← Book details Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 68 OF 121

Chapter 72

Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

By
Gentle Lady💃🏽


Tundaga muktar har khadija babu Wanda yaruntsa harsafe khadija takwana kuka kafin safe wani zazzafan zazzabine yakamata jikinta yagashe kamar wuta

Sallar asuba kanta dakyar tayi gashi jiya bataci abinciba"" dasafe inna takawo mata abun karinta tatasheta tace takoshi

Babuyanda inna batayiba Amman takici dataga zatadameta tace zataci inna tanafita tasake gyara kwanciya"" tana nan kwance har azahar muktar baishigo dakinba

Inna tasake kawo abincin rana tasamu nasafen bataciba"" ta ajemata tafita dakin muktar tayi saita sameshi zaifito kenan yana ganinta yadansaki ransa yagaida itah

Ta amsa tace idan zaka iyah rarrashin sarkin zuciyar cen kaje wlh yaukoruwa batasha ba rabonta da abinci tunjiya dasafe babu yanda banyi da itah dasafe ba tanuna masa kaga karinta nasafe yanzu danakai narana nadaukoshi

Yayi shiru sannan yace shikenan yajuya zuwa dakinta koda yaturah kofa idonta rufe yake yataka harbakin gadon yazauna yakuramata ido

Yasan tasan shine dangashinan idanuwanta sunsoma zubarda kwalla duk da arufe suke" sunanta yakirah bata amsaba"" baidamuba yace kitashi kici abinci

Nandinma banza taimasa yaturah hannunsa daniyar yatasarda itah mugun zafinda yaji shiyasa yacire hannunsa dasauri batareda yayi niyaba

Cikin tashin hankali yace khadija bakida lafiya Daman??? Meyasa baki sanardaniba duk arude yake maganar dasauri yafita yacewa innah kishirya ta yanzu zandawo da doctor yadubata yafita dasauri yana dauko waya cikin aljihunsa

Abokinsa Abubakar yakirah yasanardashi yana kano yanzu haka yanason ganinsa "" yace toyasameshi gida danyanzu Hutu yake yace toganinan tafe

Yanagama wayar yatari Dan adaidaita zuwa gidan sa bayan yakirasa yace yakaraso saiyafito motarsa sukashiga zuwa gidan

Yashiga yasanarda innah zaishigoda doctor tace to saida yashiga yasamu khadija kwance yagirgiza kansa sannan yafita"""

Yashigoda Abubakar din yagaida innah sanan sukashiga dakin "" yataba jikinta dazafi sosai sannan ya aunata"" haryagama abunda yakeyi muktar yana kallonsa

Yatashi tsaye yana kallon muktar yace me akaimata halan??? Muktar yace mefa akaimata doctor mekedamunta??? Yanisa yawan tunanine yahaifar mata da damuwa gakuma kirjinta yanazafii

Tunyaushe rabonta da abinci?? Jiki asanyaye yace jiya" yace mujeto asiyomata magani dole aimata allurar barci domin tasamu barci ko damuwar zataragu

Yace tomuje yayi maganar yana kallon khadijar taresukaje dashi akasiyo maganin da allurar yabiya sukaje inda masu fura damun injin yasiyamata suka wuce gida

Dakyar yasamu tasha furar sanann akaimata allurah takwanta yanunamasa yanda zatasha maganin idan tafarka yayimasa godiya yarakashi bakin motarsa sundade suna firah sannan yatafi hankalin muktar duk yana wajen khadija

Kodayakoma yasamu tayi barci kusa da itah yazauna yabuga tagumie yana kallonta"" wasu hawayene suka saukomasa yasadan yatsansa yataresu

Yana nan har akayi la asar yatafi masallaci yadawo yazauna ba itah tafarkaba saigoshin magrib yataimaka mata tawatsa ruwa tayi sallah taci abinci tasha maganie takoma takwanta

Sallamar labila sukajiyo tsakar gidan tagaida innah sannan tafada dakin tanakiran sahib bata rufe bakiba sukai ido hudu da muktar yasake tsuke fuskar nan

Itama saita dauke kanta tace inawuni bai amsaba itama batadamuba saman gadon tahau tace meyasameki sahiba???

