Sashe 42
Da Ciwo A Zuciyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gata dai fuska du ta fara nuna alamun daf take da zagwonyewa dan tsufa, ama bakinta ko amon muryarta bai cenza ba, shi a yau in ba dan mai kwanoni ba da matar nan sai ya saka an zo an ririketa an sauke mata aljannun kanta, ama ba komai zai kyaleta ne har su tafi haji shi ya san yaya zai yi da ita
Banza ya mata ya juya zai bar gidan, Hajia ta daga murya ta ce" Au na bata maka rai Hala dan nace wancen abar kamar muciya? Na fada in ranka ya kiya ka kawo mace mai dima dima mana ka gani in an zageka dilla malan"
A hankali Khausar dake rage wutar nan ta dan dago ta kalli Hajia, an yi katari itama ta kallota sai ta karaso tana sakin murmushi ta ce" Yar nan tuki ake? Sannu ke kuwa tashi ki yi wanka ku tafi mana tace karfe goma zaku tafi fa, tashi maza dan watsa ki dan sha na sha kin ga na karbo maki wani na farin jinnin yanzunnan wajen malan, je ki yi wanka kafin ki fito na saka maki a nono sai ki sha "
Khausar ta amsa hajia da to, domin bata da amsar da ta wuce wannan ta mike ta je dan shiryawar ta barawa mai aikin Hajiar sauran aikin,
Tana gama shiryawa ta dauki wayarta da nufin kiran TAUFEEK, dan ta ji yaya maganar wajen aiki ne yau? Kamar yadda Mama tace shin yana da hanyar da zai sanar masu ba tare da an mata fadan rashin zuwan ba, sai kuma ta dakata da wayar a hannunta tana tuna abinda ya faru jiya, ko yau ba wani gaisuwar da suka saba suka yi ba dan sai take jin wani iri a cen kasan zuciyarta da tarin tunanin me hakan ke nufi, sun dai gaisa da murmushi ama bata wani tsaya ta ji daga gareshi ko ta masa tambayar iyali ba
Salama ta yiwa Hajia ta wuce bangaren su Maman bayan hajiar ta shaida mata ta bar kayan za'a mika mota
Yau dinma sai da aka bata damar shiga kafin ta shiga baban falon
Mutanen dake falon ta fara bi da kallo kafin ta gaishe su, sai dai a cikinsu yar budurwa matashiya daya ta amsata itama a dan fizge ta dauke kanta
Ido ta zubawa Yumnah gannin sai da ta dubeta ta watsar
Tana shirin hawa saman sai ga Maman na saukowa da yar karamar jakkar hannu
Yumnah ce ta fara mikewa tana dan sosa gaban goshinta alamu na dan jin kunyar surukar nan ta shiga gaisar da Mama
Da dan sauri Maman ta amsa ta karasa saukowa ta dan dube su baki daya ta ce " Barkarku da hutawa, zamu dan fita ne da Khausar sai mun dawo"
Hajia Nuwairah ta yi kamar bata jita ba sai yarinyar wajenta da take riko wato hamdiya ce ta karasa da dan sauri tana sake gaisar da Maman
Jakar hannunta da Hamdiya ta so karba Maman ta dan rike da kula sosai tana mata murmushi ta ce" Na gode yata yi zamanki ai ba wani nauyi Allah ya maki albarka"
Hamdiya ta amsa tana dan sinne kai irin girmamawar nan tana kuma.jin dadin adu'ar Maman a ranta, a cen kasan zuciyarta kuwa ba abunda ke faranta mata a yanzu irin ta faranta ran yayansu ta hanyar yin abinda Yayansu ke so
Mama kuwa daga haka ta fice tare da KHAUSAR suka yi tafiyarsu
Cike da isa irin tata Hajia Nuwairah ta dan sake kallon yannayin Yumnah, sai kuma ta saki dan murmushi tana dauke dubanta cikin basarwa ta ce" Ya haka Yumnah na zata tare ne zaku fita da srakuwar taki?"
