Sashe 39
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata ce komai ba, sai dai a zuciyarta ta ji dadin hakan dan ita kadai ta san irin kewar ahalinta da take yi, komai dadin gidan wasu gwara naka, dan a jiya an mata gata iya gata an hadata da wani luntsumemen gado da ac, ama zuciyarta sai ta ringa kwadayin inama ta samu yar katifarta da motsin ahalinta a kusa da ita? Dandai bata da yada zata yi da Hajia ne , kuma ko ba komai dan matsawar daga gidan ya taimaketa ainun dan ta samu zuciyarta ta dan saku da irin aibatatan da mutane suka ringa yi
"Karfe bakwai zan dawo na daukeki na maidama matar cen ke " ya fada a hankali bayan ya tsaya a kofar gidan
Murmushi ta yi ta bude motar ta fice da kwondon abincin dan a juyewa busashe ta wanke flsk din da aka zuba
Sosai suka sha fira da Mama, Mama bata yi mata fadan da ta yi tunanin zata yi mata ba, saima rarashi da ta samu na ban mamaki da kuma ban baki
Da kula Mama ta ce" Komai da kika gani na rayuwa mukadari ne, ban ce maki takurarwar mutane ba zata dameki ba dan kuwa hakan na iya damunki fiye da tunanin bawa, ama abinda na sani shine mu iyayenki zamu ci gaba da binki da addu'a har Allah ya fitar maki da miji na gari, Khausar a jiya Mujaheed ya zo da dare nema sosai , Abanku ya fita ya same shi, shin akoy wata matsala tsakaninki da shi ne da ban sani ba?"
Khausar ta yi dan shiru gabanta na dan faduwa, a sanyaye ta girgizawa Mama kai
Mama ta tabe baki ta ce" Kin san mahaifinki bai cika buden abu ba, a yadda dai na dan tsinci abin kamar ya fara kokonta a kan tarenku da mutumen , harma ya bashi damar ya fito idan da gaske yake, in ba haka ba kuwa ya yi hakuri kawai, ...........hakan ya sa na tsatsamci akoy abinda yake faruwa da baya birge abanku"
Khausar ta yi tsuru gabanta na faduwa zuciyarta cike da tunanin ko wani abu ne ya faru?
Mama ta ce" To ki kula, kafin komai mutuncinki ya fi komai a duniya, ki sani idan da rabon ki yi aure ko shekara nawa zaki dauka a duniya sunnanki mace , budurwa, kar ki yarda ko menene ya taba maki mutunci , kuma ko wani irin hargitsi ya tunkaro rayuwarki ki san cewa Allah ya haliceki shi ya dora maki ba kowa ba, ....., Sai maganar auren kannenki, a jiya fa iyayen wajen mijin rukaya sun nuna da wuri suke so, dan a cewarsu sati biyu, da kyar dai abanku ya tsaida abin nan da wata daya, kennan dole mu zauna mu yi shawara mu ga abinda zai fishemu ko?"
Da mamaki ta ce" Ka8, da wuri haka Mama, na zatama sa kai bayan babar sallah?"
