Sashe 80
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Nasiha Aba ke yi mata, yana zaune ne saman kujera Khausar na zaune bakin katifar Aban
Du yadda Aba ya so kar ta yi kuka , shima kar ya yin sai gashi shine ya fara sada kansa yana mai fashewa da kukan da ba sauti
Ya Allah, Allah mai iko Allah mai amsa adu'ar bawansa
Ashe zai ga wannan rana?
Ashe zai ga auren Khausar dinsa? Auren da yake kyautatawa zaton ba hadi ne suka yi daga sama dan jin dadinsu ba? "Ya Allah alfarmar fiyayen halitta ka zaunar da y'ata a dakinta, ka kade duk wata fitina ka sa ta zamto mai biyayya wa mijinta" Aba ya fada bayan ya dago kansa yana kallonta
A rikice ta idasa fashewa da kukan itama ta sauko tana rarafowa har daf da kafar Aban ta dora kanta a hannunsa, kan da ya sha kitso , hannun da ya sha lalle , idannuwanta kawai aka sakawa kwali sai dan jan baki mai ruwan kasa dan a boye hasken jan lebenta wa kowani mutun ya zamto na mijinta ne shi shi kadai, a birkice ainun tana fitar da dadadan sanyayan kanshin lafayar dake jikinta da kuma kanshin fatar jikinta ta daban ta ce" Aba, Aba ba zan iya ba, Aba Ni babu inda zan je"
A tausashe sosai Abanta ya rike fuskarta yana murmushi ya ce" Dan ina kuka?"
Khausar ta gyada kai ta ce" dan kana kuka Abana na fasa auren !"
Abanta ya saki yar dariyar da bai shiryawa ba, a hankali ya ce" Kukan farin ciki nake yi, kukan jin dadi nake yi, kukan godiyar Allah nake yi, kin ga ai mun gama maganar rikicin kin fasa auren ko? Ai zaki je ki zauna mu gani ko?, Y'ar Aba, ki kasance mai biyayya, kar ki saki ki yadda tarbiyyar ki komai rintsi, ki sani ba wayonki ko dabarar ki ko rashin kunyar ki zata saka a so ki ba, ki kasance mai biyayya mai gaskiya mai addini da tsoron Allah, wannan shine zai ja gabanki har zuwa aljannah, kin ga tun dazu ina jin hayaniyar cewar motoci sun karaso , nima zan zo gidan ai kin ga ina zuwa wajen hajia ko? Zan zo gobe goben nan in sha Allah, kuma kin ga aikinki zaki ci gaba da tafiya ko? Share hawayen nan kar na gani kin ji?"
Khausar na sauke ajiyar zuciya mahaifinta na sake rarashinta a cen kofa kuwa motoci ne na mamaki suka zo daukan amarya wanda tun a nan kallo ya koma sama, shawo ya dau Giwa
Ba wasu motoci Masu yawa bane dan ba zasu wuce goma ba, ama a cikinsu aminai ne na kusa da kusan PROFESSEUR, a yau ya sauka a kasar dan zuwa daukan bestyn besty, wato kawar amini ce kuma aminiyar amini, shi kuma a yau yake da maganar hayata irin wace ya tanadar masu
A hankali ya yi murmushi ya kuma kashe kiran da ya shigo wayarsa na Professeur
A kalla kiran nan ya kai na hudu da yake masa idan ya daga sai ya yi shiru ya ki fadin komai
Lalle shi yake da godiyar yiwa baba da ya kasance uba jajirtacen da bai bar professeur summa a kan bege ba
Dan buga masa madubin da aka yi ana miko masa waya ya saka shi sake sakin murmushi a hankali ya karra a kunnansa yana janyo doguwar salama
A zuciyarsa ya amsa salamar ne? Ko baima amsa ba? Allah masani, abinda ya fada shine" Yaya na ga har tara zata yi shiru?"
Dariya Alhusain ya yi kasa kasa ya ce" Inspector an hanna mana Besty fa, wai sai gobe"
Shiru ya yi, irin shirun nan na daukewa gaba daya tamkar wanda ya ajiye wayar, a hankali ya furta" Baka iya ware abin wasa da wanda ba na wasa ba?"