Khadija saman kafarta tahau saitafashe dakuka nantake labila tafara kukan tace me akaimaki sahiba??? dan Allah kiyi shiru

Muktar yanazaune yanakallon ikon Allah"" innace taji kukan yayi yawa tashigo tozakufara sana ar takuba kuyiwa Allah kuyishiru

Kojinta basuyiba itama tsaye tayi tasaki baki kamardai yanda muktar yayi tsayin mintuna goma khadija tayi shiru saikuma takoma rarrashin labila sahiba kiyi shiru kinji kar zazzabi yakamaki

Saida tagama rarrashinta sannan tace inayan tafiya??? Da murmushi tayi maganar labila tace tunjiya naso inkawomaki da dare harzanfito sainaji raina abace nakoma daki nayita kuka jiya wlh banruntsaba zazzabi yarufeni

Yanzun Karin ruwama akaciremun tanunawa khadija hannunta tace inatashi nacewa hajiya kinzo tacemun ah ah shine nataso ingako lafiya

Khadija tasaki wani kayatacceñ murmushi tana kallon labila tace sahiba lafiyata qalau Nima rashin ganinkine yahaifarmuñ da damuwa Amman yanzu tunda naganki Alhamdulillah

Tace nima wlh sainaji nawarke taresuka sakarwa juna murmushii"" muktar yamike jin ansoma kiran sallah yafita baicedasu komaiba


Aransa yana tunanin wannan wace irin soyayya ce sukewa junansu aidole khadija tace tanason baban labila Kuma batai laifiba Amman anya nizan iyah barinta ta aureshi??? Nifa tsoron matan yanzu nakeyi dawan nan tunanin yatafi masallaci

Inna ma fita tayi domin tayi sallah suma sukayo alwala sukai sallah anan suka zauna sunata labari yawancin firarsu duk akan karatunsune na islamiyya har innah tagama abincin dare sukaci gabadayansu sunware tamkar basuyi ciwoba""
Muktar yadawo yasamesu suna tafirah yadade bakin kofar yana saurarensu basu ganshiba dan hankalinsu baya nan juyawa yayi yabar kofar dakin

Saikusan karfe Tara labila tayi gida saida sahiba tarakata sannan tadawo tanashigowa gidan tasha toka zuwa dakinta batajima dazamaba

Saiga muktar saman gadon yazauna yana kallonta yace sapna kenan wannan fushin duk ni akeyiwa ko??? Gashi kinware tunda kinga kawarki Amman tana tafiya kinkoma kina fushi

Dadago da sirarun hawayenta tace Yayana ciwona azuciyata yake bawai afuskaba nayi kokarin boye damuwa tane saboda labila muddin tasan inacikin damuwa zata matsane saina sanarda itah menene damuwata dakuma silar damuwar

Idanhar nasanarda itah Kaine kake fushidani wlh bazata sake kallonka da mutunciba"" ninasan labila batunyauba danhaka nake boye damuwata duk lokacinda muke tare

Yanisa yanzu khadija ninake fushidake??? Kodai kece kike fushidani"" hawayenda suke kan fuskarta suka karasa saukowa yace please nifa bakuka nace kiyimunba "" tace Yayana taya zanyi mushidakai Kaine ubana kuma Kaine uwata
Kasharemun hawayenda uwayena ne yakamata su shafemun banida wani babban farinciki aduniya Wanda yawuce inga nafaranta maka rai

Yayi murmushi khadija kenan aiyanzu banada wannan kimar tunda har nahanaki soyayya Amman kikayi dama bayada mata dadan sauki Amman khadija mai matafa kuma harya manyanta

Gyara zama tayi tana fuskantarsa tace Yayana duk da bansan dalilinka nafurta hakanba nasan kasan wannan baharamun bane

Shimai mata baza a aureshiba tosabodame??? Koshidin bamutum bane??? Kasani mata sun linka maza sosai idankowanne namiji mata daya zai aurah sauran matan kumafa wazai auresu???

Yayana idan kai aure nan gaba kana bukatar kari kaima saiwacce kakeso tace batasonka tunda kaima kanada mata"" shinzaka saki uwar yayankane saboda kanason Karin aure???

Idan kasaketa ka auri waccen kasake ra ayin karawani aurenfa??? Aganina mai mata bashida wata illarda za ace aurensa bazai yiyuba sai idan ansan shidin ba nagartaccen mutum bane tanisa banyimaka wannan maganarba waidan kabarni Na auri dadyn labila

Tundahar bakasonsa wlh nahakurah dashi zansanarda labila kayimun wani mijin kokuma inbika cen kagama bangantaba ballantana inji damuwa Amman Yayana nasan kanada dalilin fadin haka
Dan Allah kasanardani meye dalilinka


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
Chapter 68 · 0% Book details