← Book details Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 27 OF 121

chapter 30

Hatsabibin Boka Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

By
Gentle Lady💃🏽


Yanisa shikenan hajia zansanar da itah "" tace yauwa kokaifa ai boye boye bashida wani alfanu ansan kowa yanada kishi Amman hakuri zatayi ai tunda mijinta yanada bukatar kari

Yace zanfadamata insha Allah tace hakan yayi sunjima suna firah sannan sukai sallama yayi shiru yana kallon wayarsa shikam gabansa sai faduwa yakeyi

Mikewa yayi yasauko dakinsa"" hawayayi zuwa bangarenta cikin falo yasameta kwance remote ahannunta tana cenza tasha tana ganinsa tamike da fara a

Alhaji Kaine dakanka bayan kakirani inzo"" yayi murmushi bakomai aigani nazo yayi maganar yanasamun wajen zama kusa da itah

Yace hutawa akeyi"" tace ah wlh kafin majeed yadawo kasanshi akwai Rigima jiya da dare damuna yayi dakuka kamar karamin yaro

Yace todakumafa haryanzu bakimasa kaniba aidole yayi sakuwa dar taji agabanta Sam tama manta da anjuyemata mahaifa Kuma bazatayarda wani tsautsayi yasaka tasanarda Usman hakaba

Dantalurah sosai yana mutuwar son yara gashi biyune kawai da itah" yakatsemata shirun tahanyar kiran sunanta

Datago ta amsa cikin fara a"" yanisa dama akwai maganarda nakeson yidake"" tadanyi shiru sannan tagyara zamanta dandama kishingide take gahannun kujera

Takalleshi inajinka alhaji"" yadanyi jim sannan yace kafin nacekomai inamai baki hakuri akan abunda zanfurta maki nasan bazakiji dadiba Amman kiyi hakuri wlh nadade ina kumuiniyar maganar dantayi nauyi akan harshena

Yasake nisawa karkiyi zargin naraina kokarin da kikeyi akaina kodaya wlh najinjina maki hakaxalika ina alfahari dake

Karki zargeni dawani Abu Dan Allah wlh haryanzu inasonki sonda bantaba yiwa wata mace makamancinsaba aduniya

Lubcy dai tayi shiru tana saurarenshi haryakai karshe murmushi kawai takeyi yadago yakalleta murya araunane yace aure nakeson karawa kuma maganarda nakemaki harnasamu wacce zan aurah

Nakasa sanardake ne tuntunii"" nasan kinsanni kuma kinsan lalurarda nake dauke da itah bazan iyah rike kainaba nasoyin hakuri Amman nakasa doctor yasanar dani akallah zakifi shekara komafi kafin ayimaki aiki Dan likitocin dasuke wannan aikin sunakan wani aikine tayiyu sugama kafin nan kuma ka idar aikin saikinsha magani akallah nawata biyar sannan

Yasake kallonta idanuwansa sunkada jajir banaso na aikata zina abarda nakyamata tun ina saurayina yanxu dagirmana da Yayana bazanyiba dankuwa zansiyawa Yayana halaka dahannuna dankuwa duk abunda nayi nima sai anyimun

Nayi kokarin fara azumie amman duk dahaka nakasa Amman kiyi hakuri kinji matata yayi maganar yanariko hannunta ga mamakinsa saiyaga tatintsire da dariya

Bakisake yake kallonta tace wlh baban labila kasakani dariya yanzu akan wannan maganarne kakasa sanardani??

Tundazu kakeson fadar abudaya Amman kakama kwana kwana kawai kacemun aure zakayi zanhanakane??? Nasan mata sunada kishi Amman nisam banadashi kuma bawai Dan banasonka bane kodaya

Amman kasani dole inhar soyayya tacika soyayya kaso abunda masoyinka yaso kome kakeso aduniya komai muninsa gareni inhar kafurta kanaso tonima dole naso abun

Kaddarama abun bakine aguna inhar yazama fari awajenka nima yazama tuntuni nasobaka wannan shawarar tunda nidai banada jimirin dauke lalurarka kuma sainaga

Kamar zanyi shishshigi sainakama bakina Amman bakomai awajena kasaki ranka Allah yasanya Alkhairi tsuru yayi yanakallonta

Baisan sanda yarungumetaba yafara sunbatarta ganin yasoma fita hayyacinsa yasa tatureshi tace kamantane

Karamin Tsaki yaja yace wlh kamar namutu nakeji tanisa cikin alamar tausayi tace tomezaihana asabikin kusa kusa kozaka samu abunda kakeso

Yace ah sati biyu akasaka bakomai zancigaba dahakuri zuwa lokacin""" tatausaya masa matuka yace nagode sosai lubcy hakika ke Yar aljannace inama sauran mata zasuyi amfani da shawarata surika hakuri idan mijinsu zaikara aure

Dazasukoyi irin halayenki nakwarai da duniya tahaska"" murmushi tayi nidai kadaina zugani wannan zuzutawa haka

Dariya yayi aikin chan chantane"" yasake riko hannunta nagode sosai tace bakomai yasunan kanwar tawa??? Cikin nunajin nauyi yace suwaiba""😌 tace wow suna maidadi yakamata kafin akawota anunamun photo n kanwar tawa yadan Sosa kai yace bari nadauko wayata kigani Yar duma dumace kamarke

Yayi maganar yana mikewa tace bansaka wahalaba??? Yace kodaya daganan kobirnin sin kikaturani dakafa zanje saidai indade bandawoba tasa dariya ko maigidana ashedai kanaji dani ??? Yace kamar kwai kuwa yawuce

Tabi bayanshi damugun kallo yanafita taja wani dogon tsaki aranta tace wai aure???🙄 To ayi auren mugani ai wlh danabarka kakusanci wata matar amatsayin matarka nafiso kamutu

Inaruwana da lalurarka saidaifa kaje kayi zina komata Dari zakanema ni lubabatu bandamuba kazantarda bakaganiba tsabtace😏

Amman bazan taba yarda kakawo wata acikin gidan nanba Dan nawane danida Yayana"" bazantaba bari Yayana susamu yan ubaba

Karuwai ka ajedari awaje aidama akan abun zakayi aure nikuwa inamai tabbatàr maka bazaka samuba hmm namiji munafukiñe jiyanda yakewani lallaf yadauka salihar mace yakawo agidansa baisan kububuwa takeba cinnaka bakasan nagidaba zumanake maizaki ammankuma gaharbi harbinama yazarta Karin maciji dafii
Afili nake mumina Amman azuciyata nafikowa sharri jin motsin dawowarsa yasaka lubcy tadaidaita natsuwartà

Yashigo da sallama ta amsa"" kusa da itah yazauna yajawota jikinshi yakamo mata pic din tana kallo

Tace kai ammanfa kanwar nan tawa bakaramin kyaune da itaba"" yadan hararetà yaçe batakai kiba lubcy aranta tace kunji munafuki waya sàñima koharzagina kukeyi

Amman afili saitace ko??? Yace sosaima yanda kikasan kyawawan fure haka nakeganinki wai anyama wani yataba fadamàki kinada masifàr kyau?? Dariya tayi cikin nuna alamun jindadi tace ah ah Amman gashi aikai kana sanardañi


Aisha✍🏼
☠ *HATSABIBIN BOKA!!*☠
Chapter 27 · 0% Book details