Wannan karron Alhusain ya bushe da dariyar da ta saka TAUFEEK katse wayarsa ya sake yin kicin kicin ya zubawa Hajia ido wace ta ci uban bando sai kai kawo take yi ta tara tsofafin irinta a falo har wannan lokacin basu tafi ba wai amsar amarya zasu yi
Sai da suka yi ido hudu Hajia ta saki murmushi ta wani gyara tsayuwa ta ce" Kai wai wani kinibibin kake min a daka ne ? Ko auren dolen zaka kunce? Kawai ka kara gaba malan ka sa sai shigowa nake da salama Ni da dakina!, In dai Khausara ce a nan zata tare tunda auren dole na maka sai mai kwanoni ya san abin yi , aikin banza!"
Sshi dai bai tankata ba, har ta gama ta fice tana yade yaden habaici ta koma bangaren Mama, wace ke zaune a baban falon yau itama, itace zaune darr sai bakinta dake zaune tare da ita kowane cikin shiga ta alfarma an dafa abinci na alfarma an ci yanzun jiran saukar amarya ake yi dan a amsheta sai kowa ya kama gabansa, sai dai a taron nan kaf babu matan mai kwanoni da Yumnah, domin ita Yumnah tana cen dakinta ta rufe tana nata shagalin, vidio call da kawarta bayan ta gama waya da mahaifiyarta, du cikin kwontar mata da hankali suke yi, burinsu ta kwontar da hankalinta ta kuma fara aiwatar da abinda suka shirya tun a yau, dan babu abinda zai sa su yarda TAUFEEK da Khausar su zama abu daya!
Sai kusan tara da rabi motocin daukan amarya suka karaso
Mutunci irin na Hajia FUSAM tare take da kanwarta a rakiyar amarya , tana rike da wani mahaukacin turaren alfarma cikinsa fulawowi ne bayan nada nata lafayar da ta yi saman wando irin mai likewa a jikin nan da riga mai dogon hannu sai ta rufa mata alkyaba fara kall , ya zamto kanwar Mama rike da Khausar, su Rukaya sunna rike da wasu yan abubuwanta, Hajia Fusam na fesa turare a dukan tafiyarta, abin sai wanda ya gani daukaka Allah ya daukaka y'ar gidan Aba
A hannun Hajia aka damka KHAUSAR, bayan an dukar da ita ta gaishe da Hajiar
A nutse Hajiar ta bude alkyabar Khausar tana murmushi ta ce" Masha ALLAH khausara masha ALLAH"
A hankali Khausar ta fashe da kukan da take rikewa lebe har yana yi mata rawa a hankali ta dora kanta a cinyar Hajia wace ta kwashi salalami tana kallonta ta ce" Ke dan kaniya nan din ba gida bane? Ni kar ki sakani kuka bayan na dinka ba takashin kowa ba na buga daurin bando na rangada kwali abina kin ji ko?"
Mama ta saki murmushi, a hankali ta karaso daf da Hajiar ta zauna, a nutse ta saka hannunta ta dago Khausar ta saka tissu tana share hawayenta , da kula ainun ta ce" Ya isa haka mana, na san kukan ne kike ta yi tun safe ko? Tashi ku je ki huta, Allah ya maku albarka ya yiwa rayuwar aurenku albarka"
"Kai na Annabi yace amen!" Hajia ta fada tana kallon jama'ar dake daukan vidio ne, hoto ne, da masu amsa adu'ar, kai abu dai masha ALLAH, haka Hajia ta ja Khausar sauran na biye da ita suka karasa bangaren TAUFEEK kasa kasa tana fada mata magana kamar haka" ke yi shiru abinki, abinda an daina yayin kuka? Kuma yau din da na kawo ki nan dan gudun yan uba ne, gobe cen bangaren nawa zaki kaura fa kin ji ? Share hawayen kar ciwon kai ya hannaki rawar gaban hantsi!"