Yumnah ta juyo da dan sauri, dan kamarma wace ta afka tunani ta kalli Hajia Nuwairah, sai ta ga hankalinta ba a kanta yake gana daya ba, tana dan yi nata firar ne kuma tana maida hankali kan Hamdiya
Dan numfashi ta fitar, sai kuma ta juya tana fadin" Bara na koma Hajia dama gaishe da ku na leko"
Daga haka ta yi gaba
Tan fita Hajia Nuwairah ta mike ta kama kunnen Hamdiya ta ja da karfi ta yi wajen kicin dinta da ita danma kar a fito a sameta da ita a haka
Rai bace tana rike da kunnenta ta ce" Ke na tambayeki, Hajia fatima kanwar uwarki ce?"
Da sauri Hamdiya ke girgiza kai tana ji kamar Hajiar zata tsinke mata kunne ne
Murya a kausashe ta ce" To ki kula, bana son rainin hankali da shishigin tsiya, ba abinda ya hadaki da ita, ko gaisuwar kirki na ga kin kuma yi mata sai na wulakantaki sannan na maida ke gidan ubanki, dan ba zai yiwu ba na dauko ki na kawo ki kashe ni kina shiga gindin kishiyata da ba kaunata take yi ba, ke shaida ce a gidan nan dan ta haifi namiji daya kwal ba irin abinda ba'a mana a kanta da danta, to ba zai yiwu ku da kuke nawa ta kwace min ba kin fahimta?"
Kai take gyadawa har idannuwanta sun cika da kwala kafin ta saketa ta fita da sauri ta haura sama ita kuwa Hajiar ta ja tsaki tana sake hade fuska domin abin ya bata haushi ainun, sai dai wata hanyar da ta hango ta baraka ta sanyaya mata zuciya, domin ta tabata in dai har abinda ta gani a idannuwan Yumnah kishin wancen yarinyar ne to fa zata bi ta nan ta sa rashin jituwa tsakanin Hajiar da Yumnah, tana ji tana gani sarakuwar ɗan nata sai dai ta hangota ba dai su yi wata taraya ta zumunci ko fahimtar junna ba!
Sosai Khausar ta ji dadin fitar nan, sun je an aunata, daga nan suka je Hajia ta daukar mata takalma masu kyan gaske harda kafa ciki mai dan karamin hls a jikinsa fari kal mai kyan gaske, harfa kayan kwaliya, daga nan suka wuce wajen HAJUA FUSAM, nan fa ta sha kallo ta nemi rikicewa har ta ji wani irin sha'awar son ta ringa gyara jikinta irin na matar da kayan aikin matar, lalle mata sunna gyara, tun daga su dilka, kurkum, kujera, rigar dilka, itacen dilka, turare kai komai da komai dai a wajen matar nan akoy masu kyau da inganci , turatukan da Mama ta daukar mata sai da ta ji kamar ta bude ta yi ta sinsina a hancinta, turaruka masu kanshi , sanyin kanshi da saka nutsuwa a zuciya, daga nan suka wuce gidan aminiyar Maman , nanma sakonta ta amsa sannan suka wuce gidan su KHausar din dan Maman ta yiwa Maman su KHausar din barka da abin arziki, nan ta shaida mata an saka ranar ance nan da wata daya sannan ta ringa godiya dan Khausar ta kasa r8ke murnarta ta sanarwa Maman komai da komai , har maman ta rasa abin fada , sun jima sunna zantawa kafin su tafi gida
Da wannan Khausar ta karra kusan sati a gidan su TAUFEEK, a kulun zata je wajen aikinta ta dawo ne, kuma a kulun din shine zai ajiyeta ya je ya daukota, ko fushi fushin da ta so masa na yannayin matarsa sharewa ta yi ta daukarwa kanta alkawarin zata gane me hakan ke nufi dan ta dauki mataki, Yumnah dai ba sa'arta bace ba sa'ar yinta bace, ko tana da wata matsala da itane bata sani ba zata bi a hankali idan ta gane sai ta magance in mai magantuwa ce, in kuwa ba mai magantuwa bace sai ta kama kanta, dan ba zata taba yarda wani abu na rashin da'a ya shiga tsakaninta da ita ba, bata ga dalili ba
