← Book details Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 116

Sashe 61

Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

HAJIA kuwa lokaci daya ta shiga sallalami tana tafa hannu kafin ta debowa TAUFEEK wani duba tun daga ƙafarsa har kansa ta watsar ta rafka tagumi ta ce" ka cucemu, ka gama cutarmu, sai ka shirya tun gobe mu je kasuwa Ni da kai mu ciro anko mu maidawa kura aniyarta , daga nan ka kaini wajen masu kayan ganye in hado hade hade na tsumi mu zo in tafasa mu kai mata ta shiga sha dan tsumi iya tsumi sai na tsumata alkawari ne na yi kuma cikawa ya zame min tilassss!, Kai wannan yaro wannan yaro da kake gani ka haifi durum baki a dinke , kai yanzu wannan hali ne? Da WANCEN abar a bushe uwa karauki zaka gama rayuwa? Ama ba'a more aure ba sam, kuma ba'a gaji uba ba, kai ko koyi na zaka yi da mahaifinka ba? Siririya daya ya yi ya ga ba riba ya ajiye, yanzu idonka idon Khausara wani zai dauka? Dubata fa cinyoyin nan ko na sa albarka, bayanan kuwa tas kake ajiye faranti ya zauna......."

Idannuwansa ya lumshe a hankali sakamakon yadda amon Muryar HAJIA ke amsa masa a kwakwaluwarsa

Da kula ya sake zuba mata ido a karro na biyu yanai mata alamun ta iya bakinta ama zuba take tana fada har tana neman share hawaye, d'anta kuwa na bata hakuri cikin ikon Allah

A hankali ya iya saka takalmansa da ya cire ya dora ƙafarsa saman abinda ta shinfida ta zauna ya mike cikin kula da yannayinsa ya juya dan sai ya ji sam surutun ne baya so

"TAUFEEK?" Aba ya fada yana dubansa da dan mamakin yannayinsa, duba da yanzu yanzu suke firarsu a sake yadda suka saba

Juyowa ya yi dan amsawa sai ya ga shi din suke kallo, hakan ya sa ya sakar masu murmushi yana dan sosa goshinsa a hankali ya ce" Aba, inada wani aiki ne ashe yanzu na tuna, good night"

Aban ya amsa shi da Allah ya tashe su lafia sannan ya tafiyarsa ya bar Aban da HAJIA na tatauna wata muhimmiyar maganar

A daren nan, wani irin ciwon kai mai masifar zafi ne ya sauko masa, wanda ya danganta shi da rashin isashen barci ne kwana biyun da baya samu, dan haka ya yi iya yinsa dan ya samu hutun ama sam barcin ya ki zuwar masa

Lokaci kankani ya samu kansa cikin yannayi na mugu mugun bacin rai kan abubuwa da dama, domin yana dawowa daga sallar asubahi fadan da ya rike bai juyewa Yumnah ba ya sameta har dakinta tana shafa manta ya sauke mata kwondon balakin da ya tayar mata da hankali, domin tsohuwar maganar da take jin salama a ranta cewar ya manta ce ya taso mata ya sakata gaba ya mata wankin baban bargo da jan dogon kashedi a kan ko da wasa ta kuma gigin wannan banzan tunanin a kansa zata sha mamakinsa, kuma ta kiyayeshi ba auren zobe ya yi da ita ba bale tace zata ringa yanka masa kashedi a kan irin mu'amalarsa da koma waye, bai kuma aureta da alkawarin zama da ita kadai ba dan ko yanzu aure ya kama shi yana iya yi babu yarjejeniyar zama da ita kadai a duniyarsa!

Daga nan ya fice ya shige dakinsa ya shiga wanka yana jin wani balaki na Kunno shi

Yana fitowa a wankan ya saka fara kal din jalabiyyarsa da dogon wandonta yana fesa turare dan ba zai fita da wuri ba aka shiga buga baban falon

Bai tsaya wani bata lokaci ba ya shiga saukowa dan budewa

Yana budewa ya saukewa HAJIA idannuwansa da suke rine cike da gajiya da abin barci

Kicin kicin ya yi da fuskarsa ya dubeta tsaf ya ce" Meye ? Zuwa kika yi ki kaini ciro anko da menema? Sai ki daukeni, nace ki daukeni , kin ga ki fita hanyata ki bani lafiya in kina so ba anko ba ki ciro Chaina ki laka ama ni ki bani lafiya!"

HAJIA ta hangame baki tana kallonsa hadi da gyara tsayuwarta ta ce" Ka ga wani ikon Allah ranar juma'a du Musulmin kirki ai ya farka da fara'a ama banda kai?"