Da haka har suka karasa suka shigar da ita da addu'a aka haura da ita rantsatsen dakinta dake daf da na Yumnah aka zaunar da ita a gefen gadonta
Sosai danginta da yan rakiya suka yaba mutunci da karamcin ahalin mai kwanoni sannan suka tafi da addu'ar alkhairi suka bar Khausar na sauke ajiyar zuciya tana jin abin wani iri tamkar a mafarki
Ta dauki lokaci a zaunen nan har ta kage,
A hankali ta mike ta sauke alkyabar da aka naɗa mata ta nufi wajen madubin dakin mai girma wanda gabansa ke cike da tarin turaruka na alfarma kala kala ta ja ta tsaya tana kallon abin hannunta da su zoben da aka saka mata
A nutse ta sabule alkyabar gaba daya ta ninke ta ja kujerar ta ajiye sannan ta zubawa fuskarta ido har zuwa tsarin halitar da Allah ya yi mata
Da kunya ta kauda dubanta, dan a kulun takan ji kunyar kirarta sosai, bata son tsarewa kanta ido dan abin na bata kunya, bale yau da aka yi mata kwaliya irin ta mata masu aji sai ta zama tamkar ba ita ba
Wandon ne na ciki baki mai santsin nan da kama jiki wanda ke rike cinyoyi taf, sai farar rigar mai dogon hannu itama a jikin take, sai bakin dan kwalin da aka yiwa dauri irin na zara Buhari daurin da ya hau kan kitsonta das ya kawata fuskarta da dan wajen gefe da gefen nan na mata mai kyau ya yi mata luf masha ALLAH, du kuwa irin kukan da ta sha hakan sai bai boye tsararan kyan da ta zuba ba a yau
Idannuwanta ta rintse sakamakon jin karar bude kofar dakin gabanta na dokawa, dan ko wanene a yanzu ya shigo bata raba dayan biyu ko matar gidan ko mijin matar gidan ne
Ta madubi ta dan bude idannuwanta jin ba'a yi mata salama ba, kuma kamar an shigo ta zuba dubanta a kan fuskarsa
Da sauri ta dauke duban nata, hannayenta suka dan fara rawa
Gaba daya yau tamkar an karra masa cika ido da girma a idannuwanta
Shigarsa ta ɗinkin shada ne ruwan maroon , kansa dauke da hula
A tsayen da yake jinginuwa ne ya yi da garun dakin ya zuba mata ido da irin kallon nan da ba kyau ana yinsa wa mutun fa ai ko?
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃
Nasiha Aba ke yi mata, yana zaune ne saman kujera Khausar na zaune bakin katifar Aban
Du yadda Aba ya so kar ta yi kuka , shima kar ya yin sai gashi shine ya fara sada kansa yana mai fashewa da kukan da ba sauti
Ya Allah, Allah mai iko Allah mai amsa adu'ar bawansa
Ashe zai ga wannan rana?
Ashe zai ga auren Khausar dinsa? Auren da yake kyautatawa zaton ba hadi ne suka yi daga sama dan jin dadinsu ba? "Ya Allah alfarmar fiyayen halitta ka zaunar da y'ata a dakinta, ka kade duk wata fitina ka sa ta zamto mai biyayya wa mijinta" Aba ya fada bayan ya dago kansa yana kallonta
A rikice ta idasa fashewa da kukan itama ta sauko tana rarafowa har daf da kafar Aban ta dora kanta a hannunsa, kan da ya sha kitso , hannun da ya sha lalle , idannuwanta kawai aka sakawa kwali sai dan jan baki mai ruwan kasa dan a boye hasken jan lebenta wa kowani mutun ya zamto na mijinta ne shi shi kadai, a birkice ainun tana fitar da dadadan sanyayan kanshin lafayar dake jikinta da kuma kanshin fatar jikinta ta daban ta ce" Aba, Aba ba zan iya ba, Aba Ni babu inda zan je"
A tausashe sosai Abanta ya rike fuskarta yana murmushi ya ce" Dan ina kuka?"
Khausar ta gyada kai ta ce" dan kana kuka Abana na fasa auren !"
Abanta ya saki yar dariyar da bai shiryawa ba, a hankali ya ce" Kukan farin ciki nake yi, kukan jin dadi nake yi, kukan godiyar Allah nake yi, kin ga ai mun gama maganar rikicin kin fasa auren ko? Ai zaki je ki zauna mu gani ko?, Y'ar Aba, ki kasance mai biyayya, kar ki saki ki yadda tarbiyyar ki komai rintsi, ki sani ba wayonki ko dabarar ki ko rashin kunyar ki zata saka a so ki ba, ki kasance mai biyayya mai gaskiya mai addini da tsoron Allah, wannan shine zai ja gabanki har zuwa aljannah, kin ga tun dazu ina jin hayaniyar cewar motoci sun karaso , nima zan zo gidan ai kin ga ina zuwa wajen hajia ko? Zan zo gobe goben nan in sha Allah, kuma kin ga aikinki zaki ci gaba da tafiya ko? Share hawayen nan kar na gani kin ji?"