Ranar da zata koma gida sai da ta ji ba dadi a ranta, Hajia fadi take ta yi zamanta mana, itama ta yi sabo da ita harda na mamaki, dan Khausar akoy dadin zama ga girmama manya ga rashin kiywa, da kyar dai ta iya tafia bayan an cika boot da tsarabe tsarabe da dinkunnanta da kayayakinta tamkar wace ta je wata kasar ta shekare, Mama kuwa ta sakata daki ta mata nasiha mai kama da fada fada, ta yi mata nuni kan yafa dace ta dan gyara, sosai ta hadata da mutanen arzikin da zasu sake gogar da ita a hanya mai kyau ba lalataciya ba, irin tarayar nan da koda baka son gyarawa idan ka yi tsai ka ga yadda mutane ke gyarawar kaima sai ka tsinci kanka a ciki tsamo tsamo
A lokacin da ya ajiyeta gida murna wajen yan uwanta ba'a magana
Haka su mama ke saka albarka a tarin arzikin da ta dawo da shi, yan anguwa kuwa sunna leke da zunde da bakinsu da mamakin inda ta je har ta jima haka,
Ko da Baba ya dawo shima farin ciki kamar me, kasa boyewa ya yi, nan ta nuna zata raraba kayan da yan uwanta Baba kuwa ya nuna aa ko daya summa ai ga sababin kaya nan na aure ta ajiye abinta itama ta ringa sakawa
Haka baba ke daga yan jakunkunnan da takalma yana fadin" Ai zaki saka ko khausar din Aba?" Ita kuma tana dariya da fadin" Baba bara ka gani zan saka duka kaffff, kuma harda kwali"
Ita dai Mama dariya take yi a ranta tana ayana' Allah ya sa Khausar din ta saka"
Kwonci tashi har lokacin auren yan uwanta ya karaso, aka sha biki har biki dan kuwa an yi taro yan uwa da aminan arziki haka yan anguwa sun yi karra sosai an samu tarin gudunmuwa harda na mamaki, dama Aba bai yi sanya ba ya masu abinda ya dace daidai karfinsa haka kuma an ci an sha da anki din atampa daya da suka fitar har dare ya yi aka raka kowace dakinta, ya zamto a gidan a yanzu Khausar ta sake tsintar kanta daga ita sai ita domin Auta namiji ne kuma bama dakinsu daya ba, shi dakin Aba yake kwana
Banza ya mata ya juya zai bar gidan, Hajia ta daga murya ta ce" Au na bata maka rai Hala dan nace wancen abar kamar muciya? Na fada in ranka ya kiya ka kawo mace mai dima dima mana ka gani in an zageka dilla malan"
A hankali Khausar dake rage wutar nan ta dan dago ta kalli Hajia, an yi katari itama ta kallota sai ta karaso tana sakin murmushi ta ce" Yar nan tuki ake? Sannu ke kuwa tashi ki yi wanka ku tafi mana tace karfe goma zaku tafi fa, tashi maza dan watsa ki dan sha na sha kin ga na karbo maki wani na farin jinnin yanzunnan wajen malan, je ki yi wanka kafin ki fito na saka maki a nono sai ki sha "
Khausar ta amsa hajia da to, domin bata da amsar da ta wuce wannan ta mike ta je dan shiryawar ta barawa mai aikin Hajiar sauran aikin,
Tana gama shiryawa ta dauki wayarta da nufin kiran TAUFEEK, dan ta ji yaya maganar wajen aiki ne yau? Kamar yadda Mama tace shin yana da hanyar da zai sanar masu ba tare da an mata fadan rashin zuwan ba, sai kuma ta dakata da wayar a hannunta tana tuna abinda ya faru jiya, ko yau ba wani gaisuwar da suka saba suka yi ba dan sai take jin wani iri a cen kasan zuciyarta da tarin tunanin me hakan ke nufi, sun dai gaisa da murmushi ama bata wani tsaya ta ji daga gareshi ko ta masa tambayar iyali ba