Mama ta ce" Nima na zaci hakan, ama kin ga yadda Allah ya yi"
Khausar ta yi murmushi ta yi addu'ar Allah ya nuna masu ranar da rai da lafiya
Nan suka hade suka yi ta zantawa har baba ya dawo gida shima ya hadu da su ya ringa tsokanar Khausar yar gidan Hajia ya ce" Kin ga, TAUFEEK ya zo ya maidawa Hajia ke tun kafin ta tardoni tace ni na kwaceki"
Dariya Mama ke yi ta kama baki ta ce" Ni ai jiya na sha dariya Ni kadai, Hajia fa hararena take yi wai ban san ciwon Khausar ba"
Aba ya ce" Nima cewa ta yi ba sannin ciwon yar aka yi ba"
Nan fa aka dauko caftar Hajia, Khausar ta ringa dariya dan walahi sai yanzu ta idasa sakewa har ta ji wasai a ranta, ta fada masu turaren da hajiar ta mata jiya da yau da safe, ai kam kannenta da iyayenta aka rasa mai ba dan uwansa hakuri dariya suke bilhaki, Aisha ta ce" Ni walahi tsoronta nake ji, idan tana fadan nan sai na ji kamar zata iya marina, kuma ita babu wanda ta bari, harta yaya TAUFEEK fa sai ku ji ta yanko shi , shi kuwa abin mamaki idan ya zura ido ya kalleta sai ka ga ya dauke kansa kamar Allah bai yi ruwanta ba, sam baya kulata"
KHausar ta ce" Ke na rabaki da TAUFEEK, shi ai du lokacin da kake shirye ku yi balaki ne na zai biyaka ba, ki ga fa idan ina fushi da shi na yi na yi ya biye min sai kawai ya kare min kall9 ya dauke kai, ni kuwa hakan irin haushin da yake bani, sai in ga a banza kennan ban samu muka raba hali ba"
Mama na dariya ta ce" To ai shi ba mashiririci bane da zai tsaya karamar yarinya ta fada ya fada"
Haka suka yi ta sharfi sunna fara'a, a hankali kuma mutane na lekowa sunna sake yin barka da arziki da fatan Allah ya nuna masu ranar auren
Zuwan TAUFEEK ya saka suka mike sukai mata rakiya, su uku, Aisha , Rukaya, da Auta har wajen motar
A lokacin da ta bude ta shige a gaban idannuwanta yan zaman anguwar suke lekowa, ita kuwa ta cire kanta bata kula kowa ba ta shiga neman layin Mujaheed
Sai da suka kusa isa gidan ya daga wayar, cikin dan basarwa ya ce" Batan numba aka yi ba?"
Khausar ta yi dan murmushi a hankali ta ce" Barka da warhaka Elhaji"
Elhaji Mujaheed ya amsata shima da kula
Khausar ta ce" sai yanzu na ga misscall dinka, shine nace ko zaka iya zuwa nan gidan su TAUFEEK da yake a nan zan kwana? Idan har dare bai yi ba?"
TAUFEEK dake tuki yana amsa waya ya dan kalleta kadan, sai kuma ya dauke kansa ya ci gaba da tukin
Bai dai san me suka tatauna ba har suka karaso gida dan shi bai gama tasa wayar ba har sai da suka iso ya fice yana amsa wayar, ita kuma ta ciro kwanukan ta nufi bangaren Hajia da su
Samu ta yi Hajiar bata nan, mai aikinta ta shaida mata tana bangaren su Mama, dan haka sai kawai ta shige bayi ta yi wanka ta fito ta cenza kayanta sannan ta zauna ta hada lipton mai zafi ta shiga sha a hankali tana dan duba agogo domin Elhaji Mujaheed yace ta bashi minti ashirin gayanan zuwa
A lokacin da ya sanar mata yana cen babar kofa bai samu shigowa ba a dole ta mike ta shiga neman layin TAUFEEK, sai dai ta yi ta yi bai daga ba, gashi hajia bata dawo ba, abindama ya dan sakata kin bin hajiar da kuma kin zuwa ta gaisar da su mai aikin na hajiar cewa ta yi an zo an yi kiran hajiar ana fada a cen, hakan ya sa ta yi zamanta dan ba zata je kotai kotai bayan ta ji abinda aka fada ba
Hijab ta saka ta Hajia dan ta nemi nata sama ko kasa ta rasa, da dan sauri ta nufi bangaren TAUFEEK tana sake gwada kiransa ama abin haushi ba'a daga ba
A nutse ta dan buga kofar sannan ta kama ta murda da salama a bakinta
Fara'a ce ta yawaita a fuskarta tana kallon Yumnah dake tsaye wajen diner, jikinta daure da rigar girki, hannayenta da safar sauke tukwane, tana sanye da wando da riga , wandon da kadan ya dan dara gwuiwarta , rigar kuwa mai siririn hannu ta juyo ta zubawa Khausar din ido ama kuma bata amsa salamar da ta mata ba
A hankali Khausar ta dan dauke dubanta gannin yannayin shigar Yumnar tana dan murmushi ta ce" Matarmu, barka da dare, dan Allah ki yi hakuri na dame ki, ko freind na kusa?"
Yumnah ta kare mata kallo, ta dago ta watsar sannan ta juya ta ci gaba da gyaran diner dinta ba tare da ta abata amsa ba
Da dan mamaki Khausar ta dan juyo dan gannin ko dai bata bata jita bane??
*ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA*
Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu.
Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu.
Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda.
Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter.
Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba.
Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726
Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 2️⃣3️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
"Karfe bakwai zan dawo na daukeki na maidama matar cen ke " ya fada a hankali bayan ya tsaya a kofar gidan
Murmushi ta yi ta bude motar ta fice da kwondon abincin dan a juyewa busashe ta wanke flsk din da aka zuba
Sosai suka sha fira da Mama, Mama bata yi mata fadan da ta yi tunanin zata yi mata ba, saima rarashi da ta samu na ban mamaki da kuma ban baki
Da kula Mama ta ce" Komai da kika gani na rayuwa mukadari ne, ban ce maki takurarwar mutane ba zata dameki ba dan kuwa hakan na iya damunki fiye da tunanin bawa, ama abinda na sani shine mu iyayenki zamu ci gaba da binki da addu'a har Allah ya fitar maki da miji na gari, Khausar a jiya Mujaheed ya zo da dare nema sosai , Abanku ya fita ya same shi, shin akoy wata matsala tsakaninki da shi ne da ban sani ba?"
Khausar ta yi dan shiru gabanta na dan faduwa, a sanyaye ta girgizawa Mama kai
Mama ta tabe baki ta ce" Kin san mahaifinki bai cika buden abu ba, a yadda dai na dan tsinci abin kamar ya fara kokonta a kan tarenku da mutumen , harma ya bashi damar ya fito idan da gaske yake, in ba haka ba kuwa ya yi hakuri kawai, ...........hakan ya sa na tsatsamci akoy abinda yake faruwa da baya birge abanku"
Khausar ta yi tsuru gabanta na faduwa zuciyarta cike da tunanin ko wani abu ne ya faru?
Mama ta ce" To ki kula, kafin komai mutuncinki ya fi komai a duniya, ki sani idan da rabon ki yi aure ko shekara nawa zaki dauka a duniya sunnanki mace , budurwa, kar ki yarda ko menene ya taba maki mutunci , kuma ko wani irin hargitsi ya tunkaro rayuwarki ki san cewa Allah ya haliceki shi ya dora maki ba kowa ba, ....., Sai maganar auren kannenki, a jiya fa iyayen wajen mijin rukaya sun nuna da wuri suke so, dan a cewarsu sati biyu, da kyar dai abanku ya tsaida abin nan da wata daya, kennan dole mu zauna mu yi shawara mu ga abinda zai fishemu ko?"
Da mamaki ta ce" Ka8, da wuri haka Mama, na zatama sa kai bayan babar sallah?"
Mama ta ce" Nima na zaci hakan, ama kin ga yadda Allah ya yi"
Khausar ta yi murmushi ta yi addu'ar Allah ya nuna masu ranar da rai da lafiya
Nan suka hade suka yi ta zantawa har baba ya dawo gida shima ya hadu da su ya ringa tsokanar Khausar yar gidan Hajia ya ce" Kin ga, TAUFEEK ya zo ya maidawa Hajia ke tun kafin ta tardoni tace ni na kwaceki"
Dariya Mama ke yi ta kama baki ta ce" Ni ai jiya na sha dariya Ni kadai, Hajia fa hararena take yi wai ban san ciwon Khausar ba"
Aba ya ce" Nima cewa ta yi ba sannin ciwon yar aka yi ba"
Nan fa aka dauko caftar Hajia, Khausar ta ringa dariya dan walahi sai yanzu ta idasa sakewa har ta ji wasai a ranta, ta fada masu turaren da hajiar ta mata jiya da yau da safe, ai kam kannenta da iyayenta aka rasa mai ba dan uwansa hakuri dariya suke bilhaki, Aisha ta ce" Ni walahi tsoronta nake ji, idan tana fadan nan sai na ji kamar zata iya marina, kuma ita babu wanda ta bari, harta yaya TAUFEEK fa sai ku ji ta yanko shi , shi kuwa abin mamaki idan ya zura ido ya kalleta sai ka ga ya dauke kansa kamar Allah bai yi ruwanta ba, sam baya kulata"
KHausar ta ce" Ke na rabaki da TAUFEEK, shi ai du lokacin da kake shirye ku yi balaki ne na zai biyaka ba, ki ga fa idan ina fushi da shi na yi na yi ya biye min sai kawai ya kare min kall9 ya dauke kai, ni kuwa hakan irin haushin da yake bani, sai in ga a banza kennan ban samu muka raba hali ba"
Mama na dariya ta ce" To ai shi ba mashiririci bane da zai tsaya karamar yarinya ta fada ya fada"
Haka suka yi ta sharfi sunna fara'a, a hankali kuma mutane na lekowa sunna sake yin barka da arziki da fatan Allah ya nuna masu ranar auren
Zuwan TAUFEEK ya saka suka mike sukai mata rakiya, su uku, Aisha , Rukaya, da Auta har wajen motar
A lokacin da ta bude ta shige a gaban idannuwanta yan zaman anguwar suke lekowa, ita kuwa ta cire kanta bata kula kowa ba ta shiga neman layin Mujaheed
Sai da suka kusa isa gidan ya daga wayar, cikin dan basarwa ya ce" Batan numba aka yi ba?"