Khausar na sauke ajiyar zuciya mahaifinta na sake rarashinta a cen kofa kuwa motoci ne na mamaki suka zo daukan amarya wanda tun a nan kallo ya koma sama, shawo ya dau Giwa
Ba wasu motoci Masu yawa bane dan ba zasu wuce goma ba, ama a cikinsu aminai ne na kusa da kusan PROFESSEUR, a yau ya sauka a kasar dan zuwa daukan bestyn besty, wato kawar amini ce kuma aminiyar amini, shi kuma a yau yake da maganar hayata irin wace ya tanadar masu
A hankali ya yi murmushi ya kuma kashe kiran da ya shigo wayarsa na Professeur
A kalla kiran nan ya kai na hudu da yake masa idan ya daga sai ya yi shiru ya ki fadin komai
Lalle shi yake da godiyar yiwa baba da ya kasance uba jajirtacen da bai bar professeur summa a kan bege ba
Dan buga masa madubin da aka yi ana miko masa waya ya saka shi sake sakin murmushi a hankali ya karra a kunnansa yana janyo doguwar salama
A zuciyarsa ya amsa salamar ne? Ko baima amsa ba? Allah masani, abinda ya fada shine" Yaya na ga har tara zata yi shiru?"
Dariya Alhusain ya yi kasa kasa ya ce" Inspector an hanna mana Besty fa, wai sai gobe"
Shiru ya yi, irin shirun nan na daukewa gaba daya tamkar wanda ya ajiye wayar, a hankali ya furta" Baka iya ware abin wasa da wanda ba na wasa ba?"
Wannan karron Alhusain ya bushe da dariyar da ta saka TAUFEEK katse wayarsa ya sake yin kicin kicin ya zubawa Hajia ido wace ta ci uban bando sai kai kawo take yi ta tara tsofafin irinta a falo har wannan lokacin basu tafi ba wai amsar amarya zasu yi
Sai da suka yi ido hudu Hajia ta saki murmushi ta wani gyara tsayuwa ta ce" Kai wai wani kinibibin kake min a daka ne ? Ko auren dolen zaka kunce? Kawai ka kara gaba malan ka sa sai shigowa nake da salama Ni da dakina!, In dai Khausara ce a nan zata tare tunda auren dole na maka sai mai kwanoni ya san abin yi , aikin banza!"
Sshi dai bai tankata ba, har ta gama ta fice tana yade yaden habaici ta koma bangaren Mama, wace ke zaune a baban falon yau itama, itace zaune darr sai bakinta dake zaune tare da ita kowane cikin shiga ta alfarma an dafa abinci na alfarma an ci yanzun jiran saukar amarya ake yi dan a amsheta sai kowa ya kama gabansa, sai dai a taron nan kaf babu matan mai kwanoni da Yumnah, domin ita Yumnah tana cen dakinta ta rufe tana nata shagalin, vidio call da kawarta bayan ta gama waya da mahaifiyarta, du cikin kwontar mata da hankali suke yi, burinsu ta kwontar da hankalinta ta kuma fara aiwatar da abinda suka shirya tun a yau, dan babu abinda zai sa su yarda TAUFEEK da Khausar su zama abu daya!