Salama ta yiwa Hajia ta wuce bangaren su Maman bayan hajiar ta shaida mata ta bar kayan za'a mika mota
Yau dinma sai da aka bata damar shiga kafin ta shiga baban falon
Mutanen dake falon ta fara bi da kallo kafin ta gaishe su, sai dai a cikinsu yar budurwa matashiya daya ta amsata itama a dan fizge ta dauke kanta
Ido ta zubawa Yumnah gannin sai da ta dubeta ta watsar
Tana shirin hawa saman sai ga Maman na saukowa da yar karamar jakkar hannu
Yumnah ce ta fara mikewa tana dan sosa gaban goshinta alamu na dan jin kunyar surukar nan ta shiga gaisar da Mama
Da dan sauri Maman ta amsa ta karasa saukowa ta dan dube su baki daya ta ce " Barkarku da hutawa, zamu dan fita ne da Khausar sai mun dawo"
Hajia Nuwairah ta yi kamar bata jita ba sai yarinyar wajenta da take riko wato hamdiya ce ta karasa da dan sauri tana sake gaisar da Maman
Jakar hannunta da Hamdiya ta so karba Maman ta dan rike da kula sosai tana mata murmushi ta ce" Na gode yata yi zamanki ai ba wani nauyi Allah ya maki albarka"
Hamdiya ta amsa tana dan sinne kai irin girmamawar nan tana kuma.jin dadin adu'ar Maman a ranta, a cen kasan zuciyarta kuwa ba abunda ke faranta mata a yanzu irin ta faranta ran yayansu ta hanyar yin abinda Yayansu ke so
Mama kuwa daga haka ta fice tare da KHAUSAR suka yi tafiyarsu
Cike da isa irin tata Hajia Nuwairah ta dan sake kallon yannayin Yumnah, sai kuma ta saki dan murmushi tana dauke dubanta cikin basarwa ta ce" Ya haka Yumnah na zata tare ne zaku fita da srakuwar taki?"
Yumnah ta juyo da dan sauri, dan kamarma wace ta afka tunani ta kalli Hajia Nuwairah, sai ta ga hankalinta ba a kanta yake gana daya ba, tana dan yi nata firar ne kuma tana maida hankali kan Hamdiya
Dan numfashi ta fitar, sai kuma ta juya tana fadin" Bara na koma Hajia dama gaishe da ku na leko"
Daga haka ta yi gaba
Tan fita Hajia Nuwairah ta mike ta kama kunnen Hamdiya ta ja da karfi ta yi wajen kicin dinta da ita danma kar a fito a sameta da ita a haka
Rai bace tana rike da kunnenta ta ce" Ke na tambayeki, Hajia fatima kanwar uwarki ce?"
Da sauri Hamdiya ke girgiza kai tana ji kamar Hajiar zata tsinke mata kunne ne
Murya a kausashe ta ce" To ki kula, bana son rainin hankali da shishigin tsiya, ba abinda ya hadaki da ita, ko gaisuwar kirki na ga kin kuma yi mata sai na wulakantaki sannan na maida ke gidan ubanki, dan ba zai yiwu ba na dauko ki na kawo ki kashe ni kina shiga gindin kishiyata da ba kaunata take yi ba, ke shaida ce a gidan nan dan ta haifi namiji daya kwal ba irin abinda ba'a mana a kanta da danta, to ba zai yiwu ku da kuke nawa ta kwace min ba kin fahimta?"
Kai take gyadawa har idannuwanta sun cika da kwala kafin ta saketa ta fita da sauri ta haura sama ita kuwa Hajiar ta ja tsaki tana sake hade fuska domin abin ya bata haushi ainun, sai dai wata hanyar da ta hango ta baraka ta sanyaya mata zuciya, domin ta tabata in dai har abinda ta gani a idannuwan Yumnah kishin wancen yarinyar ne to fa zata bi ta nan ta sa rashin jituwa tsakanin Hajiar da Yumnah, tana ji tana gani sarakuwar ɗan nata sai dai ta hangota ba dai su yi wata taraya ta zumunci ko fahimtar junna ba!
