Sashe 37
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da ta fito bata ga Aba ba, a dole ta karasa wajen motar ta bude baya ta shiga dan Hajiar da TAUFEEK ne a gaba, Yumnah kuwa a baya
Dan murmushi ta so sakarwa Yumnah, sai ta ga gaba daya ba bangarenta take kallo ba
A hankali ya dan saita madubin motar ya kalli fuskarta, ba dan komai ba sai dan ya ga shin zata iya zuwa gidansu ta kwana da son ranta ko karfa karfa hajia ke son yi mata
Yannayinta bai kare shi da komai ba sai karin wani tunanin da damuwa, dan kasa take kallo da dara daran idannuwan nan nata sai busasun hawaye da suka kwonta a saman kumatunta
A nutse ya tuka su har suka karasa gidan
Sunna zuwa Hajia ta bude , sannan ta bude bayan ta janyo hannun KHausar tana fadin" Mu je , yi maza ba fara saka ki a ruwan kaka ka yi ka fito, sai an samo maki ki bugo wannan hawaye haka, ina ba zai yiwu ba!"
Da ido suka bi su har Hajiar ta shige bangaren su Maman TAUFEEK, wa ya san me zata yi a cen din
Motar ya rufe ya zagaya inda hajia ta bara masa jakar shi dan aikenta ya ciro jakar sannan ya rufe da nufin mika masu jakar
Da sauri Yumnah ta riko hannunsa, hakan ya sa ya juyo yana kallonta da dan mamaki, domin a sanninsa rabonta da ta kai hannunta da kanta jikinsa tun wayewar garin nan kafin komai ya shiga tsakaninsu
Fuskarta a marairaice sosai ta ce" Ama, ina zaka je ne?"
Dan tsai ya yi yana kallonta, ya san a yanzun kamar ba wata jituwa tsakaninta da Khausar, dan haka a hankali ya ce" Jakar zan ajiye masu"
Jakar ta kalla, da sauri ta miko hannayenta ta ce" Aa gani kuma zaka kai, kawo na je na kai masu ka shige ciki na dawo na zuba mana abinci ka ji yayanmu?"
Bai kawo komai ransa ba ya bara mata jakar, duda ya so ya dan zanta da Khausar sai dai ya san abu ne da kamar wuya dan a yadda hajia ta yi raf da ita din cen da wahala ta saketa
Ciki ya shige, ita kuma ta ja tsaki ta riko jakar kamar ta rike kashi ta kai cen bangaren hajiar ta yar da jakar a kofar falon Hajia sannan ta juya ta yi tafiyarta, dan ita tunda ta zo gidan nan kafarta bata taba shiga bama cikin falon Hajia saboda karara ta gane ba wani sonta take yi ba, ba zata ringa kai kanta inda ba'a sonta ba gaskiya, haka ta koma ranta cike da jin zafin hajiar na wannan sabuwar fitinar, a kan wani dalili zata dauko katuwar mace tana wani kama kumatunta tana share mata hawaye tana masifar da bata san dalili ba ta kawo mata gida inda mijinta ke nan? Bi izinillah daidai take da uban kowa a kan TAUFEEK, ta gama yarda cewa ya isa ta yi kuma idan ta yin ba laifi ta yi ba shi yasa ta sake daukar damarar bashi dukkan kulawar da ta dace, ciki kuwa harda mayar da shi baban waje du kuwa da tsoron da take , zata bashi hadin kai dari bisa dari ta yadda zai manta da wata jibgaga abin haushi gidan tsami kawai!