Taufeek har zai juya ya juyo ya sake tsareta da harara yana tunanin inama ace wannan din nan dai in ya mata wani abu mai kwanoni ba zai tsine masa ba ?
Kwafa ya yi zai juya HAJIA ta sake gyara tsayuwa ta ce" Sai ka daukeni da mari in gane tabata ta sameka, Magidanci Ni din nan da kake gani kadangaren bakin tulu nake, a karni a kar tulu a barni in bata ruwan tulu!, Maganar anko kuma ai ka san dole ne mu fitar Ni da kai dan a ramawa kura aniyarta, YANZUN dai ubanka yace ka zo ga cen wancen tana nakuda mu je mu ajiye masu ita mu wuce kasuwa, kai in ba sai na nuna maka Ni na haifi mai kwanoni ba kace min ba Ni bace HAJIA!"

Daga haka ta juya har kamar iska zata dauketa ta nufi bangaren matan gidan sai bambami take tana ambaton ita Magidanci zai gwadawa danyen kai

A hankali ya lumshe idannuwansa yana jin harda juwa ke son maka shi a kasss, a Nutse ya koma saman ya gama abinda zai yi ya sanar masu a kaisu asibitin sannan ya kimtsa ya sauko ya shige mota ya bi bayansu yana jin kawai zazabi ne ke damunsa shi yasa yake jinsa wani iri, sai tarin bacin ran da yake kyautata zaton tarawa ne ya yi yake neman yi masa yawa a ransa,

Yana fitowa daga motar ya nufi bangaren amsar haihuwar
Bai shiga ba domin likitoci ne rufe kanta dan haka ya karasa wajen mahaifiyarsa dake zaune wace rabonsa da ita tun jiya da yama ya gaisheta da kula sosai sannan ya nemi kam su mike su karasa office dinsa idan ta sauka sai su sauko

Tun kafin ta bashi amsa HAJIA dake zaune ranta a matukar nace tana sake bin asibitin da kallo zuciyyarta tamkar zata kama da wuta ta dubi bangaren da HAJIA kaka ke zaune tana jan carbi ta sake hade rai ta ce" Ni kam ina nan ai ba za'a barta ita kadai ba"

Mama ta yi murmushi ta ce" Ka je kawai ka kama aikinka ai ka ga ba zamu je cen mu zauna ba mu da muka kawo mai haihuwa, nama yi kiran KHAUSAR tace min yanzu zata karaso asibitin ko?"

A hankali ya dan dago idannuwansa dake dauke da launin ja, zai bata amsa KHausar ta karaso da salama a bakinta ta karasa wajen HAJIA ta fara gaisheta sai wani washe mata baki take sannan ta karasa wajen su Maman ta duka har kasa tana gaishe su lokaci daya tana ajiyewa Maman dangin su ruwa ne ta dan kalli TAUFEEK dake gefen Mama ta ce" Morning besty, Mama kin ga ruwa kawai na tsaya cen na amso dan ban san da me zaku karya ba, bari in amshi katinsa in koma me da me zan kawo ne na kari na tabbata safiyar nan ba'a karya ba aka fito"

HAJIA kaka aka wani saki murmushi aka cira kai kasa kasa ta ce" Aikin banza, ga mace mai mutunci kana rainan hankali yarinya ta san darajar mahaifiyarka kana shirme, mu zuba mu gani dan mai Kwanoni!"

😭 Ina tsoron HAJIA, HAJIA akoy rigima da neman mutun da balaki, sai wasu abu na neman fitina take yi🥹🥹🥹🥹 bayan mu oho sai mema wai☹️🙄

💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔

*DA CIWO A ZUCIYATA*

💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔

_MALLAKIN_

*SAJIDA NIJAR*

*FREE BOOK NE* 3️⃣7️⃣

*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*

1: Duk karyar kada

2: Yar mahaukaciya

3: Neman na kaina

4: Bani da zabi

5: Bak'a ce

6: Kutkale

7: Makauniya ce

8: Mage

9: Duk nisan jifa

10: Idan ka raina inda kake

11: Dutse

12: Alkalamin kadarata

13: Bani da zabi

14: Dakika Biyar

15:Wata kokowar

16: Aure yakin mata

17: Ni zan ladabi

18: Daga tafia daukar soja

*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*

Now

*Da CIWO A ZUCIYATA*

*Tallah, tallah, tallah*

*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*

_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_

Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicé
Lait de nuit
Parfums désodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes

*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata

Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃

Ita kam Khausar bata san komai ba, Mama kuwa murmushi ke kawace a fuskarta, cike da kular da ta saba ba KHausar in tana kusa da ita take dubanta bayan ta buda ledojin ta ce" A'a, ke da kika zo aiki kuma Khausar ma tsareki a nan? "
Chapter 61 · 0% Book details