Sosai Khausar ta ji dadin fitar nan, sun je an aunata, daga nan suka je Hajia ta daukar mata takalma masu kyan gaske harda kafa ciki mai dan karamin hls a jikinsa fari kal mai kyan gaske, harfa kayan kwaliya, daga nan suka wuce wajen HAJUA FUSAM, nan fa ta sha kallo ta nemi rikicewa har ta ji wani irin sha'awar son ta ringa gyara jikinta irin na matar da kayan aikin matar, lalle mata sunna gyara, tun daga su dilka, kurkum, kujera, rigar dilka, itacen dilka, turare kai komai da komai dai a wajen matar nan akoy masu kyau da inganci , turatukan da Mama ta daukar mata sai da ta ji kamar ta bude ta yi ta sinsina a hancinta, turaruka masu kanshi , sanyin kanshi da saka nutsuwa a zuciya, daga nan suka wuce gidan aminiyar Maman , nanma sakonta ta amsa sannan suka wuce gidan su KHausar din dan Maman ta yiwa Maman su KHausar din barka da abin arziki, nan ta shaida mata an saka ranar ance nan da wata daya sannan ta ringa godiya dan Khausar ta kasa r8ke murnarta ta sanarwa Maman komai da komai , har maman ta rasa abin fada , sun jima sunna zantawa kafin su tafi gida
Da wannan Khausar ta karra kusan sati a gidan su TAUFEEK, a kulun zata je wajen aikinta ta dawo ne, kuma a kulun din shine zai ajiyeta ya je ya daukota, ko fushi fushin da ta so masa na yannayin matarsa sharewa ta yi ta daukarwa kanta alkawarin zata gane me hakan ke nufi dan ta dauki mataki, Yumnah dai ba sa'arta bace ba sa'ar yinta bace, ko tana da wata matsala da itane bata sani ba zata bi a hankali idan ta gane sai ta magance in mai magantuwa ce, in kuwa ba mai magantuwa bace sai ta kama kanta, dan ba zata taba yarda wani abu na rashin da'a ya shiga tsakaninta da ita ba, bata ga dalili ba
Ranar da zata koma gida sai da ta ji ba dadi a ranta, Hajia fadi take ta yi zamanta mana, itama ta yi sabo da ita harda na mamaki, dan Khausar akoy dadin zama ga girmama manya ga rashin kiywa, da kyar dai ta iya tafia bayan an cika boot da tsarabe tsarabe da dinkunnanta da kayayakinta tamkar wace ta je wata kasar ta shekare, Mama kuwa ta sakata daki ta mata nasiha mai kama da fada fada, ta yi mata nuni kan yafa dace ta dan gyara, sosai ta hadata da mutanen arzikin da zasu sake gogar da ita a hanya mai kyau ba lalataciya ba, irin tarayar nan da koda baka son gyarawa idan ka yi tsai ka ga yadda mutane ke gyarawar kaima sai ka tsinci kanka a ciki tsamo tsamo
A lokacin da ya ajiyeta gida murna wajen yan uwanta ba'a magana
Haka su mama ke saka albarka a tarin arzikin da ta dawo da shi, yan anguwa kuwa sunna leke da zunde da bakinsu da mamakin inda ta je har ta jima haka,
Ko da Baba ya dawo shima farin ciki kamar me, kasa boyewa ya yi, nan ta nuna zata raraba kayan da yan uwanta Baba kuwa ya nuna aa ko daya summa ai ga sababin kaya nan na aure ta ajiye abinta itama ta ringa sakawa
Haka baba ke daga yan jakunkunnan da takalma yana fadin" Ai zaki saka ko khausar din Aba?" Ita kuma tana dariya da fadin" Baba bara ka gani zan saka duka kaffff, kuma harda kwali"
Ita dai Mama dariya take yi a ranta tana ayana' Allah ya sa Khausar din ta saka"
Kwonci tashi har lokacin auren yan uwanta ya karaso, aka sha biki har biki dan kuwa an yi taro yan uwa da aminan arziki haka yan anguwa sun yi karra sosai an samu tarin gudunmuwa harda na mamaki, dama Aba bai yi sanya ba ya masu abinda ya dace daidai karfinsa haka kuma an ci an sha da anki din atampa daya da suka fitar har dare ya yi aka raka kowace dakinta, ya zamto a gidan a yanzu Khausar ta sake tsintar kanta daga ita sai ita domin Auta namiji ne kuma bama dakinsu daya ba, shi dakin Aba yake kwana