A bangaren Khausar kuwa ta ga abin mamaki gannin idonta
Wanka dai mai sunnan wanka sai da Hajia ta sakata ta yi sau uku na magunguna Maman TAUFEEK na tsaye tana rike da kwaryar, Hajiar kuwa tana hadawa tana bata tana fadin idan fa bata yi ba shiga zaki yi ki darzar min ita dan na kula shashanci na damun yar nan banza sai sakin hawaye take ta ki fada min ubanda ya daketa, danma na san shi Magidanci ba zai daketa ba ai da tuni na samu mai kwanoni a waya ya min tsakani da shi, har ga Allah yar nan ta gama sacen zuciyata sai yadda hali ya yi kuma, ji nake uwa in janyo nesa ta zo kusa in samo mata gagarumi rikaken dan arziki ya kwasheta mu tafi"
Ita dai Mama tana tsaye har ta gama ta fito da katon hijabi nan kuma aka kuma saka mata kaskon hayaki
Khausar kifta ido kawai take tana kallon Mama dake murmushin hajia tana fadan Magidanci yau bai zo ya yi hayaki ba yana cen shi mai mata abu kamar a karye ana fama da katon hanci da feleke da waya ƙatuwa
Kai magidanci ya dauko da zafi mace ba mamora da ramin kashi
Ana gama mata turaren Hajia ta wuce cikin kicin wai zata zubo mata abinci, nan Mama ta zauna bayan ta ciro mata kaya cikin kayanta tana kallonsu da kula ta ce" Daughter me yake damunki ne? Hajia sai fadi take kina kuka?"
Khausar ta sada kanta a hankali ta girgiza kanta ta ce" Mama, ba komai fa, kawai dai abin bama wani bane Hajia dai ta yi tunanin ko wani ne ya sakani kukan"
Mama ta yi murmushi tana sake kallon Atampar, sam atampar bata wani yi mata ba, ama kumaa bata nuna ba ta bar abinta a ranta da kudurin dake ranta ta ce" Ai kam kema kin ji jiki tunda Hajiata ke kaunarki, ke da Magidancin zaku ji jiki iya jin jiki"
Dariya Khausar ta yi itama kadan tana amsar atamparta ta mike ta shige ciki ta saka tana ta jan rigar gannin tana neman fado mata , gaba daya rigar ta mata yawa yanzun bayan a da har da kyar take numfashi a cikinta, zanin dai ne daidai ta daura ta sake zumbulo hijabinta ta fito
Tana shirin zama Hajia ta watsa mata harara taa ce" Ke dilla cire hijabin, haka fa take yawo yadda kika san yar aike da hijabin nan,, ba dole a yi shiru ba wannan zamani da ya zama na dan kyale kyali, ni hijabinma haushi yake bani in ba dan kar a min wata fasara ba sai nace ina dalili ne wai? Cire ko sai na tashi?"
Mama ta zarro ido tana kallon Hajia da kokarinta, Khausar kuwa ta cire din ama kuma ta kasa ajiyewa bale ta zauna, bama kamar yadda kitsonta ya tsufa kuma kan ba hula, ga yadda rigar ta mata sai a hankali
Da ido Hajia ke nunawa Mama bayan Khausar, Mama kuwa ta ki kallo kawai ta cije abinta dan Allah kadai ya san dariyar dake cinye mata zuciya na lamarin Hajia, haka kawai ki dauko yar a gaban iyayenta kice basa sonta ke zaki kulata? Ga yarinya mai kunya sai sinne kai take ama Hajia ta ki fahimta, karshe dai haka ta sa Khausar cin abincin nan sosai sannan ta sakkata shiga daki ta kwonta suka ci gaba da tataunawa da Mama kafin ta mike ta koma itama
Tana shiga falonsu ta samu abokiyar zamanta zaune tana fira a waya
Da hannu ta gaisheta ta shige ciki dan ta ga tana waya, ita kuwa ta rakata da matsiyacin kall9, duda tsohon cikin dake jikinta bata rasa fitintinnu a tare da ita, a rayuwa taren Hajia mahaifiyar mijinsu da matar mijin nasu uwar TAUFEEK na matukar ci masu tuwo a kwarya, hajiar nan basu taba gannin fitinaniya irinta ba, gashi idan bata yinka bata yinka ne babu wanda zai sakata ta yika dan dole ko waye shi, shi yasa lokuta da dama su da ita a je a gaisheta ne a tashi dan idan ka zauna yanzu wani abin zai faru ta balo maka ruwa, sun yi sun yi su lalata taren nan abin ya faskara, ko yanzu da ta zo ta jata suka wuce ya sa dayar mikewa ta shige dan haushi, ita ta zauna dan so take ta ga abinda aka yi
