

Aranta tace wannan hartasoma tafi labila iyah yi shi abincin harsai anyiwani girmamasa 🙄"" tsaki tayi aranta tacigaba dacin abincinta"" bayan sungama sannan yakalleta yace karfa kice naciga zanzari nasan duk abunda zaifito bakin nan naki alkhairine murmushi tasaki har hakoranta suka fito tace ko???

Yace koma zakice ainidanake dake nasan haliinki fiye dake kanki""" labila kam murmushi tayi aranta tace kadaisan Wanda kasani amman babu Wanda yasan halin mom sai Allah nda yahalicceta"""

Tace hakane abunda yake gefenta tadauko Tamika masa tana murmushi shima murmushin yakeyi taredakuma mamakin menene aciki???

Tagane abunda yakenufi tace kabuda kaganie mana""" bamusu yabude biza ce tazuwa Dubai

Baki sake yake kallonta yace biza naganie??? Tamurmusa ah takuce "" tanisa tana kallon khadija tace wannan itace kyautar taya murnar auren Ku nabarku kumore amarcinku har Kanwata tasamu rabo""" dasauri khadija tasun kuyarda kanta kasa saboda kunya

Usman yarasama dawadanne irin haruffa zaiyi amfani domin yagodemata dakyar ya iyah hadiye yawun bakinsa dasuka kafe yatttaro sauran maganarda ke bakinsa yace

Maman Abdul wai dagaske kike kuwa??? Tagyada kanta sosaima aikasan inason farincikinka fiye da nawa inaso kasamu cikar burinkane bazanso kacigaba tatauyewa kanka hakkiba

Nalurah kanwar tawa bazata saki jiki dakaiba saboda tanada kunya shiyasa nashirya maku tafiyar kozatadan sake dakai

Yasaki lallausan murmushi Alhamdulillah amman naji dadi sosai bansan dawadanne irin kalamai zanyi amfanie wajen godemakina tnx matata

Murmushi tasaki najindadi tace basaika godemunba wannan aikinane nashirya maka kayanka""" sauran nata tashirya dan jirgin shadaya zakubi

Yayi murmushi yana kallon khadija takasan ido wacce haryanzu idanuwanta suna kasa kosaudaya bata dagoba"" labila kam tashiga tashin hankali dankuwa tana tunanin wannan abun kamar wata munakisar lubabatu tashirya Amman babu yanda zatayi tawargaza tafiyar tunda batada bakin fadin komai akan mahaifiyarta Amman alal hakika ranta baikwanta da wannan tafiyarba

Dolene tasamu malaminsu saboda ayiwa khadija saukar qur Anie murmushi tayi afili sanin tasamo mafita lubabatu tana jefar labila da murmushi itama haka kowannensu shikadai yasan ma anar murmushin nasa

Labila tace sahiba tashi muje intayaki hada kayanki dankinsan dasafe bazaki samu damar hadawaba tayi maganar tanajan hannunta

Tamike jiki bakwari tabi labila kamar rakumie da akala sukuma suka rakasu da idanuwa lubabatu tanayiwa Khadija kallon kingama yawo yarinya tunda kika auri mijina

Usman kuwa yanayimata kallon soda kauna yanarayawa aransa zaihuta sosai da Deejarh nsa" saida suka bacewa ganinsu sannan Usman yamike yaja hannun lubabatu suka dawo falon saman kujera suka zube

Yakuramata ido yana murmushi itama shitakeyi tace yadai mijina""" yamuskuta lubcy wlh mamaki kikebani sosai"" tarausayarda kai tace mamakin menene???

Yace yanda kike kyautatamun wai anyama zamanin nan za asamu mata masu irin halayyarki??? Gaskiya baza asamuba""" tace nidai kadaina fasamun kai da dadin bakin nan naka

Yajawota jikinsa yace badadin bakibane wlh dagaske nake nikam nayi sa ar mata tagari wacce kowanne namiji zaiyi mafarkin mallakar irinta"""

Hawayene suka sauko akan kumatun lubcy sanyinsu yaji ajikinsa yajuwoda itah dasauri yace lafiya lubcy menene kuma nakuka??? Please banason kukan nan nakie Dan Allah kidaina

Tashare hawayenta tace inajin takaiicin kaina daya kasance bana baka hakkinka dayake kaina yanda yakamata inayin hakanne kodan Allah yayafemun hakkinka danaketauyewa ninasan ina cutarda rayuwarka

Banason inzama daya dagacikin matanda Allah zaiyi fushidasu Usman yadorah yatsanshi akan labbanta yace bakyacikinsu matata nibaki tauyemun hakkinaba aihakan Allah ya halicceki kuma kinayin iya kokarinki wajen ganin nasamu kwanciyar hankali nagode maki Allah yabarmu tare yasake janta jikinsa yana aikamata wani sako mai rikitarwa