Sai kusan tara da rabi motocin daukan amarya suka karaso
Mutunci irin na Hajia FUSAM tare take da kanwarta a rakiyar amarya , tana rike da wani mahaukacin turaren alfarma cikinsa fulawowi ne bayan nada nata lafayar da ta yi saman wando irin mai likewa a jikin nan da riga mai dogon hannu sai ta rufa mata alkyaba fara kall , ya zamto kanwar Mama rike da Khausar, su Rukaya sunna rike da wasu yan abubuwanta, Hajia Fusam na fesa turare a dukan tafiyarta, abin sai wanda ya gani daukaka Allah ya daukaka y'ar gidan Aba
A hannun Hajia aka damka KHAUSAR, bayan an dukar da ita ta gaishe da Hajiar
A nutse Hajiar ta bude alkyabar Khausar tana murmushi ta ce" Masha ALLAH khausara masha ALLAH"
A hankali Khausar ta fashe da kukan da take rikewa lebe har yana yi mata rawa a hankali ta dora kanta a cinyar Hajia wace ta kwashi salalami tana kallonta ta ce" Ke dan kaniya nan din ba gida bane? Ni kar ki sakani kuka bayan na dinka ba takashin kowa ba na buga daurin bando na rangada kwali abina kin ji ko?"
Mama ta saki murmushi, a hankali ta karaso daf da Hajiar ta zauna, a nutse ta saka hannunta ta dago Khausar ta saka tissu tana share hawayenta , da kula ainun ta ce" Ya isa haka mana, na san kukan ne kike ta yi tun safe ko? Tashi ku je ki huta, Allah ya maku albarka ya yiwa rayuwar aurenku albarka"
"Kai na Annabi yace amen!" Hajia ta fada tana kallon jama'ar dake daukan vidio ne, hoto ne, da masu amsa adu'ar, kai abu dai masha ALLAH, haka Hajia ta ja Khausar sauran na biye da ita suka karasa bangaren TAUFEEK kasa kasa tana fada mata magana kamar haka" ke yi shiru abinki, abinda an daina yayin kuka? Kuma yau din da na kawo ki nan dan gudun yan uba ne, gobe cen bangaren nawa zaki kaura fa kin ji ? Share hawayen kar ciwon kai ya hannaki rawar gaban hantsi!"
Da haka har suka karasa suka shigar da ita da addu'a aka haura da ita rantsatsen dakinta dake daf da na Yumnah aka zaunar da ita a gefen gadonta
Sosai danginta da yan rakiya suka yaba mutunci da karamcin ahalin mai kwanoni sannan suka tafi da addu'ar alkhairi suka bar Khausar na sauke ajiyar zuciya tana jin abin wani iri tamkar a mafarki
Ta dauki lokaci a zaunen nan har ta kage,
A hankali ta mike ta sauke alkyabar da aka naɗa mata ta nufi wajen madubin dakin mai girma wanda gabansa ke cike da tarin turaruka na alfarma kala kala ta ja ta tsaya tana kallon abin hannunta da su zoben da aka saka mata
A nutse ta sabule alkyabar gaba daya ta ninke ta ja kujerar ta ajiye sannan ta zubawa fuskarta ido har zuwa tsarin halitar da Allah ya yi mata
Da kunya ta kauda dubanta, dan a kulun takan ji kunyar kirarta sosai, bata son tsarewa kanta ido dan abin na bata kunya, bale yau da aka yi mata kwaliya irin ta mata masu aji sai ta zama tamkar ba ita ba
Wandon ne na ciki baki mai santsin nan da kama jiki wanda ke rike cinyoyi taf, sai farar rigar mai dogon hannu itama a jikin take, sai bakin dan kwalin da aka yiwa dauri irin na zara Buhari daurin da ya hau kan kitsonta das ya kawata fuskarta da dan wajen gefe da gefen nan na mata mai kyau ya yi mata luf masha ALLAH, du kuwa irin kukan da ta sha hakan sai bai boye tsararan kyan da ta zuba ba a yau
Idannuwanta ta rintse sakamakon jin karar bude kofar dakin gabanta na dokawa, dan ko wanene a yanzu ya shigo bata raba dayan biyu ko matar gidan ko mijin matar gidan ne
Ta madubi ta dan bude idannuwanta jin ba'a yi mata salama ba, kuma kamar an shigo ta zuba dubanta a kan fuskarsa
Da sauri ta dauke duban nata, hannayenta suka dan fara rawa
Gaba daya yau tamkar an karra masa cika ido da girma a idannuwanta
Shigarsa ta ɗinkin shada ne ruwan maroon , kansa dauke da hula
A tsayen da yake jinginuwa ne ya yi da garun dakin ya zuba mata ido da irin kallon nan da ba kyau ana yinsa wa mutun fa ai ko?