___________________________________
"Idan baki saka pankeken nan ba babu inda zaki je Khausara, kin ji dan uwan rahamanu babu inda zaki je, yau ga aikin banza aikin wofi, hakaa kike son fita ki je wajen aikin? Ai ba kabari za'a saka ki ba, kina abu kamar wata ni? Ko ni kajal nake radawa in fuske bale ke yarinya danya shirat budurci a leda!" Ta ajiye maganar tana sake gogo mata hodar da ta je wajen yan matan gidan ta amso da kwali da jan baki wai aro kafin a jima ta je kasuwa ta siyowa Khausara pankeke
A tsaye yake a kofar dakin, cikin shiga ta kayan aiki , ama babu abinda zai iya ce maka ga aikin
Kanshi yake fitarwa ta ko'ina, hannunsa dauke da agogon dake nuna masa takwas ta kusa , gashi a tsaye ya kasa shuga saboda Bakin hajia da kalaman da take fada tun dazun sai yake ganninsu da jinsu wani iri
Turare ne Hajia ta rike kuuuuuuu tana fesa mata , sai kuna ta dauko wanda ta zo da shi nata ne da ta siya wajen HAJIA FUSAM mai turaren yan gayu ta bude shima ta yi mata feshin albarka dan sai da dakin ya dauki kanshin gaba daya sannan ta rufe tana fadin" Yauwa ko ke fa, ga farar rigar ga kuma dan karamin hijabin, ki je ki dawo mi je wajen tela Allah ya tsare bara na ba direba abincinki"
Daga daga nan Hajiar ta wuce da kwondon da ta zuba mata abinci lafiyaye ta bi ta kicin
Ajiyar zuciya ya sauke ya girgiza kai sannan ya daga labulen da niyar ce nata ta zo su gudu kafin hajia ta dawo ta hadasa masa ciwon barin kai
Hankali ya zuba mata ido, Atampa ce a jikinta mai haske, dinkin doguwar riga ne wanda ya dan mata yawa daga wajen tumbi dan zazagewar da tumbin ke yi ama kuma ya rike cinyoyinta tak dan kamar nan jikin ya karra komawa, sai dan madaidaicin hijab din da Hajiar tace shi zata saka ta yi tsuru tana tunanin halin da take iya shiga idan ta fita a haka domin ta san babu inda zata iya zuwa
Dan murmushi ta so sakarwa Yumnah, sai ta ga gaba daya ba bangarenta take kallo ba
A hankali ya dan saita madubin motar ya kalli fuskarta, ba dan komai ba sai dan ya ga shin zata iya zuwa gidansu ta kwana da son ranta ko karfa karfa hajia ke son yi mata
Yannayinta bai kare shi da komai ba sai karin wani tunanin da damuwa, dan kasa take kallo da dara daran idannuwan nan nata sai busasun hawaye da suka kwonta a saman kumatunta
A nutse ya tuka su har suka karasa gidan
Sunna zuwa Hajia ta bude , sannan ta bude bayan ta janyo hannun KHausar tana fadin" Mu je , yi maza ba fara saka ki a ruwan kaka ka yi ka fito, sai an samo maki ki bugo wannan hawaye haka, ina ba zai yiwu ba!"
Da ido suka bi su har Hajiar ta shige bangaren su Maman TAUFEEK, wa ya san me zata yi a cen din
Motar ya rufe ya zagaya inda hajia ta bara masa jakar shi dan aikenta ya ciro jakar sannan ya rufe da nufin mika masu jakar
Da sauri Yumnah ta riko hannunsa, hakan ya sa ya juyo yana kallonta da dan mamaki, domin a sanninsa rabonta da ta kai hannunta da kanta jikinsa tun wayewar garin nan kafin komai ya shiga tsakaninsu
Fuskarta a marairaice sosai ta ce" Ama, ina zaka je ne?"
Dan tsai ya yi yana kallonta, ya san a yanzun kamar ba wata jituwa tsakaninta da Khausar, dan haka a hankali ya ce" Jakar zan ajiye masu"
Jakar ta kalla, da sauri ta miko hannayenta ta ce" Aa gani kuma zaka kai, kawo na je na kai masu ka shige ciki na dawo na zuba mana abinci ka ji yayanmu?"