Al amarinsu labila kuwa suna hawa bangaren khadija tasheka dagudu saman gado taboye fuskarta""" labila mezatayi inba dariyaba saida tayi mai isarta tace wlh nifa mamaki kikeban kowaya fadamaki yanzun anajin kunyar soyewa danamiji

Kinganni nan wlh idan nai aure saina baki mamaki Dan wlh agaban kowayema zannunawa mijina soyayya gashidai kin girmeni Amman ninafiki sanin yanda ake tarairayar miji

Tazauna kusa da itah sahiba wannan tafiyarda zakuyi wata damace agareki daxaki saye zuciyar mijinki ki ajiye kunyar nan taki kinunawa mijinki tamkar dagake saishi kuke acikin duniyarku

Idan kinataredashi kimanta dakowa kigamsarda mijinki Dari bisa Dari kedin tashice kuma mallakarsa tarage murya kuma wlh karyanemi kibashi hakkinsa kiyita gudunsa

Khadija tamike takaimata duka tace waike yaushe kikazama marar kunya bansaniba??? Labila tace ke yarinya zauna nan ainadade inacemaki kifara chating kozaki koyi yanda ake ririta miji kinki hmmm wlh jinake damanice ke danatsula tsiya sai nasakawa wata hawanjinie😕😂

Khadija tatureta tace Allah yashiryaki mom din??? Tace au sorry namanta ashefa mom ce baridai inhadamaki kayan dannasan halinki innabiye maki manyan kaya zakidauka duka tayi maganar tana mikewa tabude drawer tajawo akwatin kayan khadija

Tahau duba kayan ciki kananun kaya tayita shiryawa khadija saboda Usman yasiyamata kananun kaya masu masifar kyau

Mini sket da kananun kaya gasunan kamar kazanta""" manyan kaya kala uku kawai tasakamata"" takoma hadamata kayan kwalliya komai saida tasaka tace sauran kuma idan kinje karkiyi kwalliyar""" nasan halinki"" danzankirah inji waima ina wayarki???

Khadija tace nafadawa dad fa yakarbomun gida namanta ta wlh kuma inason yin magana da Yayana Amman nakasa tambayarsa koya karbo kumashi baicemun komaiba"" labila tace kinsone wlh dakinason wayadashi aidasaikice inbaki Aron wayata saiki kirashi""

Tamere baki inna hardace nomber din kokuma inbar hardaceba"" labila tace kumafa hakane Amman aidason ranki lanbarda batawuce ashirinba keda kikeda kwakwalwa maikyau kikasa hardacewa

Tace kwakwalwata ta karatuce bawai danna hardace tarkacen numbers ba""" labila tace hakanefa ustaziyya Amman kinsan hardace number yanada amfani kodan watarana

Bawai ina fataba kisamu kanki inda kike neman agaji abaki Aron waya baki hardace number kowaba yakenan gashima dai yanzu karamin misali kinason waya da ya muktar Amman bakisan number saba

Khadija tace kinada gaskiya zanyi kokarin hardace tamutum biyu"" labila tace Yayana dakuma daddy ko ???

Murmushi khadija tayi labila tace bakomai mukoda ba a hardace tamuba badamuwa Amman inafatardai abunda nafadamaki dazun kinkwasheshi afaifan kanki wlh sahiba inajimaki tsoron wata baturiya takwace makishi

Aikuwa khadija tahade rai labila tahauyi mata dariya tatashi tabita sukahau zagayen dakin karshedai labila tafada saman gado tana hakiii tace tubanake small momy🤗

Khadija tace aisaikinsha rankashi aka"" labila tarumtse ido takankance kai tanadafe dakai tanajiran saukar rankwashi khadija tahauyi mata dariya tazube saman gadon tace waike atunaninki rankwashinki zanyi aka???


Ainibazan rankwashi kainaba idan dady yasamu baturiya aibanice zanyi kishiba kece dannasan kinfison farincikine fiyedani Kaina yanda kika damu dani nibandamu dakaina hakanba """

Labila tace aisaboda kinsan hakan shiyasa kikemun abunda kikaga dama takwanto saman kafafuwan khadija tace wlh sahiba jinakeyi kamar aduniya bazanso kowa sama dakeba

Idan akacire Allah da manzonsa da sahabai dakuma ahalal baitiii idan za akuma tambayana wanakeso bayansu kinsan wazanfada???

Khadija tagirgiza kai labila tace wlh sahiba sunanki zankirah !! Jinake tamkar sabodake akayini kullum soyayayrki sake shiga rainatake bansan daliliba kodan kinason babanane

Khadija tayi murmushi tace dama haka Allah yake ikonsa soyayya gamon jinice""labilata tashi zaune takurawa. Khadija ido kamar mainazarin wani abun saikuma tafashe dakuka data tunoda kudirin lubabatu akan Khadija

Itama batasan sanda tafara kukanba suka hade kai sunata kuka akarasa Wanda zai rarrashi wanie


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
Chapter 85 · 0% Book details