Khausar ta yi dan murmushi a hankali ta ce" Barka da warhaka Elhaji"
Elhaji Mujaheed ya amsata shima da kula
Khausar ta ce" sai yanzu na ga misscall dinka, shine nace ko zaka iya zuwa nan gidan su TAUFEEK da yake a nan zan kwana? Idan har dare bai yi ba?"
TAUFEEK dake tuki yana amsa waya ya dan kalleta kadan, sai kuma ya dauke kansa ya ci gaba da tukin
Bai dai san me suka tatauna ba har suka karaso gida dan shi bai gama tasa wayar ba har sai da suka iso ya fice yana amsa wayar, ita kuma ta ciro kwanukan ta nufi bangaren Hajia da su
Samu ta yi Hajiar bata nan, mai aikinta ta shaida mata tana bangaren su Mama, dan haka sai kawai ta shige bayi ta yi wanka ta fito ta cenza kayanta sannan ta zauna ta hada lipton mai zafi ta shiga sha a hankali tana dan duba agogo domin Elhaji Mujaheed yace ta bashi minti ashirin gayanan zuwa
A lokacin da ya sanar mata yana cen babar kofa bai samu shigowa ba a dole ta mike ta shiga neman layin TAUFEEK, sai dai ta yi ta yi bai daga ba, gashi hajia bata dawo ba, abindama ya dan sakata kin bin hajiar da kuma kin zuwa ta gaisar da su mai aikin na hajiar cewa ta yi an zo an yi kiran hajiar ana fada a cen, hakan ya sa ta yi zamanta dan ba zata je kotai kotai bayan ta ji abinda aka fada ba
Hijab ta saka ta Hajia dan ta nemi nata sama ko kasa ta rasa, da dan sauri ta nufi bangaren TAUFEEK tana sake gwada kiransa ama abin haushi ba'a daga ba
A nutse ta dan buga kofar sannan ta kama ta murda da salama a bakinta
Fara'a ce ta yawaita a fuskarta tana kallon Yumnah dake tsaye wajen diner, jikinta daure da rigar girki, hannayenta da safar sauke tukwane, tana sanye da wando da riga , wandon da kadan ya dan dara gwuiwarta , rigar kuwa mai siririn hannu ta juyo ta zubawa Khausar din ido ama kuma bata amsa salamar da ta mata ba
A hankali Khausar ta dan dauke dubanta gannin yannayin shigar Yumnar tana dan murmushi ta ce" Matarmu, barka da dare, dan Allah ki yi hakuri na dame ki, ko freind na kusa?"
Yumnah ta kare mata kallo, ta dago ta watsar sannan ta juya ta ci gaba da gyaran diner dinta ba tare da ta abata amsa ba
Da dan mamaki Khausar ta dan juyo dan gannin ko dai bata bata jita bane??
*ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA*
Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu.
Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu.
Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda.
Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter.
Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba.
Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726
Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
*DA CIWO A ZUCIYATA*
💔💔💔💔❤🩹❤🩹💔💔💔💔
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 2️⃣3️⃣
LITATAFAN MARUBUCIYAR
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Neman na kaina
Bani da zabi
Bak'a ce
Kutkale
Makauniya ce
Mage
Duk nisan jifa
Idan ka raina inda kake
Dutse
Alkalamin kadarata
Bani da zabi
Dakika Biyar
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*