Bai kawo komai ransa ba ya bara mata jakar, duda ya so ya dan zanta da Khausar sai dai ya san abu ne da kamar wuya dan a yadda hajia ta yi raf da ita din cen da wahala ta saketa
Ciki ya shige, ita kuma ta ja tsaki ta riko jakar kamar ta rike kashi ta kai cen bangaren hajiar ta yar da jakar a kofar falon Hajia sannan ta juya ta yi tafiyarta, dan ita tunda ta zo gidan nan kafarta bata taba shiga bama cikin falon Hajia saboda karara ta gane ba wani sonta take yi ba, ba zata ringa kai kanta inda ba'a sonta ba gaskiya, haka ta koma ranta cike da jin zafin hajiar na wannan sabuwar fitinar, a kan wani dalili zata dauko katuwar mace tana wani kama kumatunta tana share mata hawaye tana masifar da bata san dalili ba ta kawo mata gida inda mijinta ke nan? Bi izinillah daidai take da uban kowa a kan TAUFEEK, ta gama yarda cewa ya isa ta yi kuma idan ta yin ba laifi ta yi ba shi yasa ta sake daukar damarar bashi dukkan kulawar da ta dace, ciki kuwa harda mayar da shi baban waje du kuwa da tsoron da take , zata bashi hadin kai dari bisa dari ta yadda zai manta da wata jibgaga abin haushi gidan tsami kawai!
A bangaren Khausar kuwa ta ga abin mamaki gannin idonta
Wanka dai mai sunnan wanka sai da Hajia ta sakata ta yi sau uku na magunguna Maman TAUFEEK na tsaye tana rike da kwaryar, Hajiar kuwa tana hadawa tana bata tana fadin idan fa bata yi ba shiga zaki yi ki darzar min ita dan na kula shashanci na damun yar nan banza sai sakin hawaye take ta ki fada min ubanda ya daketa, danma na san shi Magidanci ba zai daketa ba ai da tuni na samu mai kwanoni a waya ya min tsakani da shi, har ga Allah yar nan ta gama sacen zuciyata sai yadda hali ya yi kuma, ji nake uwa in janyo nesa ta zo kusa in samo mata gagarumi rikaken dan arziki ya kwasheta mu tafi"
Ita dai Mama tana tsaye har ta gama ta fito da katon hijabi nan kuma aka kuma saka mata kaskon hayaki
Khausar kifta ido kawai take tana kallon Mama dake murmushin hajia tana fadan Magidanci yau bai zo ya yi hayaki ba yana cen shi mai mata abu kamar a karye ana fama da katon hanci da feleke da waya ƙatuwa
Kai magidanci ya dauko da zafi mace ba mamora da ramin kashi
Ana gama mata turaren Hajia ta wuce cikin kicin wai zata zubo mata abinci, nan Mama ta zauna bayan ta ciro mata kaya cikin kayanta tana kallonsu da kula ta ce" Daughter me yake damunki ne? Hajia sai fadi take kina kuka?"
Khausar ta sada kanta a hankali ta girgiza kanta ta ce" Mama, ba komai fa, kawai dai abin bama wani bane Hajia dai ta yi tunanin ko wani ne ya sakani kukan"
Mama ta yi murmushi tana sake kallon Atampar, sam atampar bata wani yi mata ba, ama kumaa bata nuna ba ta bar abinta a ranta da kudurin dake ranta ta ce" Ai kam kema kin ji jiki tunda Hajiata ke kaunarki, ke da Magidancin zaku ji jiki iya jin jiki"
Dariya Khausar ta yi itama kadan tana amsar atamparta ta mike ta shige ciki ta saka tana ta jan rigar gannin tana neman fado mata , gaba daya rigar ta mata yawa yanzun bayan a da har da kyar take numfashi a cikinta, zanin dai ne daidai ta daura ta sake zumbulo hijabinta ta fito
Tana shirin zama Hajia ta watsa mata harara taa ce" Ke dilla cire hijabin, haka fa take yawo yadda kika san yar aike da hijabin nan,, ba dole a yi shiru ba wannan zamani da ya zama na dan kyale kyali, ni hijabinma haushi yake bani in ba dan kar a min wata fasara ba sai nace ina dalili ne wai? Cire ko sai na tashi?"
