← Book details Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 21 OF 121

chapter 24

Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

By
Gentle Lady💃🏽


Cikin kidima yayi kan gadon yana girgizata yana kiran sunanta dakarfiii Amman ina ko motsi batayi"""

Daukarta yayi kamar jaririya yafito gidan tacikin na urah yashigo zuwa kasa saboda yayi sauri tunkafin yasauka yasoma kwalawa driver kirah

Cikin barcinsa yaji ana kiransa"" firgigita yafarka yafito dasauri yana ganin halinda alhaji yakeciki Yakoma dasauri yadauko key din mota riga ahannu yafito

Haryanzu usman jijjiga ameena yakeyi idanuwansa sunyi jajir tamkar gauta kadan yarage yasoma darzar kuka saidai kawai danyana namijine yanada juriya"" tuni driver yabude masa bayan motar yashiga da itah shikuma yazagaya yafita dasauriii zuwa hospital""

Tunkafin sukai yakirah family doctor dinsu yasanar dashi yace yana asivitin dan yana dutyn dare ne"" sunakaiwa yanabakin asivitin tareda wadansu nurse tareda gado""" yanayin pkng yadaukota akaturahta saman gado zuwa emergency

Abakin kofa akabarshi Saikai kawo yakeyi tamkar yayi kuka"" tunda suka shiga da itah sukahau dubata saidai Ashe raiyayi halinsa"" zuciyarta ce tabuga!!

Sosai yayi mamakin ciwon zuciya dahar yacita haka haryayi mata wannan illar Amman Sam shi baisan ciwon nata yakai hakanba"""

Jiki asanyaye yafito dakin tareda sauran nurse "" Usman yana ganinsa yasoma tambayar lafiyar meenal""

Doctor yajikinta ???? Tasamu saukiko???? Dan Allah zan iyah ganinta?? Banaso narasata doctor haka yayita jeromasa tambayoyi tamkar maitabin hankali

Gabadaya yabawa likitocin tausayi"" yace doctor bakace komaiba yajikin meenal din?? Yanisa yace tasamu sauki yadafashi saidai kayi hakuri Usman

Koda kukashigo asivitin nan tuni Allah yakarbi abarshi""" cikin razana yadago manyan idanuwansa yadorasu akan doctor din

Hannunsa yasaka yature hannun doctor dayake kan kafadarsa yayi cikin dakin dagudu doctor yabishi yana kiran sunansa

Yanaashiga yajaye kyallenda aka rufeta dashi fuskarta tayi fayau tamkar tana murmushi tayi haske dukawa yayi akan guiwarsa yariko hannunta cikin nashi

Cikin rawar murya yace yanzu dama tafiya zakiyi kibarni meenal duk wannan abun dakikemun na bankwanane take yafashe dakuka """

Doctor ne yadafashi yace hakuri zakayi Usman lokacintane yayi babu magani saimuyi mata fatar Allah yajikanta yasa tahuta"" ayanzu adduarka kawai takebukata

Mikewa yayi yayi hanyar fita""" saidai yaji yarabke yafadiii dasauri yakarasa wajensa yanakiran nurse "" dagudu sukazo akadauki Usman akadorah akan gado take aka bashi taimakon gaggawa

Ganin yafarfado yasaka akajona mashi Karin ruwa tareda allurar barcii "" driver"" yana waje baisan halinda uban gidansa yake cikiba"" saida doctor yasanar dashi"""

alokacin ansoma kiraye kirayen asuba" wayarsa doctor yadauko aka Kira hajiya akasanarda itah"""

Karfe bakwai darabi yamata acikin kaduna tuni labari yakai gidansu ameena"" mahaifin Abdul da Abdul suna asivitin
Tuni akadau gawar ameena zuwagida dangin ameena saidai sukaji mutuwar kamar dagasama

Koda yafarfado hajiya da Hafiz sunakusa dashi hawayene yasoma sauka gefen idanunshi hajiya tace sannu babangida""

Runtse idonsa yayi yace mom tatafi tabarniko??? Tashafo kansa tace addua zakaimata babangida lokacintane yayi"""

Yanisa inason ganinta kicewa Hafiz yakirah doctor"" takalli Hafiz tace yakirashi yace to tareda juyawa Abdul yadawo kusadashi yadafa kansa Amman yakasa cewa komai"" yana tausayin abokinsa danyasan yanason ameena sosai

Doctor yanazuwa yace badamuwa yana iyah zuwa"" taresuka fito suka dunguma"" saigidansu Ameena sunsamu har anyimata wanka""" Usman yamatsakusa da itah yayi mata addua tare akai mata sallah

Tatara mutane sosai akakaita makwancinta""" Sam babu Wanda yatuna da kaleed saibayan da hajiya takoma gidan tasameshi yanata kuka sosai ta tausaya masa"""

Saida akai sadakar uku kubra tazo tareda mijinta"" itakanta tasha kuka datasamu labarin"" Usman yakoma shiru shiru dagashi har kaleed sunrame danbasacin abinci sai hajiya tayi dagaske

Bayan wata biyu darasuwar Ameena zuwa yanzu Usman yafauwalawa Allah lamarinsà"" Yakoma wajen harkokinsa Amman haryanzu baikoma daidaiba

Hajiya takoma tareda kaleed hannunta saboda haryanzu yaki kwantarda hankalinsa"""

Kwance take tanajuyi cikin barcinta"" zunbur tatashi "" tasoma dube dube mafarkinda tayi kamar almara"""ihun murna tayi tamike yauzataga handsome dinta towadanne irin kayama zatasaka tarasa inda zatasaka ranta danjin dadi

Mikewa tayi tafada wanka"" agurguje tayi wanka tashirya cikin atamfa takawo hijabinta tasaka harkasa"""

Wayarta kawai tadauka tafita unguwar kowa yayi mamakin ganinta da hijabi akafa take tafiya tayi nisa da unguwarsu sosai wata motace tayo cikinta sauran kadan tabugeta tayi gefe dasaurii Amman dukda haka saida yasameta aikuwa tafadiii kiiii yatsaida motarsa yafito dasauriii dasauriii yana furta innalillahi tadago takalleshi tuni tawashe hakorah tunawa dazancen *hatsabibin boka* yasa tayisaurin dukadda kanta gabanta nafaduwa

Muryansa maisanyice taratsa dodon kunnenta sannuko inafatardài bakiji rauniba??? Kaitagyada masa tamike tana karkabe hijabinta"" yakuramata ido takeyaji Sonta yashiga ransa talurah da irin kallondà yakematà dadi kamar tafasa ihu arantakuwa tana aiyanawa ashema yafi kyau afili


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
Chapter 21 · 0% Book details