Mama ta zarro ido tana kallon Hajia da kokarinta, Khausar kuwa ta cire din ama kuma ta kasa ajiyewa bale ta zauna, bama kamar yadda kitsonta ya tsufa kuma kan ba hula, ga yadda rigar ta mata sai a hankali
Da ido Hajia ke nunawa Mama bayan Khausar, Mama kuwa ta ki kallo kawai ta cije abinta dan Allah kadai ya san dariyar dake cinye mata zuciya na lamarin Hajia, haka kawai ki dauko yar a gaban iyayenta kice basa sonta ke zaki kulata? Ga yarinya mai kunya sai sinne kai take ama Hajia ta ki fahimta, karshe dai haka ta sa Khausar cin abincin nan sosai sannan ta sakkata shiga daki ta kwonta suka ci gaba da tataunawa da Mama kafin ta mike ta koma itama
Tana shiga falonsu ta samu abokiyar zamanta zaune tana fira a waya
Da hannu ta gaisheta ta shige ciki dan ta ga tana waya, ita kuwa ta rakata da matsiyacin kall9, duda tsohon cikin dake jikinta bata rasa fitintinnu a tare da ita, a rayuwa taren Hajia mahaifiyar mijinsu da matar mijin nasu uwar TAUFEEK na matukar ci masu tuwo a kwarya, hajiar nan basu taba gannin fitinaniya irinta ba, gashi idan bata yinka bata yinka ne babu wanda zai sakata ta yika dan dole ko waye shi, shi yasa lokuta da dama su da ita a je a gaisheta ne a tashi dan idan ka zauna yanzu wani abin zai faru ta balo maka ruwa, sun yi sun yi su lalata taren nan abin ya faskara, ko yanzu da ta zo ta jata suka wuce ya sa dayar mikewa ta shige dan haushi, ita ta zauna dan so take ta ga abinda aka yi
___________________________________
"Idan baki saka pankeken nan ba babu inda zaki je Khausara, kin ji dan uwan rahamanu babu inda zaki je, yau ga aikin banza aikin wofi, hakaa kike son fita ki je wajen aikin? Ai ba kabari za'a saka ki ba, kina abu kamar wata ni? Ko ni kajal nake radawa in fuske bale ke yarinya danya shirat budurci a leda!" Ta ajiye maganar tana sake gogo mata hodar da ta je wajen yan matan gidan ta amso da kwali da jan baki wai aro kafin a jima ta je kasuwa ta siyowa Khausara pankeke
A tsaye yake a kofar dakin, cikin shiga ta kayan aiki , ama babu abinda zai iya ce maka ga aikin
Kanshi yake fitarwa ta ko'ina, hannunsa dauke da agogon dake nuna masa takwas ta kusa , gashi a tsaye ya kasa shuga saboda Bakin hajia da kalaman da take fada tun dazun sai yake ganninsu da jinsu wani iri
Turare ne Hajia ta rike kuuuuuuu tana fesa mata , sai kuna ta dauko wanda ta zo da shi nata ne da ta siya wajen HAJIA FUSAM mai turaren yan gayu ta bude shima ta yi mata feshin albarka dan sai da dakin ya dauki kanshin gaba daya sannan ta rufe tana fadin" Yauwa ko ke fa, ga farar rigar ga kuma dan karamin hijabin, ki je ki dawo mi je wajen tela Allah ya tsare bara na ba direba abincinki"
Daga daga nan Hajiar ta wuce da kwondon da ta zuba mata abinci lafiyaye ta bi ta kicin
Ajiyar zuciya ya sauke ya girgiza kai sannan ya daga labulen da niyar ce nata ta zo su gudu kafin hajia ta dawo ta hadasa masa ciwon barin kai
Hankali ya zuba mata ido, Atampa ce a jikinta mai haske, dinkin doguwar riga ne wanda ya dan mata yawa daga wajen tumbi dan zazagewar da tumbin ke yi ama kuma ya rike cinyoyinta tak dan kamar nan jikin ya karra komawa, sai dan madaidaicin hijab din da Hajiar tace shi zata saka ta yi tsuru tana tunanin halin da take iya shiga idan ta fita a haka domin ta san babu inda zata iya zuwa